← Book details Ta Fita Zakka Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 86 OF 193

Sashe 86

Ta Fita Zakka Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read

Dukkansu suka juya Baba mallam ne Cikin Akyabbansa da Rawani Tsaye kofar Falonsa yana kallonsu Bai ji Mganarsu ba Fitowarsa kenan Daga Daki yaji Akilu na fadin shi Sa"anta ne yana Lekowa yaga zai kai mata hannu.
Akilu na ganin Baba Mallam ya Rankwafa yana fadin"Allah ya kara girma Baba..!
Amina kuwa gaisheshi tayi ya amsa yana fadin"Mamana Daga ina da Safan nan..?
Amina ta sharara karya da cewa"Nazo gaida Hajiya ne..!
Baba maallam ya Murmusa yana kallonta kafim yace"Yar gidan Hajiya..To kin gaishetan ne..?
Amina kanta na kasa ta Daga kai Baba mallam Akilu ya kallah yana Fadin"Bana son na kara ganin wannan Sakarcin..In har zaka Daketa ashe zaka sa ka hannu ka Daki Umaru ko..?
Akilu ya Dago kansa yana kallon Mallam kafin ya juya yana kallon Amina da kanta ya fashe ta Hura Hanci tana Juya ido shifa tun sanda aka Daura auran Amina da ya Danmallam yake Tsausayamai ko shi da yake yaro daidai da ita bazai iya da Amina ba ballatana ya Danmallam wanda bai da Hayaniya mai sanyi ne shi.Ai Tsab zata jazamai hawan jini in kuma ta Hadu da Sauran ciwo Tsab zata Karisa shi Lokacinsa bai yi ba.
Dukar da kansa yayi yana Fadin"Ayi hakuri mallam baza"a kara ba..!
Yaji Dadin haka nan da nan ya saki Fuskarsa yana fadin"Ko kai fa..?Allah yayi muku albarka..!
Ya amsa da Ameen ya mike yana kallon Amina Data fakaici idon mallam ta Zabgamai gwalo Rai ya bata yana Kada mata ido ita kuma tana wani Juyamai ido.
Sai da ya shige Dakinsu sannan Mallam ya kalli Amina yana Fadin"Ina Sa"idu..?
Yana gida ko ya fita ne..Au ga motarsa ma ashe yana gida kenan..!
Amina tace"Eh yana gida mallam
Mallam yace"Yauwa in kin je gida kice mai ina son ganinsa saboda da wuri zan fita!
Amina tace"Mallam tafiya zakayi..?
Mallam yace"Zaria zani Cikin makarantar ABU akwai wani Taro da aka gayyaceni a Depatment din Islamis Studies shine Uzairu zai kaini yau nakeson mu dawo bana so muyi Dare..!
Cikin Sanyinta tace"Allah ya Kiyaye hanya..!
Ya amsa da Ameen uwata Daganan tamai sallama ta wuce ya bita da kallon Tsausayi har yau bai daina jin yanayin kamar bai kyauta ma Amina ba,Hajiya tataso da wannan mganar kuma bazai iya musa mata Ba bataba ja da mganarsa ba yasanta sarai tana da Dalili ammh Tunda bata Fadamai ba bazai matsamata sai yaji ba Jiya yayi istikara akan al"amarin kuma yaga Hasken Amina Tatare agidan Umaru zasu rakasu da addu"an zama Lafiya da Zuru"a Dayyaba..!
Amina Jikinta a sanyaye ta shiga gida ba Kowa a tsakar gidan Har Falon Aba a kulle alamun bai fito ba Sai ta wuce Dakin Mamanmu.
Bata afalo sai ta kutsa kai Uwar Dakinta Kamar yadda ta saba kai Tsaye hankalinta baya tare da ita Shiyasa har bata jin shigowar Amina ba,kalma Daya Amina ta jita Cikin kunnenta.

"Kada ki damu bani nace ba..Ki kwantar da Hankali......!

"Mamanmu..!

Gabanta ya fadi dam jin muryan Amina abayanta Jikinta sai ya fara rawa ckin rawan jiki ta juyo tana kallon Amina Dake kallonta Cikin mamakin ganin yadda take rawan Jiki ga Zufa na keto mata ta saman goshinta.
Cikin Fargaba da wani irin Tsoro tace"A..A..mina yaushe kika shigo..?
Amina tace"Yanzu na shigo mamanmu..!
Tana jin sadda ta Sauke ajiyar zuciya Da sai da ta kalleta,Cikin mamakin ganin yadda tayi Firgai Firgai kamar wacce tayi karya agaban Sarki.
Hannun Amina ta riko Daya jike da Zufa ta zaunar da ita gefen gado tana Fadin"Kin gayama Hajiyar abunda nace..?
Amina ta samu kanta da kasa Fadama mamanmu komai da Farko ta shigo da Niyyar Fadamata har wayar dataji Anty Amarya nayi ammh yanzu sai ta kasa Haka kurum kamar an Rufe mata baki an sauya mata mgana taji ta tana fadin"Eh na fada mata..!
Tana ganin sadda ta washe baki tana Fadin"Yauwa to me tace..?
Amina gabanta ne ya fadi bata so zargi ya shiga ranta Kodai kodai mamanmu ce suke mgama da Anty Amarya Da sauri tace A"a mamanmu ba muguwa bace ba mamanmu bace ba ita bace watace ta Dabam ita Tana yin komai Saboda Farincikina ne.
Da sauri ta Kauda wannan Tunanin da Fadin"Tace na koma gida gatanan zuwa..!
Mamanmu tayi shuru tana Tunanin anya Hajiya zata janye mganar ta kuwa..?
Duk da Mallam da Safen nan Amarya tace ya Tarasu ya fada musu Tariyar Amina ayau dinnan
Ganin kallon da Amina ke mata yasa Ta fashe da kukan makirci tana Fadin"Amina duk abunda kikaga inayi Saboda ke ne .Ina so na ga Rayuwarki ta Inganta kamar ta kowa Amina..Danmallam bai dace dake ba..Matansa Biyu Amina ina zaki iya Kishi da mata Biyu mace ma irin Sakina..Uwarta Kinsani na sani bata Kaunarmu Amina zasu yi komai Saboda su ga bayanki ni kuma na Shirya Saboda ingata Rayuwarki Sai inda Karfina ya kare,na gwammace na rasa komai Ciki kuwa har da Rabuwa da Aba dinku Saboda ke Amina..!
Ran Amina ya cika da Tsausayin Mamanmu aranta take jin mamanmu bazata taba Cutar da su ba,da sauri ta Rike Mamanmu tana fadin"A"a mamanmu kada kice haka fa..Insha Allahu saki bazai kara shiga Tsakaninki da Aba ba..Ki daina Fadar haka don Allah bana jin Dadi..!
Mamanmu tana Jan hanci tace"Tun jiya muke tsiya dashi Nidai nace ban yarda ki tare ba sai kin gama makaranta kamar kowacce ya haba..Ai wannan rashin adalci ne shima Maallam din bai Duba ba Gaskiya..Ni bazan yarda ba na Fadamai sai dai koma miye ya faru din..!
Amina tayi saurin cewa"A"a Mallam bazai taba kaini inda za"a cutar dani ba..Shi da Hajiya suma bangarena Jikina ne Mamanmu kamar yadda kike sona haka suke kaunata don Allah na Rokeki kada ki saka baki ran Aba ya baci don Allah..!
Mamanmu na kara matsan kwallah tace"Ni daman ban ce basa kaunarki ba..Bama ke ba Duka Ya"yanmu damu kanmu suna kaunarmu nace ne su Dubaki don Allah kin yi kankanta da Daukan wannan auran..!
Nidai in kina so nayi shuru kada nayi mgana koda Hajiya tazo Aba dinku ya kiraki ko yayi mgana ki Taimakeni ki Fadamai Bakisan wannan Tarewar da auran gabadaya in kuma kika kasa Fada ni zan Tubure nace ban yarda ba Duk da yace in nayi mgana zai yanke igiyar auranmu ban damu ba Zan iya yin komai Saboda ke Amina..!
Amina Sai kuka itama jin kalaman mamanmu Cikin kuka tace"Naji zan fada..Don Allah mamanmu kada kiyi mgana Ran Aba ya baci..na rasa yaya alokacin da bansan Dadinta awajena ba..Kema kuma bana so na rasaki..In kika tafi kikabar gidam nan ina zamu..?Wazai Rikemu..!?
Ni da Hamida zamu lalace mamanmu..!
Da Sauri ta Rumgume Amina Tana Mirmishin nasara kafin cikim karyewan murya take fadin"Bana so a Gurgunta miki Rayuwa ne Amina..!
Haka take fada tana jan majina karshenta dai Amina ce ta share hawayenta tana Cigaba da bama Mamanmu baki har tayi shuru kafin ta kalleta tana Fadin"Tashi kije Dakin ku..Abun karyawanku na Kitchen bari naje Nagani ko Jawad yagama Shirin Tafiya makaranta..!
Daga haka ta mike ta fice tana Dariyan Nasara duk karya ta Fadama Amina tun DAran jiya datayi mganar da Aba bata kara cemai komai ba Shima bai ce mata ba ita shegiya ce da zata bata goma ko Daya bata gyaru ba Saboda Amina ta Samu Sakin Farko ta Tabbata Sa"idu zai iya Sakinta Saboda mallam da Hajiya duk da ta samo kansa din ammh gwara ta Kiyaye in har Makircinta bai yi ba zatace ma Madina ta Kira malaminsu arufe bakin Hajiya da mallam din kan mganar Tarewar kowa ya Huta..!
Amina ma Dakinsu ta koma ta Iske Hamida da Hanne kozai kozAi ba Fara"a kallonsu tayi kafin tace"Miye haka kowacce ido kamar Nama..kunyi wani Figai figai kamar Kajin da aka Tsoma acikin Ruwan zafi..!?
Chapter 86 · 0% Book details