← Book details Ta Fita Zakka Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 83 OF 193

Sashe 83

Ta Fita Zakka Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Karfe biyu da rabi na rana aka Dauran auran su ya zeena bayan an idar da sallar jumma"a ana Daura auran Hajiya ta kira ya Fatima awaya tace su taho dasu Abidan malam zai yi sallama dasu zasu tafI kada Dare yayi ga yanayin Tsaron kasar tamu daya riga ya lalace sai fatan Allah yabamu zaman lafiya.
Gabadayansu suna gidan ya jafar har su Amina,tunda amaran suka ji an daura auran suka fara kuka su ya Jamila na musu Dariya suna fadin muma hakanan akayi mana kuma gashi mun zauna..!
Amina ce harda wakar"Su sukace suna so..Da basu ce suna so ba..Da ba"a basu shi ba..!
Ya Abida na kuka cikin Hijabinta ta Leko Tana hararan Amina Lokaci Daya tana fadin"Kema yarinya kwana nawa ne..?Keda ma zaki bar kasar bar ma wasu dariya..!
Tana fadin haka sai bakin Amina ya Mutu ta yamutsa fuska kafin ta Tura baki tace"Tab..Wlh in na je Allah ya Tsinan..!
Ya nazifa na wajen tace"Kin je ma kin gama zuwa yarinya..!
Amina ta kara Hade rai tana faman kunkuni aka saka mata Dariya gabadaya har da su Hamida daganan ta Hade rai bata kara mgana ba har suka shirya komai suka Tattara kayan amaran da suka cire waje Daya su Amina suka bamawa suka fara yin gaba su Uzairu zai zo da Mota ya Daukesu sauran kuma suka taka da kafarsu tunda ba wani nisa.
Koda suka iso kofar gidan ba Jama"a sosai,Amina ita hankalinta ma baya ma wajen kallon jama"ar wajen duk Rashin kunyarta bata juran kallon Taron maza.
Bata ma Lura da ya Danmallam Dake bakin wata bakar mota ba Shi da abokinsa Aliyu suna mgana su Hanne ne suka ganshi,Hamida Dake kusa da Amina ta tabota tana nuna mata barayin da suke Lokaci daya tana Fadin"Amina kalli mijinki..!
Amina tabi inda Hamida take nuna mata da kallo,Suna dagachan nesa ne ba lalle su gansu ba,dukkansu suna Tsaye jikin Motar ne Danmallan yana Sanye cikin Shadda kalan Sararin Samaniya Dinki riga da wando tazarce anyi Dinkin zamani na matasa masu ji da kansu sai hula zanna bukar Zaran yanayin aikin shaddan Jikinsa kafarsa cikin Bakin Rufaffan Takalmi na Fatar damisa sai bakin agogon Fata Dake tsitsiyan hannunsa na Hagu bashi ke mganar ba Aliyu Dake kusa dashi yake saurareshi shi key din Mota ne ke hannunsa yake kadawa Lokaci bayan Lokaci yana Sassauta yanayin Fuskarsa.
Sai da gaban Amina ya fadi da Sauri ta kauda kai ta sani ita bata isa tace Ya Danmallam ya dace da ita ba Tazaran Dake Tsakaninsu mai girma ce,kana kallonsa zaka hango Tsantsan kamala Dattako da sannin addini sannan uwa uba kwarjinin da Haiba ta mutumin da yasan addini sosai da sanin ya kamata sannan da yana kyau, kyau irin na fatan kowacce mace zabinta ya kasance haka..!
Bata son mgana saboda ranta ya riga ya baci shiyasa taja karamin Tsaki ta kauda kanta sai ma ta kara Sauri ta shige gidan bata son wata mgana ammh Hanne da Hamida sai suka saka Dariya har suna Tafawa Allah yasa Zafira na baya tare da yan garinsu.
Hamida ta kara riko gefen Hijabinta tana Fadin"Amina ki kallesa mana..Kai wlh ya Danmallan yayi kyau matuka..!
Amina ta Juyo a Fusace daidai sanda suka shiga get din gidan Baba mallam tace"Ba mijina ba..A"a ubana ne..Nace sai dai Ubana Hamida haba..Kin Dameni..!
Hamida da hannu suka kalli juna suna kunshe Dariya Hanne tace"Mijinki ne..Kuma ko bakomai ya Danmallan yana matsayin Uba ne agareki..!
Amina ta kalleta shekeke kafin tace"Allah..?Aiban yi mamaki ba..Kowa ya ganni yasan auran son zuciya yayi da yar cikinsa..!
Hamida da Hanne suka zaro ido Hanne tace"Amina kin ma kanki karya..Kaf gidanan ko ya Nazir bai kama kafar ya Danmallam akomai ba wlh..Baki magodema Allah ba kin Samu miji Kamar sa bama..!
Cikin Hargowa Amina tace"Ban gode ba..Domin bani nayi tallar kaina ba..Da kike mganar duk gidanan ba kmarsa to ni ina ruwana..Kinsan dai ina da Aminu..Kudi kyau nasaba ga yarinta bai isa ya nuna mai ba..!
Sai kawai ta saka musu kuka abunda basu taba gani ba in ta Tuna da Aminu bata iya Boye rauninta har Abada bazata taba mantawa dashi ba ko wani Hali yake ciki yanzu Allah masani..!
Jikinsu yayi sanyi suka kasa mgana ganin su zafira suna kokarin shigowa ne yasa ta juya ta fara tafiya suka mara mata baya Hanne na Fadin"Allah baki Hakuri Amina..Ammh aragama yayana ko Saboda ni..!
Amina ta Daga murya tana Fadin"Saboda ke..?ai ke din ba Mutumcinki nake gani ba Hanne..Ki kyaleni kada ki Tunzurani na yi miki Tijaran da zaki ji Haushina..!

Hamida tace"Hanne abar mganar..!
Daga haka suka kyaleta har shashen Hajiya sun shiga ba Dadewa sai ga Amaran da yan gusai,ba kamar wanchan karon ba Amina wannan karon batayi ra"ayi ba shiyasa da su Hanne suka ce tazo su raka amaran Nasiha Shashan su Haj.uwani da Nasara da gidan Aba Amina tace sai sun dawo ita ba inda zata jin haka sai suma jikinsu yayi sanyi suka ki binsu Zafirace dataga sunki zuwa sai ta Bisu.
Basu fito ba sai da Zafira tazo tana Fada musu amare zasu tafi ssannan suka fito Lokacin ma suna Falon Mallam ana musu nasiha da bankwana sai fito da kayan abinci su Ya Akilu suke motocin amaran suna kwasa suna sakawa acikin Booth ya Zeenatu Tawagar angoyen ta suna shirye harda mace Daya wacce zata tafi da amarya suka zo ya Abida dai tafi gata tunda su Anty Amarya na chan sai gobe zasu dawo..
Suna wajen sai gasu Haj.Nasara da Hajiya babba da goggo yakura sun fito dasu,kafin su ma mazan ne suka fara fitowa su ya uzairu da su ya Nasir ya Danmallanm da abokinsa Daga baya suka fito baba mallam da Aba sune ke rike da Amaran zuwa motocinsu Ba yau aka saba biki agidan ba ammh wannan na Dabam ne kamar yadda amaren suke na Dabam haka suke ta kuka kamar ransu zai fita Zeenatu da Abida.
Ana fito dasu suka kyalla ido suka hango su Amina suka kwace daga rikon Baba mallam suka nufesu Abida ta Rukunkume hanne tana kuka Zeenatu ta rumgume Amina da Hamida tana kuka duk da sun girmesu sune sakon su na kusa dasu akwai shakuwa sosai a Tsskaninsu.
Amina bata taba tsammanin zata yi kuka domin su ya Abida zasu tafi gidan mijinsu ba ammh yadda suke kuka suna rike su ne da kuma yadda Hamida da hanne ke kuka sai Amina ta fara Tsausayin kanta tana Tunanin in da gaske ne ta auri ya Danmallam kenan watarana itama zata iya Tsintar kanta cikin wannan yanayin sun bala"in bata Tsausayin da batasan sadda ta fara kuka ba takamkame Zeenatu suna kuka ita da Hamida ganin haka yasa Abida da Hanne suka zo suka hade suka yi Rumfa suna ta kuka kamar anyi mutuwa sai kallo ya koma garesu hajiya bata awajen ta koma cikin gida Haj.Nasara ne sai dangin mamanmu dana Aba na gusai.
Baba mallam tsaye kawai yayi bai ce komai ba ya jafar ne ya fara fada shi da ya Nasir suna fadin iskanci banza kukan uban me suka hadu suna ma mutane..!
Baba mallam ya kallessu yana Fadin"Ku kyalesu suyi kukan rabuwa da kannensu da gidansu..Gida fa ba kamarsa kuma aure ai yakin mata ne ko domin ku din maza ne shiyasa baku san wannan Raunin ba..!

Jin haka yasa sukayi shuru ya Danmallam bai ma san abunda ke faruwa ba suna haraban gida azatonsa amaren sum mika Aba kuma an kirasa a waya ya kebe agefe.
Haj.Nasara ne ta kalli Baba mallam tana Fadin"Maallam Uku tayi fa..Tafiyace kuma agabansu..!
Goggo yakura tace"Abidar kuma Angon yace jirgin karfe hudu zasu bi zuwa chan kuma ta Dutse zasu tashi..!
Baba mallam bai ce komai ba ya juya yana fadin"Ina Umaru..?
Ya Jafar yace"Yana daga cikin gida mallam..!
Kai Tsaye yace"Kiramin shi..!
Ba musu ya juya ya shiga ya kirasa sun ma hadu dasu ne zasu fito ya fadamai kiran mallan din sun fito kenan sai ga su Sakina da Sadiya da Tawagan yan"uwansu sun fito su ga Tafiyar amaran.
Daman Aliyu ya rako zai koma sai ga Kiran mallam sai ya isa wajensa yana zuwa Mallan ya dafa kafadarsa yana Fadin"Ka ga matarka da kannenka chan sun hade kai suna ta kuka. taimakeni ka lallasomin su kafi su Jafar sanyi su yanzu sai su ce zasu kai musu hannu..!
Inda mallam ya nuna mai yabi da kallo Takaici ya kumesa su din yara ne da zasu zauna suna ma mutane kuka kamar wasu marasa hankali sai karin wani takaicin wai matarsa shi fa har ga Allah ya Dauka Sakina ce da farko sai da ya kalli wajen yaga su hanne ne Tunanin sa ya basa wannan kazaman yarinyar ce bazai iyama mallam gaddama ba yasa ya kada kai yana Fadin"Shikenan mallam..!

Ko kafin ma ya isa garesu su ya Zulaihat sun isa suna faman lallashinsu su saki juna Sakina na gefe ta kame tana kallon kowa Daya bayan Daya sai ta ga Danmallam ya isa wajen yana mgana batajin me yake fadi,Ranta ya baci kishi ya Rufemata ido ganin Amina awajen badai ita yaje yana Lallashi ba..!
Sadiya ce tace"Ya sakina ga ya danmallam chan yana Lallashi..!
Bata tankata ba ta wuce fuu sai da ta isa wajen ne sannan taTsinkayi mganarsa yana fadin"Haka kurum zaku zo kuna ma mutane kukan banza..?
Kukan jin dadi kuke yi ko na menene..?Ko kuma an dake ku ne..Dillah ku sake su bana son Sakarci..!
Cikin Kiftawan ido suka Saki junansu suna Cigaba da gunjin kuka Daya bayan Daya ya kallesu kafin yace"Kowacce ta kama bakinta kafin nayi kasa kasa daku..!
Bai gama rufe baki ba suka yi shuru suna ajiyar rai Amina da Hanne suna rike da hannun juna kansu na kasa Amaran ya kallah sun yi Dama dama da Hijabinsu da hawaye da majina kafin yace"ku kuma ku wuce ku shiga mota..!
Da sauri ya Nazifa tace"Bari mu rikesu..!
Haj.Nasara na Dariyan su Amina tace"Danmallam da ka roki mallam ya bari su je koda kai Zeenatu ne zasu ji Dadi..!
Ko amsata bai bata ba illah su Amina Daya kalla cikin Taushinsa yace"Haj.Ba inda zasu je me zasu je suyi kuka..?Kowaccen ku ta koma cikin gida kuma ku cigaba da kukan ku gani Tunda anyi mutuwa ne..!
Chapter 83 · 0% Book details