Sashe 66
Ta Fita Zakka Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin bacin rai ta kalli Amina tana Fadin"Ai bake bace da kuka ba Amina..Umaru ne da kuka domin shi aka Gurbanta ma Rayuwa..Mutum kamili kamarsa an Hadasa da wacce bata Dace dashi ba Amina kamar ki ace kin san Namiji..?Daman nasan wannan Firiritan nan naki watarana sai yakai ga haka har kina mana wani kukan banza to wlh ki kama bakin ki ko na sake Dana miki Dukan da sai kin Raina kanki Sakarya wawiya mara Tunani kawai..!
Ta karishe Fada Cikin Huci Amina na kuka tana Fadin"Wlh bana bin Maza..Ni ba yar iska bace..!
Yaya tace"Shi Jafarun zai miki karya ne..?yaron da yace ya ganki Rumgume dashi Ubanki ne shi..?wlh in bakin ki bai Mutu ba,zaki sha wahala ke baki ji kunya da Tsausayin kanki ba..?Mahaifnki nachan kwance asibiti taa Dalilinki Tir da Halinki Amina Tir wlh..!
Tafada Tana nuna ta da Hannu Cikin wani yanayi Hanne ce ta Dukar dakai Cikin wani yanayi tana Fadin"Don Allah yaya kiyi hakuri..Nasan Wacece Amina sai dai in kuskure akayi wlh bazata aikata abunda akace ba..!
Yaya bata samu bakin mgana ba Mamanmu Data Daga Labule tun dazu Tana jin yaya tace"Hanne ku kyalesu..Duk abunda zasu fada sun Dade basu fada ba..Abu Daya na sani Amina ba Haka take ba..Amina bazata Watsar da Tarbiyanta ba..Akwai abunda ba Daidai ba..!
Yaya tayi mirmishin Takaici kafin ta Juyo tana kallon Mamanmu Cikin Sanyin Muryanta tace"Yaushe ne Ranar da Amina zatayi kuskure ki nuna mata tayi ba Daidai ba..?
Yaushe ne Ranar da zaki bi bayam gaskiya ba bayan Amina ba..?
Mamanmu tace"Sai Ranar da na Tabbatar da gaskiyan kuke fada yaya..Ammh ayanzu har gaban Abada bazan bar Tsagin Amina ba..Amina Diyatace da nake mata soyayyar da ko ya'yan dana Haifa da cikina ban musu shi ba,Har abada bazan Daina Fadin kunyi kuskure Amina ba haka take ba..!
Yaya Batace komai ba kawai ta girgiza ta raba ta gefen mamanmu ta fice Mamanmu ta bita da kallo kafin ta maida kallonta kan su Hamida tana Fadin"Ku bata baki..Bari akawo abinci taci tasha mgani..!
Daga haka ta saki Labulen Dakin ta koma to a wannan gabar sai kukan Aminan ya tsaya cak kamar an Dauke ruwa Zuciyarta ta Bushe bata jira Lallashin kowa ba ta Gyara zama Daga zaune ta tada sallah domin jikinta har yanzu atsame yake bata iya Tsayuwa waje daya ta Gudanar da sallar ba..!
Wajen karfe Tara na Dare sai ga Ya Jafar da ya Nasir sun zo Amina na Daki taji Ya Jafar na fadin"Ina ita mara kunyar Aminar .?
Yaya Data Fito daga Daki tana gyara zaman Hijabin jikinta Da zasu tafi asibiti tace"Tana ciki..Tun dazu da taji Labarin abunda ya faru take kuka..!
Yaya Jafar sai da ya Lailaya ashar kafin yace"Yar iskace bata Daku bane..Ai wannan auran Baba mallam ya Daurasa ne ba domin ya dace ba wlh..!
Ya Nasir yace"Uhmm.Ni kuma ina ganin Daidai ne Jafar..Amina sai irin su ya Danmallan ne daidai dasu..!
Ya Jafar yace"Kamanta ne shi fa ba irin mu bane bai da Hayaniya bai kuma kaimu Zafi ba..!
Ya Nasir yace"Duk na yarda..Ammh kuma ya fimu Shekaru sannan cikin Ruwan sanyu yake Ladabtar da Mutum..Wlh ina ji ajikina Wannan al"amarin ba Tsarin Mallam bane Tsarin Daga Allah ne..Abu ne da Hasashe ko Tunanin mu bai taba kawo ba yanzu muka gama mgana da Ya Nazir shima haka yace..!
Ya Jafar yace"Nima ya Kirani yana Tambayana sai dai ina mamakin waya fadamai..?
Ya Nasir yace"Tab to har su Nazeem Dake Zaria sun ji Labari..Ya Danmallan din ne ban da masaniya ko ya sani..?
Mamanmu na zaune saman Tabarma cikin baranda tace"Nima yaran nan sai kirana suke Zulahait dai tace min Aisha ta Kirata ta fadamata itama tace Abida ta sanar da ita da wayar Hajiya..Suma mamaki suke suna son ji ko gaskiya ne nace musu gaskiya ne..!
Ya jafar yayi ajiyar rai kafin yace"Dawa dawa zamu koma asibitin..?
Mamanmu tace"Da yaya zaku je ni bazani ba zan zauna wajen Amina..!
Ya zeenatu tayi karaf tace"Ya Jafar don Allah zani..!
Tana rufe baki Hamida da Hanne suka Fito suna Fadin"Muma zamu don Allah..!
Sai da ya Hararesu kana yace"Bazaku ba..gobe da safanan za"a sallamesa..!
Mamanmu ce tace"Kaje dasu don Allah Jafar..Oh na manta ina mai ciwon kunni..?
Ya jafar yace"Yayi sauki sosai kin ma Tunamin ban karbi mganin da Baba Mallam yace nazo na karba ba..bari mu dawo..kuzo mu tafi Dare yayi kuma bana son rawan jiki yarinya ta natsu..!
Ba musu suka shiga Taitayinsu Ya Zeenatu ce ta Dauko kwandon data Zuba abinci yaya daman da hijabinta Jawad na gefenta sai su Hamida sallama suka ma mamanmu suka Fice,ya zeenatu da Hamida Motar Ya Nasir suka shiga ashe matarsa na gaba Anty Fadila da ita za"aje..!
Yaya kuma da Hanne suna Motar ya Jafar
Koda sukaje Aba yaji Sauki sosai sun samesa yana cin kayan marmari ga Ferfesun kayan ciki ne,da suka tambayesa wa ya kawo masa..?
Yace Hajiya Babba da Hajiya uwani yanzu suka fita Idi Direba ya kawosu ya riga ya koshi shiyasa suka ijiye abunda suka zo dashi Aba ya amsa gaisuwan Hamida da Hanne ya Kallesu Cikin kulawa yana Fadin"Ina Amina..?
Hamida tace"Tana gida Baba..!
Daman ta sani Amina na ransa ita din yarinya ce mai shiga rai kaunar da iyayanta Biyu suke mata Allah ne kadai yasanta sai dai baza su bayyanata ba Saboda kawaici da kuma Tunanin ba ita kadai suka Haifa ba
Daganan bai kara mgana ba Jawad yaja kan jikinsa yana Tambayansa ya makaranta yana bashi amsa basu Dade da zuwa ba sai ga Baba mallam ya shigo Cikin shigar Alkyabbansa da Rawaninsan nan suka Ramkwafa suna gaishesa ya amsa cikin Sakin Fuska yana kallon Su Nasir kafin yace"Ashe nan kuka zo..?
Kan Nasir na kasa yace"Eh Baba..Na kawo Fadila ne ganin bata zo ba..!
Yana zama saman kujeran Dake gefen gadon Aba da Ya jafar ya tashi ya bashi yace Lokaci daya"Yayi kyau..Kun kyauta Allah yayi muku albarka..!
Su hamida ya kallah ita da Hanne kafin yace"Naga zara ban ga wata ba..Ina mamana..?
Wannan karon Hanne tace"Tana gida Ita da Mamanmu Baba..!
Kai ya gyada kafin yace"In ta warware zamu daidaito ni da uwata insha Allahu..!
Ba wanda yayi mgana sai Su ya Jafar ne suka Murmusa kawai,Baba Sa"idu ya kallah yana Fadin"Kai ai ka warke tunda naga har kana iya Daukan Jawaad..!
Baba Sa"idu yace"Da sauki Baba..nacema ce su sallame ni yau sukace sai da safe in Likita yazo..!
Baba Mallam yace"Gwara ka kara samun karfin jikin ka kafin ka koma gida..!
Ganin suna gaisawa da Aba yasa su ya jafar sukayi shirin tafiya sai alokacin Baba Mallam ya kalli yaya yana Fadin"Hadiza bana son ganin wannan Damuwar afuskarki Daga gani kin ta kuka..Sa"idu ne babban banza shi ga inda ya kawomu ke kuma kina chan kina kuka har wata Cuta ta kamaki ta Miki illah ina amfaninta..?Ina ce Amina ce Matsalarku..?to ta fita Daga Hannunku ta koma karkashin ikon Umaru sai ku daina Damuwa..Ina ce ba Shikenan ba..?
Yafada yana kallon Aba da kunya yasa ya Sunkuyar da kansa Yaya kuwa kanta na kasa batayi mgana ba har sukayi musu sallama suka fice suka bar Baba Mallam anan da Jawad daya makale ma Aba yaki tafiya Baba Mallam yace a kyalesa in zai taho zasu taho tare. !
******
Tun bayan Fitarsu daga gidan ta Mike ta Leka Amina abinci ta Debomata Farar Shinkafa da Miya Kadan Amina taci don ma Mamanmu tana bata baki Tana Hadawa da Lallashinta Fadi take yi"Ki daina damun kanki ni nasan babu abunda kika aikata..Kuma mganar auran in baki so batare da kowa ya sani ba zan kira shi Danmallan din na Rokesa ya Sauwake miki..Ina Zaki iya da Sakina..?Matansa fa Biyu Kina yarinya Dake duka duka Shekarunki nawa Amina..?Sha Shidda fa Ko sha bakwai din Baki cika ba Har yanzu..Gaskiya akwai kwa ruwa acikin Hukuncin Mallam..!
Take fada cikin bayyana bacin ranta Amina kallonta kawai take batayi mgana ba to me zatace..?Tayi mgana ai bai da amfani komai ya riga ya kare ta rasa Aminu ta gama rasa komai Mganar Rabuwa da Ya Danmallam kuma bata isa ba har gaban Abada bazata watsama Baba Mallam kasa a ido ba kamar yadda bazata watsama Mamanmu ba uwa uba gasu Aba da yaya bata Fatan wani abu ya kara Giftawa,Ta riga ta sani Kaddara ta,kaita wani bingiren da Har yanzu ta kasa dora kanta a inda kaddaran ta jata ta kaita in tana tunawa ma sai wani Rauni da Faduwar gaba su Lulleta waje ne da har Abada zatayi Daraja ba ta sani..!
Har mamanmu ta gama bata tana ta Mita panadol ta bata tasha sai kuma ta shafa mata man zafi ajikinta Da Amina taji Dadinsa kwarai hawaye take yi da kukan zucci acikin ranta tana kara Ninka kaunar dake yi ma Mamanmu tana Fadin dama dama ana Sauya wani abu da Tuni ita Amina ta Dade da Sauya Yaya da Mamanmu amtsayin uwa..!
Amina bata sani ba Allah yana Boyemana wani abun ne kafin mu sani saboda kila alokacin in ya bayyana mana bamu da karfin gwiwan da zuciyan da zamu iya Dauka..!
Boyayyin Fuskokin wani Lokacin Alheri ne garemu kila sanda zasu bayyana Mun Tsaya da kafafunmu Raunin da zai bayyana garemu kadan ne..!
Sai da ta tabbatar da barci ya fara Daukan Amina kana ta bar dakin Dakinta ta koma bata Dangana ako"ina ba sai Cikin Bedroom dinta tana shigowa wayarta Dake kan gadonta ta sake Daukan kuwwa alamun kira ya shigo Da hanzari ta karisa ta Dauki Wayar sunan wacce ke kiran yasa bata Tsaya bata Lokaci ba ta Daga Daman ta sani zata kirata itama din Jiran kiran nata take yin bayan Tabbattuwaar abunda basu taba Tsammani ba..!
"Dayyaba Da saninki komai nawa ya Rushe..Dayyaba da saninki akamin wannan yankar bayan..Da Saninki kika bari yarinyar da ta Ratso cikin gabar aikina alokacin danake Hasashen ina gabda cin nasara..Na sani hakan zata faru shiyasa nake ta Kiranki tun dazu baki Daga Kirana ba..!
Ta karishe Fada Cikin Huci Amina na kuka tana Fadin"Wlh bana bin Maza..Ni ba yar iska bace..!
Yaya tace"Shi Jafarun zai miki karya ne..?yaron da yace ya ganki Rumgume dashi Ubanki ne shi..?wlh in bakin ki bai Mutu ba,zaki sha wahala ke baki ji kunya da Tsausayin kanki ba..?Mahaifnki nachan kwance asibiti taa Dalilinki Tir da Halinki Amina Tir wlh..!
Tafada Tana nuna ta da Hannu Cikin wani yanayi Hanne ce ta Dukar dakai Cikin wani yanayi tana Fadin"Don Allah yaya kiyi hakuri..Nasan Wacece Amina sai dai in kuskure akayi wlh bazata aikata abunda akace ba..!
Yaya bata samu bakin mgana ba Mamanmu Data Daga Labule tun dazu Tana jin yaya tace"Hanne ku kyalesu..Duk abunda zasu fada sun Dade basu fada ba..Abu Daya na sani Amina ba Haka take ba..Amina bazata Watsar da Tarbiyanta ba..Akwai abunda ba Daidai ba..!
Yaya tayi mirmishin Takaici kafin ta Juyo tana kallon Mamanmu Cikin Sanyin Muryanta tace"Yaushe ne Ranar da Amina zatayi kuskure ki nuna mata tayi ba Daidai ba..?
Yaushe ne Ranar da zaki bi bayam gaskiya ba bayan Amina ba..?
Mamanmu tace"Sai Ranar da na Tabbatar da gaskiyan kuke fada yaya..Ammh ayanzu har gaban Abada bazan bar Tsagin Amina ba..Amina Diyatace da nake mata soyayyar da ko ya'yan dana Haifa da cikina ban musu shi ba,Har abada bazan Daina Fadin kunyi kuskure Amina ba haka take ba..!
Yaya Batace komai ba kawai ta girgiza ta raba ta gefen mamanmu ta fice Mamanmu ta bita da kallo kafin ta maida kallonta kan su Hamida tana Fadin"Ku bata baki..Bari akawo abinci taci tasha mgani..!
Daga haka ta saki Labulen Dakin ta koma to a wannan gabar sai kukan Aminan ya tsaya cak kamar an Dauke ruwa Zuciyarta ta Bushe bata jira Lallashin kowa ba ta Gyara zama Daga zaune ta tada sallah domin jikinta har yanzu atsame yake bata iya Tsayuwa waje daya ta Gudanar da sallar ba..!
Wajen karfe Tara na Dare sai ga Ya Jafar da ya Nasir sun zo Amina na Daki taji Ya Jafar na fadin"Ina ita mara kunyar Aminar .?
Yaya Data Fito daga Daki tana gyara zaman Hijabin jikinta Da zasu tafi asibiti tace"Tana ciki..Tun dazu da taji Labarin abunda ya faru take kuka..!
Yaya Jafar sai da ya Lailaya ashar kafin yace"Yar iskace bata Daku bane..Ai wannan auran Baba mallam ya Daurasa ne ba domin ya dace ba wlh..!
Ya Nasir yace"Uhmm.Ni kuma ina ganin Daidai ne Jafar..Amina sai irin su ya Danmallan ne daidai dasu..!
Ya Jafar yace"Kamanta ne shi fa ba irin mu bane bai da Hayaniya bai kuma kaimu Zafi ba..!
Ya Nasir yace"Duk na yarda..Ammh kuma ya fimu Shekaru sannan cikin Ruwan sanyu yake Ladabtar da Mutum..Wlh ina ji ajikina Wannan al"amarin ba Tsarin Mallam bane Tsarin Daga Allah ne..Abu ne da Hasashe ko Tunanin mu bai taba kawo ba yanzu muka gama mgana da Ya Nazir shima haka yace..!
Ya Jafar yace"Nima ya Kirani yana Tambayana sai dai ina mamakin waya fadamai..?
Ya Nasir yace"Tab to har su Nazeem Dake Zaria sun ji Labari..Ya Danmallan din ne ban da masaniya ko ya sani..?
Mamanmu na zaune saman Tabarma cikin baranda tace"Nima yaran nan sai kirana suke Zulahait dai tace min Aisha ta Kirata ta fadamata itama tace Abida ta sanar da ita da wayar Hajiya..Suma mamaki suke suna son ji ko gaskiya ne nace musu gaskiya ne..!
Ya jafar yayi ajiyar rai kafin yace"Dawa dawa zamu koma asibitin..?
Mamanmu tace"Da yaya zaku je ni bazani ba zan zauna wajen Amina..!
Ya zeenatu tayi karaf tace"Ya Jafar don Allah zani..!
Tana rufe baki Hamida da Hanne suka Fito suna Fadin"Muma zamu don Allah..!
Sai da ya Hararesu kana yace"Bazaku ba..gobe da safanan za"a sallamesa..!
Mamanmu ce tace"Kaje dasu don Allah Jafar..Oh na manta ina mai ciwon kunni..?
Ya jafar yace"Yayi sauki sosai kin ma Tunamin ban karbi mganin da Baba Mallam yace nazo na karba ba..bari mu dawo..kuzo mu tafi Dare yayi kuma bana son rawan jiki yarinya ta natsu..!
Ba musu suka shiga Taitayinsu Ya Zeenatu ce ta Dauko kwandon data Zuba abinci yaya daman da hijabinta Jawad na gefenta sai su Hamida sallama suka ma mamanmu suka Fice,ya zeenatu da Hamida Motar Ya Nasir suka shiga ashe matarsa na gaba Anty Fadila da ita za"aje..!
Yaya kuma da Hanne suna Motar ya Jafar
Koda sukaje Aba yaji Sauki sosai sun samesa yana cin kayan marmari ga Ferfesun kayan ciki ne,da suka tambayesa wa ya kawo masa..?
Yace Hajiya Babba da Hajiya uwani yanzu suka fita Idi Direba ya kawosu ya riga ya koshi shiyasa suka ijiye abunda suka zo dashi Aba ya amsa gaisuwan Hamida da Hanne ya Kallesu Cikin kulawa yana Fadin"Ina Amina..?
Hamida tace"Tana gida Baba..!
Daman ta sani Amina na ransa ita din yarinya ce mai shiga rai kaunar da iyayanta Biyu suke mata Allah ne kadai yasanta sai dai baza su bayyanata ba Saboda kawaici da kuma Tunanin ba ita kadai suka Haifa ba
Daganan bai kara mgana ba Jawad yaja kan jikinsa yana Tambayansa ya makaranta yana bashi amsa basu Dade da zuwa ba sai ga Baba mallam ya shigo Cikin shigar Alkyabbansa da Rawaninsan nan suka Ramkwafa suna gaishesa ya amsa cikin Sakin Fuska yana kallon Su Nasir kafin yace"Ashe nan kuka zo..?
Kan Nasir na kasa yace"Eh Baba..Na kawo Fadila ne ganin bata zo ba..!
Yana zama saman kujeran Dake gefen gadon Aba da Ya jafar ya tashi ya bashi yace Lokaci daya"Yayi kyau..Kun kyauta Allah yayi muku albarka..!
Su hamida ya kallah ita da Hanne kafin yace"Naga zara ban ga wata ba..Ina mamana..?
Wannan karon Hanne tace"Tana gida Ita da Mamanmu Baba..!
Kai ya gyada kafin yace"In ta warware zamu daidaito ni da uwata insha Allahu..!
Ba wanda yayi mgana sai Su ya Jafar ne suka Murmusa kawai,Baba Sa"idu ya kallah yana Fadin"Kai ai ka warke tunda naga har kana iya Daukan Jawaad..!
Baba Sa"idu yace"Da sauki Baba..nacema ce su sallame ni yau sukace sai da safe in Likita yazo..!
Baba Mallam yace"Gwara ka kara samun karfin jikin ka kafin ka koma gida..!
Ganin suna gaisawa da Aba yasa su ya jafar sukayi shirin tafiya sai alokacin Baba Mallam ya kalli yaya yana Fadin"Hadiza bana son ganin wannan Damuwar afuskarki Daga gani kin ta kuka..Sa"idu ne babban banza shi ga inda ya kawomu ke kuma kina chan kina kuka har wata Cuta ta kamaki ta Miki illah ina amfaninta..?Ina ce Amina ce Matsalarku..?to ta fita Daga Hannunku ta koma karkashin ikon Umaru sai ku daina Damuwa..Ina ce ba Shikenan ba..?
Yafada yana kallon Aba da kunya yasa ya Sunkuyar da kansa Yaya kuwa kanta na kasa batayi mgana ba har sukayi musu sallama suka fice suka bar Baba Mallam anan da Jawad daya makale ma Aba yaki tafiya Baba Mallam yace a kyalesa in zai taho zasu taho tare. !
******
Tun bayan Fitarsu daga gidan ta Mike ta Leka Amina abinci ta Debomata Farar Shinkafa da Miya Kadan Amina taci don ma Mamanmu tana bata baki Tana Hadawa da Lallashinta Fadi take yi"Ki daina damun kanki ni nasan babu abunda kika aikata..Kuma mganar auran in baki so batare da kowa ya sani ba zan kira shi Danmallan din na Rokesa ya Sauwake miki..Ina Zaki iya da Sakina..?Matansa fa Biyu Kina yarinya Dake duka duka Shekarunki nawa Amina..?Sha Shidda fa Ko sha bakwai din Baki cika ba Har yanzu..Gaskiya akwai kwa ruwa acikin Hukuncin Mallam..!
Take fada cikin bayyana bacin ranta Amina kallonta kawai take batayi mgana ba to me zatace..?Tayi mgana ai bai da amfani komai ya riga ya kare ta rasa Aminu ta gama rasa komai Mganar Rabuwa da Ya Danmallam kuma bata isa ba har gaban Abada bazata watsama Baba Mallam kasa a ido ba kamar yadda bazata watsama Mamanmu ba uwa uba gasu Aba da yaya bata Fatan wani abu ya kara Giftawa,Ta riga ta sani Kaddara ta,kaita wani bingiren da Har yanzu ta kasa dora kanta a inda kaddaran ta jata ta kaita in tana tunawa ma sai wani Rauni da Faduwar gaba su Lulleta waje ne da har Abada zatayi Daraja ba ta sani..!
Har mamanmu ta gama bata tana ta Mita panadol ta bata tasha sai kuma ta shafa mata man zafi ajikinta Da Amina taji Dadinsa kwarai hawaye take yi da kukan zucci acikin ranta tana kara Ninka kaunar dake yi ma Mamanmu tana Fadin dama dama ana Sauya wani abu da Tuni ita Amina ta Dade da Sauya Yaya da Mamanmu amtsayin uwa..!
Amina bata sani ba Allah yana Boyemana wani abun ne kafin mu sani saboda kila alokacin in ya bayyana mana bamu da karfin gwiwan da zuciyan da zamu iya Dauka..!
Boyayyin Fuskokin wani Lokacin Alheri ne garemu kila sanda zasu bayyana Mun Tsaya da kafafunmu Raunin da zai bayyana garemu kadan ne..!
Sai da ta tabbatar da barci ya fara Daukan Amina kana ta bar dakin Dakinta ta koma bata Dangana ako"ina ba sai Cikin Bedroom dinta tana shigowa wayarta Dake kan gadonta ta sake Daukan kuwwa alamun kira ya shigo Da hanzari ta karisa ta Dauki Wayar sunan wacce ke kiran yasa bata Tsaya bata Lokaci ba ta Daga Daman ta sani zata kirata itama din Jiran kiran nata take yin bayan Tabbattuwaar abunda basu taba Tsammani ba..!
"Dayyaba Da saninki komai nawa ya Rushe..Dayyaba da saninki akamin wannan yankar bayan..Da Saninki kika bari yarinyar da ta Ratso cikin gabar aikina alokacin danake Hasashen ina gabda cin nasara..Na sani hakan zata faru shiyasa nake ta Kiranki tun dazu baki Daga Kirana ba..!