Sashe 11
Ta Fita Zakka Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*AMINU GUSAI* basu hada komai ba sai da sun Taba Hada yin Makarantar allo anan garin na Bichi kano A talabijin yaga Malam yunusa yana ganinsa ya ganesa Domin alokacin ba wanda baisan Yunusa bazanga ba, Yayi Tattaki har gida yaje ya samesa sukayi Zumunci da Tambayan bayan Rabuwa,Aminu ya sanar dashi bayan Sun yi Sauka yayi karatu shima Har matakin Masters sannan kuma sai ya Fada Siyasa Daman gidansu gidan yan Boko ne da kuma Tsofaffin masu Kudi Dayake awanchan zamani Karatun allo yana da Daraja ba kamar yanzu Domin yawancin manyan mu na yanzu in da zasu baka Tarihinsi zaka Ji cewa sai da suka fara da Karatun allo kafin su dawo su Dora na bokon
Aminu yaji mamakin ganin yadda Malam Yunusa ya koma sannan ya kara yarda ma kamsa yana na nan bai Sauya ba Tunda Har ya iya bari Garin Madina yazo kasarsa yana Wahala.
Daganan Zumunci ya fara Har Ya kawo Iyalinsa Hadiza da Dansa Daya mai Suna SA"IDU mai kimamin Shekaru goma sha biyar alokacin tun gaanin Farko da Yunusa da Zainabu sukayi ma Sa"idu ya shiga ransu Matuka suna son yara suna kewarsu sai dai Allah bai basu ba,Sannan ga Hadiza mai kunya da karamci Sa"idu shima yana son zuwa gidan Malam Yunusa kodomin yaga Dabbobi kaunarsu acikin Ransa yake Ranar har cema Malam Yunusa yayi Baba ina son ka bani Rago in na kara girma na kula Dashi alokacin gaban Dukkan ne ya Fadi mganar Malam Yunusa ya Dafa kansa Cikin Kauna yace"Insha Allahu Watarana kai zaka kula dssu Sa"idu..Fatana ka Dake da Karatu..!
Wannan mgana ta saka Sa"idu Farinciki kuma abunga ga yaro ya rike mganar acikin kansa.
Tundaga Ranar yake murna yana Fadin in ya girma zai zama mai kula da Raguna kowa yana ganin Shirme ne da yarinta.
Duk da alokacin Zainabu zata girmema Hadiza ita Allah ya bata Haihuwan da Wuri tana da kananun Shekarunta Ammh sun zama kawaye tunda Zainabu batasan kowa agarin ba sai suka zama kamar yan"'uwa koda yaushe suna ziyatar juna Sannan Sa"idu duk karshen Sati wajensu yake yi kaunar yaron ta fara ne tun Tuni Sannan Shi kauna Allah ke hadashi ma Mutum ba.
Akwai Ranar da Malam Yunusa suna mgana da Aminu ya kallesa yana Fadin"Aminu ina kaunar Sa"idu ina jinsa kamar dan cikina..Ina ji kamar ya zauna Dani har Abada..!
Alokacin Aminu Dariya yayi ya Dafa Kafadar Malam Yunusa yana Fadin"Haba yunusa ai ni da kai mun Zama Daya..Wlh har araina na yarda da wannan kaunar Dake Tsakaninka da Sa'idu Dama Hadiza nada juna Biyu sai ta Haifa mana wani kai kuma ku rike Sa"idu kai da Zainabu har abada na tabbata ko bayan Raina Sa"idu zai fi Alheri Dakai Fiye Dani..!
Wata mganace da Malam Yunusa ya Dauketa kamar Fadice sai dai ba Haka bane Har azuciyan Aminu haka take Malam Yunusa bai Tabbatar ba sai da Aminu ya Tara Duka yan"uwansa ya Fadamusu ba wanda yayi gaddama Sanin Waye Malam Yunusa Shiyasa kowa yayi Na"am da Batun Hadiza ma bata kawo Damuwa ba macece mai kunya da kawaici Duk da kasancewarta Bazanfara gaba da baya.
Malam Yunusa yayi kukan Murna Aranar da Aminu da Hadiza suka Dauko Sa"idu da duka kayansa suka kawo musu shi Har abada shi da ZAINABU sun kasa Daina kuka suna ganin kamar mafarki ne sai dai Zahiri ne,Sa"idu bai damu ba ya Saki Jikinsa Sosai Saboda Dabbobi daman yafi son gidan Baba Malam kamar yadda Sa'idu shine Mutum na Farko Daya Fara Radamai wannan suna kuma yake binsa yana alfahari dashi.
Abu kamar wasa karamar mgana ta zama ba Sa"idu ya dawo hanun Malam Yunusa da matarsa zainabu abun Tsusayi Cikin Da Hadiza ta Samu ta Haifeshi ba rai ammh duk da Haka basu Damu Sa"idu ya cigaba da zuwa makarantar Boko sannan kuma Malam da Zainabu suna Karantar dashi karantun addini acikin Gida sannan suna iya bakin kokarinsu wajen Tarbiyansa da Rike Amanar da aka basu
Wajen sau uku Hadiza na Haihuwa ba rai sai ana Hudu ta Tsaya macece mai Suna Hafsah sunan Mahaifiyar Aminu ce suna cemata Husai sai kowa ya samu nashi Sa"idu na zuwa ganinsu Lokaci bayan Lokaci kamar yadda suma basa gajiya da Ziyartan Juna.
Tun alokacin ana ta yima Malam yunusa Tayin ya"ya Domin ya kara aure ko zai Samu Haihuwa sai yace A"a Domin Zainabu nada kima awajensa,Sannan koda an mai mganar Haihuwa sai yace Sa"idu ya isheni Rayuwar Duniya da Lahira Saboda irin kauna da Shakuwar Dake Tsakaninsu suna bashi Dukkan wani Gatan Duniya sai dai suna kokari wajen Kula da Tarbiyansa.
Cikin Ikon Allah kamar yadda Malan Yunusa yace Haihuwa ta Allah ce Hakan ce ta kasance Domin Sa"idu ko Shekara uku bai yi da Dawowa Hannunsu ba Zainabu ta samu Ciki kuma Haihuwarta na Farko Ta Haifi Namiji Malam Yunisa ya saka masa Suna UMAR IBN YUNUS..!
Koda zainabu ta Haihu mganarsa Dayane Sa"idu ne babban yaro na Domin kafin na Samu Umar Sa"idu na Haifa,Duk da Mutane sunsan ba Dansa bane ammh suna Girmama Kaunar dake Tsakaninsu kuma koda suka samu nasu babu abunda ya Sauya Daga soyayyar da sukemai.
Yayinda Aminu Daga Husai Hadiza bata kara ko barin wata ba kuma basu Damu ba Tunda Da ga Allah ne sun Tabbatar Sa"idu yayi Dace da iyaye nagari kuma ko bayan ransu Watarana sai yayi alfahari da hakan
Tundaga lokacin Haihuwa ta Budema Hajiya Babba Daga Umar tazo tayi Nazir wanda Tsakaninsu ba Nisa alokacin kuma Malam Yunusa ya kara aure Shima Bashi matar akayi sun je Da"awa garin Tsafe na Jahar Zamfara gidan Malamin da suka sauka Malam Hamza ya Dauki Yarsa Kwara Daya cikin jerin ya"yansa Uwani ya bama Yunusa shi kuma bazai iya Bijiremasa ba ya karba Hannu Bibbiyu achan aka Daura aure sai dai ya Dawo da mata kawai Sannan bai samu matsala da Zainabu ba ta karbi Uwani Hannu Bibbiyi suka cigaba da zaman Amana ko ita sai Daga baya tasan ba Malam ya Haifi Sa"idu ba shima sai da ya Fadamata ta yarda ammh tana Girmama wannan kaunar Daga Malam din har Zainabun da ya"yanta basu da Mganata sai ta Sa"idu ko"ina kaje agidan nan Sa"idu ne wannan kaunar Daga Allah ne.
Haka Rayuwa ta cigaba da gangarawa da Dadi ba Dadi Malam na Cigaba da nenan sani da Da"awa sannan Lokaci Daya yana karantar matasa Abunda ya sani na Addini Alokacin Aminu gusai akayi Chanjin gwannati bai samu Kakin majalisa ba sai aka Nada wani Daga Shekarar kuma Jinya ta kamasa na Ciwon kafa Daga Sama Sama sai abu ya Zarce baya iya tashi Sai dai a kwantar atayar Jinya tayi Jinya anyi mganin Asibiti anyi na gargajiyam Duka ba"a Dace ba Sai da Duka Abunda Alhaji Aminu ya Tara ya kare Malam ma bai zauna ba Shima Duk in da yaji wani mgani zai amsomai Sai dai ita Kaddaran Allah Daman Dayace komai Tsalle Tsallen bawa bai isa ya Gujemata ba, Aminu gusai ya Rasu Lokacin da Jinyarsa ta karar da komai ya Rasu ya bar Matarsa Hajiya Hadiza da Yarsa Husai da Sa'idu ko kafin Rasuwarsa ya kara Jadaddama Malam Sa'idu nasa ne har Abada wannan karamcin na Aminu Malam har ya koma ga Allah bazai manta ba.
Yaso ya Dauko Husai da Hajiya Hadiza ya Rikesu sai yan"uwan Aminu suke roko alfarman ya bar musu Rikonsu sai ya kyale musu Tunda karamcimsu garesa mai girma ne Gidan yayan Aminu Hajiya Hadizan ta koma da zama ita da Husai ba kyashi ba Hasaada riko na Tsakani ga Allah Sa"idu Lokacin yana makarantar kwana ta Hassan gwarzo Dake kano Aminu ya rasu sai da ya Dawo yaje yayima iyayensa gaisuwa Kowa bashi yake tsausayi ba Domim cewa ake Aminu yayi ma Sa"idu gata Domin Uba irin Malam abun Alfaharin kowani Cikakken D'a ne.
Tun Rasuwar Aminu Garin Gusai ya Fita kan Malam Yunusa batare da Shawara da kowa ba ya Fara Binciken yadda zai tashi Daga garin Dayake Tunamai da adalin Amini kamar Aminu,Ba Dadewa ya samu Cikakken bayani kan garin Gumel da yadda Suke da amfanin gona da Sauran Cigaba ba Dadewa ya mallaki Fili a wannan anguwan ta Zango ya Fara Gina iya adadin ida zasu zauna.
Sannan ya samar da Katon Fili Domim Kiwo yayi alkawarin Sa"idu sai ya zama wani abu sannan yana da Burin Cikamai wannan Burin nasa.
Dawowar Malam Yunusa garin Gumel baima Hajiya Hadiza Dadi ba Saboda ta Saba da Hajiya Babba sosai sannan Husai ta Saba da su Umar ammh bata da yarda zatayi tun anan din ma ba Wahala take ciki Yan"uwan Aminu ba suna Rike dasu tsakani ga Allah Duk da itama Duka na gida ne
Shekarun da suka Shude masu yawa ne sannan sun zo da Nasarori da Dadama da kuma akasinsu Sa"idu ya gama Secondary ya Fada Jami"ar garin Dutse yana karantar agric abunda ya Shafi noma da kiwo Ko alokacin Gidan gonar Baba Mallam Dake kusa dasu Sa"idu ke da Ahakin kula dasu Haka Allah ya yisa Zama Cikin Dabbobi sune ke sakashi Nishadi sannam Agarin ba wanda yasan Sa"idu ba yaron Malam bane Sannan kowa Dauka yake Shine Babba sannan su Umar Duka kannensa ne,Malam bai yi kasa a gwiwa ba anan din ma ya Cigaba da Karantar wa Ya Hakura da neman ilimi ya Zauma yana karantar da Duka Dalibin Dayazo wajensa neman ilimi Sannan bai da ina zuwa Da"awa ba duk inda za"a je dashi ake zuwa.
Zuwa Lokacin Malam ya Kara auran yar nan garin Jigawa ce Hajiya Nasara ita yar Masu kudi ce sannan zuwa Lokacin Gidan Malam ya fara Cika da Ya"ya kamar yadda yake fata sannan bai manta da Hajiya Hadiza da Husai ba da Lokaci bayan Lokaci suna zuwa suma suna zuwa sannan babu abunda suka nema suka rasa na bangaran Rayuwa.
*******
*Bayan shekaru Talatin..*
Aminu yaji mamakin ganin yadda Malam Yunusa ya koma sannan ya kara yarda ma kamsa yana na nan bai Sauya ba Tunda Har ya iya bari Garin Madina yazo kasarsa yana Wahala.
Daganan Zumunci ya fara Har Ya kawo Iyalinsa Hadiza da Dansa Daya mai Suna SA"IDU mai kimamin Shekaru goma sha biyar alokacin tun gaanin Farko da Yunusa da Zainabu sukayi ma Sa"idu ya shiga ransu Matuka suna son yara suna kewarsu sai dai Allah bai basu ba,Sannan ga Hadiza mai kunya da karamci Sa"idu shima yana son zuwa gidan Malam Yunusa kodomin yaga Dabbobi kaunarsu acikin Ransa yake Ranar har cema Malam Yunusa yayi Baba ina son ka bani Rago in na kara girma na kula Dashi alokacin gaban Dukkan ne ya Fadi mganar Malam Yunusa ya Dafa kansa Cikin Kauna yace"Insha Allahu Watarana kai zaka kula dssu Sa"idu..Fatana ka Dake da Karatu..!
Wannan mgana ta saka Sa"idu Farinciki kuma abunga ga yaro ya rike mganar acikin kansa.
Tundaga Ranar yake murna yana Fadin in ya girma zai zama mai kula da Raguna kowa yana ganin Shirme ne da yarinta.
Duk da alokacin Zainabu zata girmema Hadiza ita Allah ya bata Haihuwan da Wuri tana da kananun Shekarunta Ammh sun zama kawaye tunda Zainabu batasan kowa agarin ba sai suka zama kamar yan"'uwa koda yaushe suna ziyatar juna Sannan Sa"idu duk karshen Sati wajensu yake yi kaunar yaron ta fara ne tun Tuni Sannan Shi kauna Allah ke hadashi ma Mutum ba.
Akwai Ranar da Malam Yunusa suna mgana da Aminu ya kallesa yana Fadin"Aminu ina kaunar Sa"idu ina jinsa kamar dan cikina..Ina ji kamar ya zauna Dani har Abada..!
Alokacin Aminu Dariya yayi ya Dafa Kafadar Malam Yunusa yana Fadin"Haba yunusa ai ni da kai mun Zama Daya..Wlh har araina na yarda da wannan kaunar Dake Tsakaninka da Sa'idu Dama Hadiza nada juna Biyu sai ta Haifa mana wani kai kuma ku rike Sa"idu kai da Zainabu har abada na tabbata ko bayan Raina Sa"idu zai fi Alheri Dakai Fiye Dani..!
Wata mganace da Malam Yunusa ya Dauketa kamar Fadice sai dai ba Haka bane Har azuciyan Aminu haka take Malam Yunusa bai Tabbatar ba sai da Aminu ya Tara Duka yan"uwansa ya Fadamusu ba wanda yayi gaddama Sanin Waye Malam Yunusa Shiyasa kowa yayi Na"am da Batun Hadiza ma bata kawo Damuwa ba macece mai kunya da kawaici Duk da kasancewarta Bazanfara gaba da baya.
Malam Yunusa yayi kukan Murna Aranar da Aminu da Hadiza suka Dauko Sa"idu da duka kayansa suka kawo musu shi Har abada shi da ZAINABU sun kasa Daina kuka suna ganin kamar mafarki ne sai dai Zahiri ne,Sa"idu bai damu ba ya Saki Jikinsa Sosai Saboda Dabbobi daman yafi son gidan Baba Malam kamar yadda Sa'idu shine Mutum na Farko Daya Fara Radamai wannan suna kuma yake binsa yana alfahari dashi.
Abu kamar wasa karamar mgana ta zama ba Sa"idu ya dawo hanun Malam Yunusa da matarsa zainabu abun Tsusayi Cikin Da Hadiza ta Samu ta Haifeshi ba rai ammh duk da Haka basu Damu Sa"idu ya cigaba da zuwa makarantar Boko sannan kuma Malam da Zainabu suna Karantar dashi karantun addini acikin Gida sannan suna iya bakin kokarinsu wajen Tarbiyansa da Rike Amanar da aka basu
Wajen sau uku Hadiza na Haihuwa ba rai sai ana Hudu ta Tsaya macece mai Suna Hafsah sunan Mahaifiyar Aminu ce suna cemata Husai sai kowa ya samu nashi Sa"idu na zuwa ganinsu Lokaci bayan Lokaci kamar yadda suma basa gajiya da Ziyartan Juna.
Tun alokacin ana ta yima Malam yunusa Tayin ya"ya Domin ya kara aure ko zai Samu Haihuwa sai yace A"a Domin Zainabu nada kima awajensa,Sannan koda an mai mganar Haihuwa sai yace Sa"idu ya isheni Rayuwar Duniya da Lahira Saboda irin kauna da Shakuwar Dake Tsakaninsu suna bashi Dukkan wani Gatan Duniya sai dai suna kokari wajen Kula da Tarbiyansa.
Cikin Ikon Allah kamar yadda Malan Yunusa yace Haihuwa ta Allah ce Hakan ce ta kasance Domin Sa"idu ko Shekara uku bai yi da Dawowa Hannunsu ba Zainabu ta samu Ciki kuma Haihuwarta na Farko Ta Haifi Namiji Malam Yunisa ya saka masa Suna UMAR IBN YUNUS..!
Koda zainabu ta Haihu mganarsa Dayane Sa"idu ne babban yaro na Domin kafin na Samu Umar Sa"idu na Haifa,Duk da Mutane sunsan ba Dansa bane ammh suna Girmama Kaunar dake Tsakaninsu kuma koda suka samu nasu babu abunda ya Sauya Daga soyayyar da sukemai.
Yayinda Aminu Daga Husai Hadiza bata kara ko barin wata ba kuma basu Damu ba Tunda Da ga Allah ne sun Tabbatar Sa"idu yayi Dace da iyaye nagari kuma ko bayan ransu Watarana sai yayi alfahari da hakan
Tundaga lokacin Haihuwa ta Budema Hajiya Babba Daga Umar tazo tayi Nazir wanda Tsakaninsu ba Nisa alokacin kuma Malam Yunusa ya kara aure Shima Bashi matar akayi sun je Da"awa garin Tsafe na Jahar Zamfara gidan Malamin da suka sauka Malam Hamza ya Dauki Yarsa Kwara Daya cikin jerin ya"yansa Uwani ya bama Yunusa shi kuma bazai iya Bijiremasa ba ya karba Hannu Bibbiyu achan aka Daura aure sai dai ya Dawo da mata kawai Sannan bai samu matsala da Zainabu ba ta karbi Uwani Hannu Bibbiyi suka cigaba da zaman Amana ko ita sai Daga baya tasan ba Malam ya Haifi Sa"idu ba shima sai da ya Fadamata ta yarda ammh tana Girmama wannan kaunar Daga Malam din har Zainabun da ya"yanta basu da Mganata sai ta Sa"idu ko"ina kaje agidan nan Sa"idu ne wannan kaunar Daga Allah ne.
Haka Rayuwa ta cigaba da gangarawa da Dadi ba Dadi Malam na Cigaba da nenan sani da Da"awa sannan Lokaci Daya yana karantar matasa Abunda ya sani na Addini Alokacin Aminu gusai akayi Chanjin gwannati bai samu Kakin majalisa ba sai aka Nada wani Daga Shekarar kuma Jinya ta kamasa na Ciwon kafa Daga Sama Sama sai abu ya Zarce baya iya tashi Sai dai a kwantar atayar Jinya tayi Jinya anyi mganin Asibiti anyi na gargajiyam Duka ba"a Dace ba Sai da Duka Abunda Alhaji Aminu ya Tara ya kare Malam ma bai zauna ba Shima Duk in da yaji wani mgani zai amsomai Sai dai ita Kaddaran Allah Daman Dayace komai Tsalle Tsallen bawa bai isa ya Gujemata ba, Aminu gusai ya Rasu Lokacin da Jinyarsa ta karar da komai ya Rasu ya bar Matarsa Hajiya Hadiza da Yarsa Husai da Sa'idu ko kafin Rasuwarsa ya kara Jadaddama Malam Sa'idu nasa ne har Abada wannan karamcin na Aminu Malam har ya koma ga Allah bazai manta ba.
Yaso ya Dauko Husai da Hajiya Hadiza ya Rikesu sai yan"uwan Aminu suke roko alfarman ya bar musu Rikonsu sai ya kyale musu Tunda karamcimsu garesa mai girma ne Gidan yayan Aminu Hajiya Hadizan ta koma da zama ita da Husai ba kyashi ba Hasaada riko na Tsakani ga Allah Sa"idu Lokacin yana makarantar kwana ta Hassan gwarzo Dake kano Aminu ya rasu sai da ya Dawo yaje yayima iyayensa gaisuwa Kowa bashi yake tsausayi ba Domim cewa ake Aminu yayi ma Sa"idu gata Domin Uba irin Malam abun Alfaharin kowani Cikakken D'a ne.
Tun Rasuwar Aminu Garin Gusai ya Fita kan Malam Yunusa batare da Shawara da kowa ba ya Fara Binciken yadda zai tashi Daga garin Dayake Tunamai da adalin Amini kamar Aminu,Ba Dadewa ya samu Cikakken bayani kan garin Gumel da yadda Suke da amfanin gona da Sauran Cigaba ba Dadewa ya mallaki Fili a wannan anguwan ta Zango ya Fara Gina iya adadin ida zasu zauna.
Sannan ya samar da Katon Fili Domim Kiwo yayi alkawarin Sa"idu sai ya zama wani abu sannan yana da Burin Cikamai wannan Burin nasa.
Dawowar Malam Yunusa garin Gumel baima Hajiya Hadiza Dadi ba Saboda ta Saba da Hajiya Babba sosai sannan Husai ta Saba da su Umar ammh bata da yarda zatayi tun anan din ma ba Wahala take ciki Yan"uwan Aminu ba suna Rike dasu tsakani ga Allah Duk da itama Duka na gida ne
Shekarun da suka Shude masu yawa ne sannan sun zo da Nasarori da Dadama da kuma akasinsu Sa"idu ya gama Secondary ya Fada Jami"ar garin Dutse yana karantar agric abunda ya Shafi noma da kiwo Ko alokacin Gidan gonar Baba Mallam Dake kusa dasu Sa"idu ke da Ahakin kula dasu Haka Allah ya yisa Zama Cikin Dabbobi sune ke sakashi Nishadi sannam Agarin ba wanda yasan Sa"idu ba yaron Malam bane Sannan kowa Dauka yake Shine Babba sannan su Umar Duka kannensa ne,Malam bai yi kasa a gwiwa ba anan din ma ya Cigaba da Karantar wa Ya Hakura da neman ilimi ya Zauma yana karantar da Duka Dalibin Dayazo wajensa neman ilimi Sannan bai da ina zuwa Da"awa ba duk inda za"a je dashi ake zuwa.
Zuwa Lokacin Malam ya Kara auran yar nan garin Jigawa ce Hajiya Nasara ita yar Masu kudi ce sannan zuwa Lokacin Gidan Malam ya fara Cika da Ya"ya kamar yadda yake fata sannan bai manta da Hajiya Hadiza da Husai ba da Lokaci bayan Lokaci suna zuwa suma suna zuwa sannan babu abunda suka nema suka rasa na bangaran Rayuwa.
*******
*Bayan shekaru Talatin..*