← Book details Ta Fita Zakka Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 14 OF 193

Sashe 14

Ta Fita Zakka Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read

A Gidan Baba Sa"idu ma akwai Mata guda Biyu Hadiza da yara ke Kiranta Yaya sai Baralaba da yaran ke kiranta Mamanmu Saboda Gabadaya yaran danatan da ba natan ba Duka Dayane a wajenta itace komai nasu ita Yaya kamar yar kallo ce acikin Gidan
Yaya nada ya"ya bakwai ne Jafar ne Babba sai Jadwa sai Jaleela sai Jamela sai Jawahir sannan Amina sai Jawaad Dakin Mamanmu kuma ya"yanta biyar Zulfa ce Babba sai Fatima Zahra sai Zulahait sai Zeenatu sai karamarsu Hamida.
jadwa tana auran Yaron Goggo Husai kanwar Baba Sa"idu Dake chan Jordan tana chan itama sai  Jaleela Dake auran Abokin aikin Ya Nazir wanda Sun zo Tare ne ya ganta yayi ma Malam mgana Akayi Bincike aka gano na gari ne aka bashi Tana chan Lagos din da zama Duk da shi ma Dan Jahar kano ne.
Sai jamila Dake  Gombe Tana auran wani Contoroller ne ma"aikacin Costume ne,Sai Jawahir Data Tafi Gusai Tana auran yaron wan Baban Baba Sa"idu ita auran gida tayi tana chan gusai ba kasafai suke zuwa gida ba Malam ya hana sai da wani Dalili mai karfi.
Sai Zulfa itama tana Zaria Tana auren wani Lecture ne Awajenta ma su Nazeem suke zaune Tunda suna Cikin Jerin Gidajen malama ne na Abu zaria,sai Zahra Dake parthorcourt Tana auran wani Mai kwangilan Titin Sama ne sai Zulahait da wannan Lokacin ne za"a aurar da ita sai Zeena mai bi mata sai Hamida wanda Tsakaninta da Amina Wata Uku ne
Amina ce aka fara Haihuwa sannan Hamida,Rayuwar Gidan Baba Sa"idu Kamar Rayuwar gidan Baba Malam ce Domin komai Tare suke Gudanarwa sannan Gabadaya Doka da Tarbiyan Lokaci Daya take aiki bama Haka ba Baba Sa"idu Tarbiyan Malam ne ko shi baya Tsallake mganarsa Ballatana Iyalansa.
baza'ace Duka gidajen yaran basa Samun Sakewa ba A"a sai dai ba irin Sakewar nan ta ya"yan da suka Samu gata mai yawa ba suna cikim jerin ya"ya masu samun komai na Rayuwa cima mai kyau Sutura mai kyau komai Tare Baba Malam ke gudanarwa ba Nuna bambamci Gabadaya makaranta Daya suke yi manyansu da yaransu in Sallah Tayi kaya iri Dayame kuma Duka Mallam zai bada Umarnin Asiya Baka Taba Nuna wani bambamci Tsakanin ya"yan Gidansa dana Baba Sa"idu.
Suna Samun ilimi sosai Da Tarbiya Mata basa Rike waya sai agidan mijinki Wani Daga cikin su tun kan su Jadwa ba wacce tataba Tsayawa da wani Namiji a waje Da sunan Zence sai wanda zaki aura zaku gana afalon Baba Malam ko Falon Baba Sa"idu ba inda suke zuwa Daga makaranta Sai gida shima mota ce kai kaisu ta Dawo dasu basa ma Fita Ballatana Har wani ya Taresu su Rayuwarsu tana cikin Gida ne sannan Gidan Baba Malam da Baba Sa"idu ba"a Kallo basu ma da kayan kallo Saboda gidan Mahaddata ne ba"a Saka Musu abunda Zai Dauke musu Hankali.
Sannan akwai girmamana na gaba Dakai ba Rashin kunya Yaro ko kwana Daya ya baka Dole ka Kirasa Yaya kuma ka Girmamasa Dole kuma in yayi maka Hukunci ka karbeshi Haka suka Taso Tundaga Tushen manyansu har kawo yanzu suna girmama juna da ganin Darajan juna.
Ba"a taba Haihuwar Mara kunya Mara jin mgana irin Amina ba,Tunda aka Haifeta tazo Duniya ba wanda ya Huta da Fitinarta da Jidalinta ita Kadai ta Fara Rashin kunya da kin girmama na gaba da ita tun Tana karama sannan ita kadai ta fara yin abu gaban Kanta Amina ba irin Sauran yara bane Duk wannan Hallayar nata yarinya ce mai Shiga Rai Aba yana Matukar Kaunarta Ballatana Datake bala'in kama da Yaya Hadiza sanda sukayi aure ba sonta yake yi ba ammh Hakurinta Sadaukarwanta Nasabanta Kirkinta yasa Ta samu Matsayi mai girma acikin Ransa tana da Kimar da Har Abada wata mace bazata kamota aransa ba.
Ba shi kadai ba ya zamo Hatta Baba Malam yana Kaunar Amina Saboda Baba Sa"idu yayi mai kara ya saka sunan Mahaifiyarsa yasa tun Amina na karamarta ta fara Bude ido da Kaunar Baba Malam gareta Har girmanta kuma wannan Kaunar shi yajamata Bakin jini wajen Ya"yan Anty Amarya da suke ganin Baba Malam na Fifita Amina akan Ya"yansa
Tun Tasowarta tare sukayi wasan kasa da Hanne da Hamida da kuma Sa"adatu daman Tun alokacin ba",a Shiri kafin agama wasa ayi Dambe fin sau Biyar wannan Kiyayyar tasu ba ta yau bane Ta Dade a zukatan junansu Sannan Kaunar Junansu Tsakanin Hamida da Hanne Daga Allah ne Duk kuwa da Amina ta fisu Baudewar Hali Ammh suna Tare da ita kowani Jidali ta Debe suna Daukansa ya koma kansa..
In nace Amina ta gagari kowa Zaku yarda..?duka ko Fada baya mata komai Domin in duka nasa yaro ya Natsu da ba haka ba sai dai bata Jin ko Daya ba wanda ya isa ya hanata abunda tayi niyya Duka baya Damunta Domin ya Zame mata Jiki Aba tun baya Damuwa da Lamarinta Har ya fara yana Tunanin kada watarana Ta fita zakkan da zata sakamai wani Cutar da zai kaisa kasa ganin Tun tana da kananun Shekarun Idanuwanta a Tsaye suke basu da Ladabi ballatana su Rankwafa.
Goggo Husai taso ya bata Amina Tatafi Da ita Saboda Duka ya"yanta Manya maza ne macenta Dayane kuma Tayi aure Baba Sa"idu ya Hanata Saboda yana Tunanin anan ma Amina ya aka kaya ballatana taje Cikin Jajayen Fata hakanan yaji gwara Tana gabansu da wata uwa Duniya Malam ma bai amince ba yace Amina zata Sauya Har yau har gobe yana ganin yarinta ne ke Damunta.
Baba Malam bai manta da gida ba Yana Zuwa bazanga kaima yan"uwansa da suke Rage ziyara suma suna zuwa sannan Duk Shekara achan yake Fidda Zakka Sannan Har alokacin ana Nomamai Gonakinsa Daya gada wajen Mahaifinaa sannan bai daina yawon Da"awa ba yana cikin Malaman Kungiyar Sunna alokacin ba garin da basa zuwa Da"awa ko kuma wani Taimako in wani abu ya taso bai da matsala Baba Sa"idu na kan komai zai kuma Kula da komai kamar yadda ya Sani.
Hajiya Babba itace Uwa bada Mama ga Baba Sa"idu ko ya"yanta sun sani in Abu ya Shafi. Baba Sa"idu Hajiya bata Zaune bata Tsaye gabadaya ya"yansa matsayin kaka suke kallonta Tasha Fadi Sa'idu babban yaro na ne Balle da bata Kiran sunan Umar sai dai tacemai D'an mallan sunan Daya bisa Har yau bamai kiran sunansa sai Yaya D'an Malam in ya nuna jin Haushinsa sai tayi Dariya Har ce mata ya Taba yi Hajiya meyasa ni bakya Kiran sunana..?ammh kuma kina Kiran sunan Baba Sa"idu..!
Dariya take alokacin sai tace"Sa"idu babban yaro na ne..Dashi na Fara sanin Soyayya ya"ya Shiyasa bana masa alkunya..!
Tabbas bata masa alkunya Wani mtsalan nasa Baba Mallam saidai yaji sa bakin Hajiya akwai Fahimtar juna da Shakuwa Tsakaninsu hakama Hajiyar ko wani abu ne saita Dauki Waya ta Kirasa Sa"idu in ka dawo kazo ina nemanka..Ko ya"yanta basu isa su san Tsakanin Hajiya da Baba Sa"idu ba,ita din Uwace garesa bada Mama ko Baba Mallam wani Lokacin sai yace suna mai Wariya da yan Ubanci fa Shi Kanshi yasani Haihuwan Sa"idu ne kadai basu yi ba ammh Suna mai kauna irin wacce ko ya"yan Cikinsu basu yimawa.
Shi kanshi Baba Sa"idu haka yake jinsu Ammh Duk da Haka baai yada Danginsa na Gusai ba suna zuwa shima yana zuwa ballatana Har gaban Abada bazasu Daina Labarin kima da Dattakon Baba Malam ba..!
Koda Yaushe suka zo ko Sa"idu yazo Sai sun Fadamai ya yi ma Baba Malam Biyayyah Shi din Uba ne Cikin Dubu sai antona Gaskiya suka Fada In yana Kallon Alkhairan Baba Mallam zuwa garesa sai yaga yafi kowani Da Sa"an Uba awannan Duniya Soyayyar da ko su Umar basu Sameta ba Sa"idu Shi kadai ne Mallam bai Taba Hadasa da wani ba kowa ya san da wannan ba ga ya"yan nasa ba har ga Matan nashi.

Wannan kenan ..!
Chapter 14 · 0% Book details