Sashe 81
Ta Fita Zakka Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Baba maallam na gaban Makeken Dorowansa na Littafai Dake falonsa Sanye yake da Jallabiya Mai ruwan zuma kansa ba Hula fufuransa ta bayyana sai Farin gilashinn da ke karamai karfin gani Falon akwai hasken Wutan gen ko"ina tar,kansa na chan kasa yana so ya Dauko wani Littafi Anty Amarya ta shigo Falon cikin kwalliyarta Ita ke da Shashen ayau din dazu ta iso taga yana Tare da su ya jafar da su Aba sai ta koma sai da Tara ta wuce goma saura sannan ta Dawo domin ta tabbatar da zuwa Lokacin Mallam din shi kadai ne..!
Har ta kariso bayansa bai sani ba sai da ya Dauko Littafin ya Juyo sannan yaci karo da ita bai nuna Razana ba illah kallonta da yayi yana Fadin"Da girmanki marliya sai ki shigo ba sallama..?
Ido ta Juyamai Kafin tace"Nayi baka ji bane..ina nan na Tsaya ina karema Mijina kallo sai yanzu na Lura ashe ashe Mallam ya Tsufa bansani ba..!
Ta karishe fada cikin yar Dariya Shima Dariyan yayi kafin ya wuce gaba tabiyosa abaya cikin Sanyinsa yace"Sanda aka bani auranki Farin gashi bai gama cika kaina ba marliya..Kuma ahaka kika gani kikace kina sona ko ba haka ba..?
Ya fada yana zama kan Daya cikin kujerun falon mai zaman Mutum Daya tana Dariya ta zauna ahannun kujeran tana fadin"Ah..Ni yaushe nace ina sonka..?Kuma ka rufeni da rawaninka bansan haka farin gashi ya Cika kanka ba..!
Tafada tana jan gashin nasa yar Dariya yayi kafin yace"Ai lokacin bai kai haka cika ba..Bayan na aureki ne kika Ida Tsufar dani Marliya..!
Yafada yana kallomta Baki ta Rike tana Dariya tace"Mallam!.
Saurin tareta yayi da fadin"Dole na fadi haka..Naga yau Amaryan tawa Gori take ji da tsokana..!
Dariya take yi tana fadin"Kodai ka Tsufar dani mallam?
Mirmishi ya saki kafin yace"Ko nan da shekara ashirin muka kara tare..Mallam dinki zai cigaba da kallon yarintarki Marliya..!
Sai kanta ya fashe ta fara Mirmishi Ta sani duk cikin matansa tafi kowaccensu Kuruciya kuma Tsakani ga Allah sai kana da kuruciya ake Damawa Dakai.
Bata samu zarafin mgana ba wayarsa Dake saman Center table din Dake falon ta Dauki Kidan Larabawa Gabadaya hankalinsu ya koma kan inda wayar take cikin Daidaita Natsuwarsa yace"Hanzarta mikomin kada ta katse..!
Da azama tatashi ta Daukomai sai dai ganin sunan mai kiran yasa nan da nan Ranta ya baci ABU NA..!
Hajiya ce wannan Keda sunan tun auranta da Maallam ta sanshi dashi abu na kamar wani yaro mtseewa tsaki taja acikin Ranta kafin ta mikamai wayar yana Fadin"wake kirana..?
Sai da ta koma Kujeran dake gefensa kafin tace"Ina ga Hajiya ce..!
Tafada tana Daidaita yanayinta Abu Daya ke batamata rai sufa da sunayensu yayi Saving a wayarsa ammh ita Hajiya kai Tsaye yake nuna ita din ta Dambace komai zai yi kafin ya aiwatar dashi ita da Sa"idu sai sun fara Tabbatar dashi sannan..!
Tana jinsa Daya karbi wayar yana Fadin"Hajiyar ce ma ba musu ba..!
Kiran ya katse sai yabi bayan kiran tana jin sandda Hajiyar ta Dauka da Sallama ya amsa yana Fadin"Hajiya..!
Bata ji me tace ba sai dai taji yace"Kizo shashena ki sameni daman nima ina son mgana Dake..!
Daga haka bata san me tace ba yace yana Jiranta ta katse kiran
Sai da ya gama sannan ya Dago yana kallon Anty Amarya kafin yace"Amarya..Amarya..!
Dan juya ido tayi kafin ta dan Tura baki na Shagwaba Mirmishi yayi kafin yace"Yanzu dai kimin hakuri adana duk wannan amarcin naki zuwa anjuma..Ina so na gana da Hajiya na minti talatin in ba Damuwa..!
Yake tayi kafin ta mike cikim basarwa tace"ba damuwa..in kun gama sai ka Taboni..!
Cikin jin Dadi yace"Shikenan Allah yayi miki albarka..!
Aciki ta amsa ta fice tana kunkuni ahanya suka Hadu da Hajiya tasha Lullubinta suka gaisa ta wuce Anty Amarya ta bita da kallo tana Fadin"Tsofai tsofai dake bazaki hakura da miji kibar ma yara irin mu ba Mtsewww Jaraba..!
Take fada har ta fada shashenta Hajiya batama san tanayi ba Falon Mallam ta karisa sukayi mgana kan Kayan garan Amaran ne da Tsarin da za"a cire musu sai abincin Bikin da na yan Daurin auran,Baba Mallam yace su bar abincin Daurin aure Mallam Hamza ya Dauki nauyin mutane bayan Daurin aure zasu je suyi Reception abincin gara kuma yace a Diba kamar yadda tsarin yake..!
Bayan sun gama mganar Hajiya ta mike zata tafi tunda ba ita keda Mallam din ba shi ya Tsaidata da Fadin"Zainabu kunyi mgana da Da'nki kuwa..?
Tana Daga Tsayen tace"Sa'idu..?
Yar dariyq yayi kafin yace"Sa"idu..Sa"idu..Ke da Sa"idu bansan wanda yafi wani kaunar wani ba..Nan fa muke mgana dashi gani ni Ubansa ammh sai ya tsallakeni komai nace sai yace Mallam kuyi mgana da Hajiya yadda tace haka zaa"ayi..Anya Zainabu baki kwacemin Sa"idu ba..!
Hajiya na Dariya tace"Ni ban kwacesa ba..Ammh ai kowa yasan Sa"idu na Zainabu ne..Kayi hakuri dai da aron da nake baka..!
Mallam yace"Ai na ma gode..Tunda ana bani aronsa!
Dukkansu dariya sukayi kafin tace"Nazir kake mgana..?Mun yi mgana dashi dazu yace sai Ranar Daurin aure zai zo..matarsa kuma yace saboda aiki yara kuma ga makaranta..!
Baba Mallam yace"Bama shi ba..Ai shi nasam zan samu labarinsa awajenki..Umaru fa nake mgana..!
Hajiya ta tabe baki tace"Sai kace min Danka. kanin Sa"idu sai nafi ganewa..!
Mirmishi yayi kafin yace"Zauna muyi mgana nasan kema bai kiraki ba..!
Hajiya ta zauna gefen Mallam tace"Jiya ya Kirani mun gaisa Daganan bai ce min komai ba badai wata matsala bane ko..?
Mallam ya Sauke Numfashi kafin yace"To matsala ne kan matansa..!
Hajiya tace"Topha me ya faru..?
Mallam yace"To ni ma bansan Farkon abun ba..Yadda dai Abu kattab ya Kirani ya fadamin kan zuwa wannan Sha"anin ne..!
Hajiya cikin mamaki tace"Daman ba Danmallam din ya kiraka ya Fadamin ba..?
Mallam yace"Kema kinsan bazai Fadamin ba..Sa"idu ya Kira sukayi mgana nima yanzu bayan fitansu Abu kattab din ya Kirani mukayi mgana..Kan zuwa Sha"anin nan ne yace yaso yazo shi kadai saboda zirga zirga da kashe kudi kuma ko wata biyar basu yi da komawa ba,gashi ba wasu kudi a hannunsa sai yace zai taho shi kadai sai Sakina tace zata zo ita zata Biya ma kanta kudin jirgi,To bayan haka ita Saratun daman yace tayi hakuri ta zauna har su dawo ga karatunta tunda tana hada Degree dinta anan Jami"ar musulunci to bai kuma sani ba ko Sakinar ce ta Zugata har ta amimce sai ta fara mai boren itama sai ta taho shine yace duka su hakura bazai zo da ko daya ba Sukayi ta Hayaniya yayi musu yaji yaje ya kwana acikin makaranta shine ita Saratun taje ta Fadama Abu Kattab din shi kuma ya Nemo Umaru yayi musu Sulhu ya kuma bama Umaru Umarni Daya Taho da Sakina Ita kuma Saratun ta zauna ta jirasa har su dawo Tunda tataba zuwa kinji Abunda ya Faru..Kuma dazu fa mun yi mgana dashi bai ce min komai ba yadai cemin zai taso gobe zai kwana ajidda Daga jidda zai shigo Jirgi zuwa Kano..!
Hajiya tace"Allah ya kyauta..!
Mallam yace"Amin fa.bana so Kattab yaga kamar na nuna Umaru dana ne..Da sai nace itama Sakina ta zauna ban ga abunda zata zo yi ba..!
Hajiya tace"Barta tazo ba ruwanka..Inkana da iko da Mijinta ita fa..?
Cikin Dattakonsa yace"Ko bata tashi agidana ba..Kamar ya"yana Haka na Dauki matan ya"yana Saboda haka na isa da su gabadayansu ballatana ahannuna tatashi na kuma aurama Umaru ita..!
Hajiya ta mike tana Fadin"Gwara da baka ce ba..Allah ya sauke su lafiya..!
Ya amsa da Ameen daganan sukayi sallama ta fice ya bita da kallo bai tana ganin mace mai kawaici da kauda kai iron Hajiya ba to sai marigayiya matar Sa"idu su kan suna da kauda kai kan abunda suka Haifa yasan Hajiya bata taba saka baki kan Umaru da sakina ba,ko abaya ballatana yanzu..!
Anty Amarya ya Kira yace ta shigo Ya sallami Hajiya ba jimawa sai gata ta Dawo ta kara sabunta kwalliyanta yayi ta kallonta yana yaba mata kanta nakara Fashewa.!
*****
Har ta kariso bayansa bai sani ba sai da ya Dauko Littafin ya Juyo sannan yaci karo da ita bai nuna Razana ba illah kallonta da yayi yana Fadin"Da girmanki marliya sai ki shigo ba sallama..?
Ido ta Juyamai Kafin tace"Nayi baka ji bane..ina nan na Tsaya ina karema Mijina kallo sai yanzu na Lura ashe ashe Mallam ya Tsufa bansani ba..!
Ta karishe fada cikin yar Dariya Shima Dariyan yayi kafin ya wuce gaba tabiyosa abaya cikin Sanyinsa yace"Sanda aka bani auranki Farin gashi bai gama cika kaina ba marliya..Kuma ahaka kika gani kikace kina sona ko ba haka ba..?
Ya fada yana zama kan Daya cikin kujerun falon mai zaman Mutum Daya tana Dariya ta zauna ahannun kujeran tana fadin"Ah..Ni yaushe nace ina sonka..?Kuma ka rufeni da rawaninka bansan haka farin gashi ya Cika kanka ba..!
Tafada tana jan gashin nasa yar Dariya yayi kafin yace"Ai lokacin bai kai haka cika ba..Bayan na aureki ne kika Ida Tsufar dani Marliya..!
Yafada yana kallomta Baki ta Rike tana Dariya tace"Mallam!.
Saurin tareta yayi da fadin"Dole na fadi haka..Naga yau Amaryan tawa Gori take ji da tsokana..!
Dariya take yi tana fadin"Kodai ka Tsufar dani mallam?
Mirmishi ya saki kafin yace"Ko nan da shekara ashirin muka kara tare..Mallam dinki zai cigaba da kallon yarintarki Marliya..!
Sai kanta ya fashe ta fara Mirmishi Ta sani duk cikin matansa tafi kowaccensu Kuruciya kuma Tsakani ga Allah sai kana da kuruciya ake Damawa Dakai.
Bata samu zarafin mgana ba wayarsa Dake saman Center table din Dake falon ta Dauki Kidan Larabawa Gabadaya hankalinsu ya koma kan inda wayar take cikin Daidaita Natsuwarsa yace"Hanzarta mikomin kada ta katse..!
Da azama tatashi ta Daukomai sai dai ganin sunan mai kiran yasa nan da nan Ranta ya baci ABU NA..!
Hajiya ce wannan Keda sunan tun auranta da Maallam ta sanshi dashi abu na kamar wani yaro mtseewa tsaki taja acikin Ranta kafin ta mikamai wayar yana Fadin"wake kirana..?
Sai da ta koma Kujeran dake gefensa kafin tace"Ina ga Hajiya ce..!
Tafada tana Daidaita yanayinta Abu Daya ke batamata rai sufa da sunayensu yayi Saving a wayarsa ammh ita Hajiya kai Tsaye yake nuna ita din ta Dambace komai zai yi kafin ya aiwatar dashi ita da Sa"idu sai sun fara Tabbatar dashi sannan..!
Tana jinsa Daya karbi wayar yana Fadin"Hajiyar ce ma ba musu ba..!
Kiran ya katse sai yabi bayan kiran tana jin sandda Hajiyar ta Dauka da Sallama ya amsa yana Fadin"Hajiya..!
Bata ji me tace ba sai dai taji yace"Kizo shashena ki sameni daman nima ina son mgana Dake..!
Daga haka bata san me tace ba yace yana Jiranta ta katse kiran
Sai da ya gama sannan ya Dago yana kallon Anty Amarya kafin yace"Amarya..Amarya..!
Dan juya ido tayi kafin ta dan Tura baki na Shagwaba Mirmishi yayi kafin yace"Yanzu dai kimin hakuri adana duk wannan amarcin naki zuwa anjuma..Ina so na gana da Hajiya na minti talatin in ba Damuwa..!
Yake tayi kafin ta mike cikim basarwa tace"ba damuwa..in kun gama sai ka Taboni..!
Cikin jin Dadi yace"Shikenan Allah yayi miki albarka..!
Aciki ta amsa ta fice tana kunkuni ahanya suka Hadu da Hajiya tasha Lullubinta suka gaisa ta wuce Anty Amarya ta bita da kallo tana Fadin"Tsofai tsofai dake bazaki hakura da miji kibar ma yara irin mu ba Mtsewww Jaraba..!
Take fada har ta fada shashenta Hajiya batama san tanayi ba Falon Mallam ta karisa sukayi mgana kan Kayan garan Amaran ne da Tsarin da za"a cire musu sai abincin Bikin da na yan Daurin auran,Baba Mallam yace su bar abincin Daurin aure Mallam Hamza ya Dauki nauyin mutane bayan Daurin aure zasu je suyi Reception abincin gara kuma yace a Diba kamar yadda tsarin yake..!
Bayan sun gama mganar Hajiya ta mike zata tafi tunda ba ita keda Mallam din ba shi ya Tsaidata da Fadin"Zainabu kunyi mgana da Da'nki kuwa..?
Tana Daga Tsayen tace"Sa'idu..?
Yar dariyq yayi kafin yace"Sa"idu..Sa"idu..Ke da Sa"idu bansan wanda yafi wani kaunar wani ba..Nan fa muke mgana dashi gani ni Ubansa ammh sai ya tsallakeni komai nace sai yace Mallam kuyi mgana da Hajiya yadda tace haka zaa"ayi..Anya Zainabu baki kwacemin Sa"idu ba..!
Hajiya na Dariya tace"Ni ban kwacesa ba..Ammh ai kowa yasan Sa"idu na Zainabu ne..Kayi hakuri dai da aron da nake baka..!
Mallam yace"Ai na ma gode..Tunda ana bani aronsa!
Dukkansu dariya sukayi kafin tace"Nazir kake mgana..?Mun yi mgana dashi dazu yace sai Ranar Daurin aure zai zo..matarsa kuma yace saboda aiki yara kuma ga makaranta..!
Baba Mallam yace"Bama shi ba..Ai shi nasam zan samu labarinsa awajenki..Umaru fa nake mgana..!
Hajiya ta tabe baki tace"Sai kace min Danka. kanin Sa"idu sai nafi ganewa..!
Mirmishi yayi kafin yace"Zauna muyi mgana nasan kema bai kiraki ba..!
Hajiya ta zauna gefen Mallam tace"Jiya ya Kirani mun gaisa Daganan bai ce min komai ba badai wata matsala bane ko..?
Mallam ya Sauke Numfashi kafin yace"To matsala ne kan matansa..!
Hajiya tace"Topha me ya faru..?
Mallam yace"To ni ma bansan Farkon abun ba..Yadda dai Abu kattab ya Kirani ya fadamin kan zuwa wannan Sha"anin ne..!
Hajiya cikin mamaki tace"Daman ba Danmallam din ya kiraka ya Fadamin ba..?
Mallam yace"Kema kinsan bazai Fadamin ba..Sa"idu ya Kira sukayi mgana nima yanzu bayan fitansu Abu kattab din ya Kirani mukayi mgana..Kan zuwa Sha"anin nan ne yace yaso yazo shi kadai saboda zirga zirga da kashe kudi kuma ko wata biyar basu yi da komawa ba,gashi ba wasu kudi a hannunsa sai yace zai taho shi kadai sai Sakina tace zata zo ita zata Biya ma kanta kudin jirgi,To bayan haka ita Saratun daman yace tayi hakuri ta zauna har su dawo ga karatunta tunda tana hada Degree dinta anan Jami"ar musulunci to bai kuma sani ba ko Sakinar ce ta Zugata har ta amimce sai ta fara mai boren itama sai ta taho shine yace duka su hakura bazai zo da ko daya ba Sukayi ta Hayaniya yayi musu yaji yaje ya kwana acikin makaranta shine ita Saratun taje ta Fadama Abu Kattab din shi kuma ya Nemo Umaru yayi musu Sulhu ya kuma bama Umaru Umarni Daya Taho da Sakina Ita kuma Saratun ta zauna ta jirasa har su dawo Tunda tataba zuwa kinji Abunda ya Faru..Kuma dazu fa mun yi mgana dashi bai ce min komai ba yadai cemin zai taso gobe zai kwana ajidda Daga jidda zai shigo Jirgi zuwa Kano..!
Hajiya tace"Allah ya kyauta..!
Mallam yace"Amin fa.bana so Kattab yaga kamar na nuna Umaru dana ne..Da sai nace itama Sakina ta zauna ban ga abunda zata zo yi ba..!
Hajiya tace"Barta tazo ba ruwanka..Inkana da iko da Mijinta ita fa..?
Cikin Dattakonsa yace"Ko bata tashi agidana ba..Kamar ya"yana Haka na Dauki matan ya"yana Saboda haka na isa da su gabadayansu ballatana ahannuna tatashi na kuma aurama Umaru ita..!
Hajiya ta mike tana Fadin"Gwara da baka ce ba..Allah ya sauke su lafiya..!
Ya amsa da Ameen daganan sukayi sallama ta fice ya bita da kallo bai tana ganin mace mai kawaici da kauda kai iron Hajiya ba to sai marigayiya matar Sa"idu su kan suna da kauda kai kan abunda suka Haifa yasan Hajiya bata taba saka baki kan Umaru da sakina ba,ko abaya ballatana yanzu..!
Anty Amarya ya Kira yace ta shigo Ya sallami Hajiya ba jimawa sai gata ta Dawo ta kara sabunta kwalliyanta yayi ta kallonta yana yaba mata kanta nakara Fashewa.!
*****