Sashe 97
Hayateem Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Baya Asim yayi cikin kasa yadda da abinda yake ji ya juyar da idanuwansa akan hailen da wani irin sauri muryansa na rawa yayi kanta ya saka hannuwansa duka biyu ya kamata yana kallan cikin idanuwanta da dukkanin imaninsa akan bazata iya aikata hakan ga sultan ba ya bude baki muryansa na rawa yace
'Mami ki fada abinda ya faru wanda ba abinda Kadir yake fada ba,
Ki fada mana meya faru?
Waye yayiwa sultan hakan?
Waye yayi wannan mummunan aikin?
Ki fada ba kece ba Mami...
Dagowa tayi ta kallesa da idanuwanta da sukai jajir itama suna taruwa da wasu hawaye masu zafin gaske ta bude baki tace
'Asim nice nayi sbd zuciyata bazata iya daukan ya zabi wata baiwa akaina ba.......
Sai a lokacin NUAB ya dago kansa cikin wani irin slow ya juyo yana sauke idanuwansa masu kaifi akanta a karan farko daya ke sanin asalin kamanninta da baima saniba,
Dagowa da juyowansa ya saka kowa tsayawa kallansa banda ita data riqe Asim dake neman sarewa qasa sbd abinda ta fada jikinta na rawa muryanta na rawa dukkanin haukacewanta na bayyana idanuwanta na rufewa kaman yanda zuciyarta ta rufe ta qanqame hannuwansa tana cewa
'Asim shine yayi sanadin halin dayake ciki,
Shine ya zabeta akaina,
Shine ya zabi 'danta akan nawa dan,
Shine ya zabi binta qasarta yabar qasarsa da ni da yayana,
Shine yace yana sonta,
Ita yake tsananin so ba ni ba,
Sbd ita ya sauka mulki sbd ita a yanzu komai na rayuwarsa yake tafiya,
Na tambayesa yace Allah ne ya saka masa hakan dan haka bazan iyaba na zabi mutuwa tareda shi sbd nasan nima mutuwar zanyi gwara na fara turasa.....
Miqewa tsaye NUAB yayi sbd yanda kalamanta ke jijjiga kwakwalwansa suna tsinka jijiyoyin jikinsa.
Yana miqewa Aleey ya saka kiran keelah a wayarsa ya bada umarnin a kai securities bangaren queen haile ba ba wanda zai sake fita daga bangaren har yayanta.
NUAB kallo daya yayi mata da idanuwansa bayan ya miqe ya dauke idanuwansa sbd abinda yakeji zai iya fasa kanta da hannunsa a gurin take dan haka juyawa yayi yana fuskantar kofar dakin da sultan yake yana kasa cewa komai tukuna.
Kadir ma baqin ciki da tashin hankalin abinda take fada sakawa yayi ya rasa abin fada ya juya baya yana dafe goshinsa da hannuwansa tareda rintse idanuwansa.
Asim kuwa da yayi mutuwan tsaye sbd tashin hankali sakinta yayi yana ja da baya ahankali tareda rintse idanuwansa hannuwansa na wata irin rawa,
Kafin ya iya dawowa daidai daga tashin hankalin daya shiga NUAB ya bude baki batareda ya juyo ba yacewa aleey akaita bangarenta a rufeta a cikinsa ya sallami duka bayin dake bangaren da duk wani me rai dayake ciki ita kadai zaa bari a rufe bangaren ba shiga ba fita tukuna.
Asim na jin hakan wasu hawaye masu tsananin zafin gaske suka gangaro masa ya rintse ido ya bude yana tabbatarda Allah ne kadai a yanxu zai fidda mamin daga wannan kaddara data jawa kanta me muni.
Aleey da daman jiran umarnin yake wayarsa ya daga zai saka kiran wainda zasu shigo su tafi da ita Asim kallansa yayi cikin wani irin mutuwan jiki yace ya bari zai kaita da kansa.
Hakan daya fada ya saka kadir kallansa hakama aleey din.
NUAB kuwa buqatan a fice da itan yake ba bata lokaci dan shaqar numfashin tsayuwanta agurin kadai toshe kirjinsa yakeyi yana neman saka masa kasa iya riqe kansa gurin mata illa.
Asim hannu ya miqa ya kama hannunta yayi gaba da ita tafara tirjewa tana kokarin kwacewa da karfi tana ihun ambatar bazata tafi koina ba sai likitocin sun fito sun sanar da mutuwar sultan.
Yanda take maimaita kalman da karfi tana kwacewa tana tirjewa Asim yana janta ya saka kadi binta a bayan yana turata cikin zafin zuciya da baqin ciki hakama aleey yana bayansu dan tabbatarda ta isa inda akace a kaita din.
Kuka takeyi sosai tana ihun fadan jiran labarin mutuwan sultan din sbd mutuwan ce ta dace dashi,
Mutuwansa ce zata saka ayanah ghaz a cikin baqin cikin datake son ganinta.
Tsit koina yayi ihun maganganunta ne kadai suke amsawa koina tana fada da karfin gaske dan NUAB yaji shima baqin cikin datake ji ya kashesa.
Asim kuwa hawaye yake fiddawa masu radadi da baqin ciki yana kasa sakin hannunta tana dukansa tana son kwacewa amma ya kasa sakinta haka ya nufi bangarenta da ita Aleey da securities da fadawa marasa imani suna biye dasu.
Tin kafin su iso su Aslam da aka fito dasu suka nufo hanyar cikin babban tashin hankalin da basu taba shigaba sbd jin abinda ya faru.
Cikin tashin hankali da tsoron gaske suka yo kanta tana ihu har lokacin tana jin idan bata ji zancen mutuwar sultan da kunnuwanta ba zata iya mutuwa sbd baqin ciki.
Kuka me karfin gaske dayake hade da mummunan tashin hankali Aslam ta fasa tana kokarin kama Mamin itama amma sam idan mutuwan sultan zaa fada mata ba batason komai.
Shigewa akai da ita bangaren har tsakiyar palonta Asim ya jijjigata da karfin gaske yana ambatar sunanta da karfin gaske yace
'Mami ki dawo hankalinki sbd Sultan bazai mutuba insha Allah,
Bazaki taba saka Ayanah baqin cikin da kikeson gani a tattare da itaba sbd ta dade da shiga kowane kalan baqin cikin rayuwa,
Babu sauran baqin cikin dazaizo mata a ayanzu da bata taba shigarsaba,
Zatai baqin ciki da radadin rasa Sultan idan ya rasu amma bazata mutu ba zata rayu kuma hankali zata dawo farin ciki sbd haka rayuwan take dan haka bazaki iya saka mata dawwamamman baqin ciki ba idan ba Allah daya halicceta ba,
Kin aikata babban kuskuren da daga lokacinda kika shayar da uban yayanki mijinki gubar mutuwa kika dasawa kanki baqin cikin da zaki dawwama cikinsa,
Meyasa zakiyi hakan mami?
Meyasa kika bari shedan ya rufe zuciyar dake kirjinki da idanuwanki?
Meyasa zaki saka mu a cikin wannan halin da babu abinda zamu iya miki dan cetanki?
Meyasa zaki sakamu a halinda zamu kalla hukunci ya hau kanki batareda munada ikon komaiba.
Kuka me karfin gaske ya zowa meryam itama jin kalamansa na karshe dan kuwa da gasken basuda abinda zasu iya yimata a matsayinsu na yayanta sbd Allah ya kwace dukkanin dama daga hannunsu,
Aslam kasa cewa komai tayi suka zuba dukansu qasa a gabanta suna fasa kuka suna rerowa mai tsananin shiga zuciya,
Daga mata da yayan dasuka fi kowace me rai dake boyem daraja yau sun zama mafi qasqancin rayuka a boyem sbd abinda Mamin tayi ayau zai shiga tarihin da har jikokin jikokinta zaa fada,
Zuriarta bazasu taba sake daraja ko ta qimar kallo ce daga yanzu har abada a tarihin boyem,
Jininta daga yanzu sun rasa daraja da martabarsu da jininsu sbd abinda tayi hatta matsayinsu duka zasu rasa a cikin masarautar da duniya gabaki daya.
Kukan da sukeyi mai tsananin karfi da tsima jikin kowannensu yana jijjiga ya sakata zamewa itama ta zube qasa tana fasa kukan tareda cusa kanta cikin kafafunta zuciyarta na mata wani irin tsananin zafi da ciwo da radadin da nauyin datake jin har numfashinta yana toshewa.
Shi kansa Asim din kuka yakeyi sosai mara sauti jikinsa na rawa yana jin inama baizo duniya a cikin jinin sarauta ba,
Inama ya fara zuwa bangaren Maminsa kafin ta fita tayi wannan aikin mummunan kaddarar,
Inama tin suna yara suka gane komai suka sauya rayuwar da zata amfanesu ba wannan ba.
Keelah ne da wasu securities suka shigo aka fitar da 'yayan nata suna kuka suna jin wani irin tashin hankali da mummunan tsoro da firgici sbd jin kaman bazasu sake haduwa ba da ita.
Ganin halinda suka shiga suna ficewa zasu barta ya sakata fasa kuka tana riqesu da hannuwanta dake rawa tana cewa kada su barta su tsaya da ita su kadai gareta a yanxu.
Yanda ta rikice tana kuka jikinta na rawa ya sakasu sake shiga mummunan hali amma a haka akai karfin halin rabasu aka fice dasu aka barta tana wani irin jijjiga.
Rufe bangaren akai ba kowa a cikinsa bayan ita aka zagayesa da tsaro me karfin gaske.
Suma su Aslam bangare daya dole suka koma suka zauna cikin tsaka me wuyar tinanin kaddarar data samesu a dare daya.
Asim ma dole bangaren sultan ya koma ya zauna tareda NUAB daya kasa zama da samun kowace irin nutsuwa.
Tsit masarautar ta dauka dare ya sake tsalawa sosai komai ya tsaya musu cak,
Duk wani me matsayi a masarautar da manyan fada tsoffi da sabbi da duk wanda yakeda alaqa da jinin boyem din labarin mummunan lamarin ya isar musu kafin safe dan haka koda aka wayi gari da mummunan labarin aka tashi komai ya tsaya cak ana jiran farfadowansa wadda likitocin sun tabbatarda ba tabbas sunyi iya abinda zasuyi sai ajira hukuncin ubangiji kawai.
#MAMUH
09033181070
[15/01, 2:00 pm] Dasoo: HAYATEEM
Mamuhgee
171
Duk hanyar dasu Ammi zasu samu labarin abinda yake faruwa NUAB ya saka aleey ya toshe ta sbd sam anqi barin kowace kafar media ta fidda labarin hakama masarautar tin daga babbar gate din farko aka dakatar da kowace irin shiga da kowace irin fita komai ya tsaya a yanda yake sai an samu sanin halinda sultan zai kasance,
Babu wanda ya rintsa babu wanda ya matsa,
Sallar asuba ce kadai ta fiddasu amma suna bangaren sultan din sun kasa sun tsare suna jiran tsammani cikin zallar fargaba.
Guraren karfe goma sha daya da rabi Bahar ce ta fara kirasa sbd ganin bai kiraba lokacinda ya saba kira,
Bai bari ta fahimci komai ba sukai magana sama sama sbd itama bata jin dadi,
Suna gama wayar ba dadewa Amminsa ma ta kirasa jikinta a sanyaye sukai magana itama ta kashe tana kasa kiran sultan sbd batason shiga haqqin haile ko nasa hakama shi daya saba kira bai kira din ba dan haka ta hakura tana hana kanta kira dan basu lokacin daya kamata.
Shima Asim leylah ta kirasa ganin be kira dinba sukai magana ta kashe tana jin damuwa a ranta sbd shi kam bai iya dannewa da boye damuwansa kaman NUAB ba dan haka ta fahimci akwai damuwa tattare dashi ta tambaya kuma yace ba komai.
'Mami ki fada abinda ya faru wanda ba abinda Kadir yake fada ba,
Ki fada mana meya faru?
Waye yayiwa sultan hakan?
Waye yayi wannan mummunan aikin?
Ki fada ba kece ba Mami...
Dagowa tayi ta kallesa da idanuwanta da sukai jajir itama suna taruwa da wasu hawaye masu zafin gaske ta bude baki tace
'Asim nice nayi sbd zuciyata bazata iya daukan ya zabi wata baiwa akaina ba.......
Sai a lokacin NUAB ya dago kansa cikin wani irin slow ya juyo yana sauke idanuwansa masu kaifi akanta a karan farko daya ke sanin asalin kamanninta da baima saniba,
Dagowa da juyowansa ya saka kowa tsayawa kallansa banda ita data riqe Asim dake neman sarewa qasa sbd abinda ta fada jikinta na rawa muryanta na rawa dukkanin haukacewanta na bayyana idanuwanta na rufewa kaman yanda zuciyarta ta rufe ta qanqame hannuwansa tana cewa
'Asim shine yayi sanadin halin dayake ciki,
Shine ya zabeta akaina,
Shine ya zabi 'danta akan nawa dan,
Shine ya zabi binta qasarta yabar qasarsa da ni da yayana,
Shine yace yana sonta,
Ita yake tsananin so ba ni ba,
Sbd ita ya sauka mulki sbd ita a yanzu komai na rayuwarsa yake tafiya,
Na tambayesa yace Allah ne ya saka masa hakan dan haka bazan iyaba na zabi mutuwa tareda shi sbd nasan nima mutuwar zanyi gwara na fara turasa.....
Miqewa tsaye NUAB yayi sbd yanda kalamanta ke jijjiga kwakwalwansa suna tsinka jijiyoyin jikinsa.
Yana miqewa Aleey ya saka kiran keelah a wayarsa ya bada umarnin a kai securities bangaren queen haile ba ba wanda zai sake fita daga bangaren har yayanta.
NUAB kallo daya yayi mata da idanuwansa bayan ya miqe ya dauke idanuwansa sbd abinda yakeji zai iya fasa kanta da hannunsa a gurin take dan haka juyawa yayi yana fuskantar kofar dakin da sultan yake yana kasa cewa komai tukuna.
Kadir ma baqin ciki da tashin hankalin abinda take fada sakawa yayi ya rasa abin fada ya juya baya yana dafe goshinsa da hannuwansa tareda rintse idanuwansa.
Asim kuwa da yayi mutuwan tsaye sbd tashin hankali sakinta yayi yana ja da baya ahankali tareda rintse idanuwansa hannuwansa na wata irin rawa,
Kafin ya iya dawowa daidai daga tashin hankalin daya shiga NUAB ya bude baki batareda ya juyo ba yacewa aleey akaita bangarenta a rufeta a cikinsa ya sallami duka bayin dake bangaren da duk wani me rai dayake ciki ita kadai zaa bari a rufe bangaren ba shiga ba fita tukuna.
Asim na jin hakan wasu hawaye masu tsananin zafin gaske suka gangaro masa ya rintse ido ya bude yana tabbatarda Allah ne kadai a yanxu zai fidda mamin daga wannan kaddara data jawa kanta me muni.
Aleey da daman jiran umarnin yake wayarsa ya daga zai saka kiran wainda zasu shigo su tafi da ita Asim kallansa yayi cikin wani irin mutuwan jiki yace ya bari zai kaita da kansa.
Hakan daya fada ya saka kadir kallansa hakama aleey din.
NUAB kuwa buqatan a fice da itan yake ba bata lokaci dan shaqar numfashin tsayuwanta agurin kadai toshe kirjinsa yakeyi yana neman saka masa kasa iya riqe kansa gurin mata illa.
Asim hannu ya miqa ya kama hannunta yayi gaba da ita tafara tirjewa tana kokarin kwacewa da karfi tana ihun ambatar bazata tafi koina ba sai likitocin sun fito sun sanar da mutuwar sultan.
Yanda take maimaita kalman da karfi tana kwacewa tana tirjewa Asim yana janta ya saka kadi binta a bayan yana turata cikin zafin zuciya da baqin ciki hakama aleey yana bayansu dan tabbatarda ta isa inda akace a kaita din.
Kuka takeyi sosai tana ihun fadan jiran labarin mutuwan sultan din sbd mutuwan ce ta dace dashi,
Mutuwansa ce zata saka ayanah ghaz a cikin baqin cikin datake son ganinta.
Tsit koina yayi ihun maganganunta ne kadai suke amsawa koina tana fada da karfin gaske dan NUAB yaji shima baqin cikin datake ji ya kashesa.
Asim kuwa hawaye yake fiddawa masu radadi da baqin ciki yana kasa sakin hannunta tana dukansa tana son kwacewa amma ya kasa sakinta haka ya nufi bangarenta da ita Aleey da securities da fadawa marasa imani suna biye dasu.
Tin kafin su iso su Aslam da aka fito dasu suka nufo hanyar cikin babban tashin hankalin da basu taba shigaba sbd jin abinda ya faru.
Cikin tashin hankali da tsoron gaske suka yo kanta tana ihu har lokacin tana jin idan bata ji zancen mutuwar sultan da kunnuwanta ba zata iya mutuwa sbd baqin ciki.
Kuka me karfin gaske dayake hade da mummunan tashin hankali Aslam ta fasa tana kokarin kama Mamin itama amma sam idan mutuwan sultan zaa fada mata ba batason komai.
Shigewa akai da ita bangaren har tsakiyar palonta Asim ya jijjigata da karfin gaske yana ambatar sunanta da karfin gaske yace
'Mami ki dawo hankalinki sbd Sultan bazai mutuba insha Allah,
Bazaki taba saka Ayanah baqin cikin da kikeson gani a tattare da itaba sbd ta dade da shiga kowane kalan baqin cikin rayuwa,
Babu sauran baqin cikin dazaizo mata a ayanzu da bata taba shigarsaba,
Zatai baqin ciki da radadin rasa Sultan idan ya rasu amma bazata mutu ba zata rayu kuma hankali zata dawo farin ciki sbd haka rayuwan take dan haka bazaki iya saka mata dawwamamman baqin ciki ba idan ba Allah daya halicceta ba,
Kin aikata babban kuskuren da daga lokacinda kika shayar da uban yayanki mijinki gubar mutuwa kika dasawa kanki baqin cikin da zaki dawwama cikinsa,
Meyasa zakiyi hakan mami?
Meyasa kika bari shedan ya rufe zuciyar dake kirjinki da idanuwanki?
Meyasa zaki saka mu a cikin wannan halin da babu abinda zamu iya miki dan cetanki?
Meyasa zaki sakamu a halinda zamu kalla hukunci ya hau kanki batareda munada ikon komaiba.
Kuka me karfin gaske ya zowa meryam itama jin kalamansa na karshe dan kuwa da gasken basuda abinda zasu iya yimata a matsayinsu na yayanta sbd Allah ya kwace dukkanin dama daga hannunsu,
Aslam kasa cewa komai tayi suka zuba dukansu qasa a gabanta suna fasa kuka suna rerowa mai tsananin shiga zuciya,
Daga mata da yayan dasuka fi kowace me rai dake boyem daraja yau sun zama mafi qasqancin rayuka a boyem sbd abinda Mamin tayi ayau zai shiga tarihin da har jikokin jikokinta zaa fada,
Zuriarta bazasu taba sake daraja ko ta qimar kallo ce daga yanzu har abada a tarihin boyem,
Jininta daga yanzu sun rasa daraja da martabarsu da jininsu sbd abinda tayi hatta matsayinsu duka zasu rasa a cikin masarautar da duniya gabaki daya.
Kukan da sukeyi mai tsananin karfi da tsima jikin kowannensu yana jijjiga ya sakata zamewa itama ta zube qasa tana fasa kukan tareda cusa kanta cikin kafafunta zuciyarta na mata wani irin tsananin zafi da ciwo da radadin da nauyin datake jin har numfashinta yana toshewa.
Shi kansa Asim din kuka yakeyi sosai mara sauti jikinsa na rawa yana jin inama baizo duniya a cikin jinin sarauta ba,
Inama ya fara zuwa bangaren Maminsa kafin ta fita tayi wannan aikin mummunan kaddarar,
Inama tin suna yara suka gane komai suka sauya rayuwar da zata amfanesu ba wannan ba.
Keelah ne da wasu securities suka shigo aka fitar da 'yayan nata suna kuka suna jin wani irin tashin hankali da mummunan tsoro da firgici sbd jin kaman bazasu sake haduwa ba da ita.
Ganin halinda suka shiga suna ficewa zasu barta ya sakata fasa kuka tana riqesu da hannuwanta dake rawa tana cewa kada su barta su tsaya da ita su kadai gareta a yanxu.
Yanda ta rikice tana kuka jikinta na rawa ya sakasu sake shiga mummunan hali amma a haka akai karfin halin rabasu aka fice dasu aka barta tana wani irin jijjiga.
Rufe bangaren akai ba kowa a cikinsa bayan ita aka zagayesa da tsaro me karfin gaske.
Suma su Aslam bangare daya dole suka koma suka zauna cikin tsaka me wuyar tinanin kaddarar data samesu a dare daya.
Asim ma dole bangaren sultan ya koma ya zauna tareda NUAB daya kasa zama da samun kowace irin nutsuwa.
Tsit masarautar ta dauka dare ya sake tsalawa sosai komai ya tsaya musu cak,
Duk wani me matsayi a masarautar da manyan fada tsoffi da sabbi da duk wanda yakeda alaqa da jinin boyem din labarin mummunan lamarin ya isar musu kafin safe dan haka koda aka wayi gari da mummunan labarin aka tashi komai ya tsaya cak ana jiran farfadowansa wadda likitocin sun tabbatarda ba tabbas sunyi iya abinda zasuyi sai ajira hukuncin ubangiji kawai.
#MAMUH
09033181070
[15/01, 2:00 pm] Dasoo: HAYATEEM
Mamuhgee
171
Duk hanyar dasu Ammi zasu samu labarin abinda yake faruwa NUAB ya saka aleey ya toshe ta sbd sam anqi barin kowace kafar media ta fidda labarin hakama masarautar tin daga babbar gate din farko aka dakatar da kowace irin shiga da kowace irin fita komai ya tsaya a yanda yake sai an samu sanin halinda sultan zai kasance,
Babu wanda ya rintsa babu wanda ya matsa,
Sallar asuba ce kadai ta fiddasu amma suna bangaren sultan din sun kasa sun tsare suna jiran tsammani cikin zallar fargaba.
Guraren karfe goma sha daya da rabi Bahar ce ta fara kirasa sbd ganin bai kiraba lokacinda ya saba kira,
Bai bari ta fahimci komai ba sukai magana sama sama sbd itama bata jin dadi,
Suna gama wayar ba dadewa Amminsa ma ta kirasa jikinta a sanyaye sukai magana itama ta kashe tana kasa kiran sultan sbd batason shiga haqqin haile ko nasa hakama shi daya saba kira bai kira din ba dan haka ta hakura tana hana kanta kira dan basu lokacin daya kamata.
Shima Asim leylah ta kirasa ganin be kira dinba sukai magana ta kashe tana jin damuwa a ranta sbd shi kam bai iya dannewa da boye damuwansa kaman NUAB ba dan haka ta fahimci akwai damuwa tattare dashi ta tambaya kuma yace ba komai.