Sashe 100
Hayateem Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yana tinkarar bangaren nata da securities din da aka zuba suka janye sun bar bangaren ana cewa ta rasu sbd babu sauran abinda ya rage musu suyi
Wani sautin ihun kukan Meryam ne da nysah ke amsa kuwwa da amo tin daga nesa ya fara jiyowa kafafunsa suka fara neman sarewa daqyar ya iso bangaren yana shigowa a palonta na farko ya tadda gawarta a rufe gaban yan uwansa dake wani irin kuka me ratsa rai da kunnuwa da tashin hankali.
Zubewa yayi kan kafafunsa yana rintse idanuwansa hawaye na qafewa daga idanuwanta jikinsa na rawa cira ya rarrafo ya iso gaban gawar ya saka hannu ya bude fuskanta yana budewa ya saki rufar yana sunkuyar da kansa tareda dunqule hannuwansa dake fizga yana kasa dagowa.
Gabaki daya yan uwansa su ukun kuka sukeyi mai tsananin gaske kaman rayukansu zasu fita sbd iya su yayanta ne kadai suka sani tukuna dan an hana kowa zuwa bangaren.
Jikinsa Nysah ta fada ta qanqamesa tana kukan da sam bayajin komai shi sbd jinsa da ganinsa sun dauke dip na wucin gadi.
Babu wanda yayi yunkurin shigowa saida aka basu lokaci suna kukansu da tashin hankalinsu na farko tukuna aka janyesu ana ficewa dasu.
Acan ma dakin sultan bayan ficewan Asim kadir ya bude ido ya kalla yana buqatan a kawo wheelchair dinsa a ajiye a kusa sbd dole zaije gurin gawar haile yayi mata addua a matsayinsa na mijinta da harta bar duniya akwai aure a tsakaninsu.
NUAB kuwa shiru yayi yana kasa motsawa bare tashi daga zaunen dayake yana kallo Sultan ya saka kadir ya dauke takardar gabansa ya fice da ita dan qonawa sbd maganar saukansa mulki sam bama zata fita daga dakin ba bare wani yaji dan kuwa a yanxu babu sultan din da boyem take tsananin buqata da so kamarsa dan haka ko baya boyem matiqar yana raye NUAB bazai taba sauka mulki ba sai lokacin saukansa yayi hakama dole a yanxu bazaiyi zaman dindindin a anjom ba zai dawo boyem da Ayanah sbd su tsaya a karkashin mulkin 'dansu dan basa cikakkiyar albarkarsu a ko yaushe.
******kaman yanda masarautar take cikin shiru da jimamin halinda Sultan ya shiga haka ta sake daukan wani shirun na rasuwan haile wadda tini akace ayi shirinta dan janaizarta batareda bata lokaci ba dan babu amfanin sake kwananta a duniya ba rufeba akan tsarin musulunci.
Fadar irin mummunan halin da Yayanta suke ciki da iyayenta da Asim bame yiyuwa bane dan kuwa a abinda bai wuce awanni ba take suka sauya mummunar kama,
Suna ji suna gani akaiwa mahaifiyarsu sutura sai a lokacin aka turo sultan akan kujera baida kuzari ko kadan da lafiya har zuwa bangarenta cikin palonta gaban gawarta da aka gama shiryawa aka fito da ita,
Yayanta ne a zagaye da ita koda ya iso dan haka kowa ficewa yayi aka barsa daga shi sai yayan nata sukai mata addua.
Sun dan dauki lokaci a ciki kafin sultan ya fito aka turasa zuwa komawa bangarensa sbd bazai iya fita janaizar ba daqyar yake jan numfashinsa daidai ma.
Karfe biyar da mintina akai janaizar haile wadda ta tara dubban jamaa dik da anyi janaizar a lokacinda mutane ma basu gama ankarewa da labarin rasuwan tata ba.
Ankaita gidanta na gaskia an dawo kowa ya shige bangarensa sbd bazaayi zaman gaisuwan ba a bisa ga umarnin daya fito daga sultan yasar.
Shi kansa Asim ba iya matan kadai ba shima bangarensa ya shige ba shiga ba fita baya buqatan fitowa ko ganin kowa.
Leylah ce a tareda shi cikin tsananin damuwa da kulawa tana masa addua tana kokarin basa juriya da karfin zuciya da basa addua sbd kada damuwa ta sakasa mantawa da riqe fadan Allah a bakinsa.
Haka aka wuni a masarautar tsit kaman ba rasuwa akaiba tin karfe 8 da mintina kowane sahu ya dauke a cikin masarautar gabaki daya babu motsi ko sautin komai.
NUAB yana bangaren mahaifinsa tareda shi saida ya tabbatar angama basa dukkanin kulawan daya kamata dasu maganinsa tukuna ya fito ya fice zuwa bangarensa ya nufi bathroom kai tsaye ya cire komai na jikinsa ya sakarwa kansa ruwa yana rufe idanuwansa ahankali yana sauke numfashi me dumi sbd daga karshe Allah me iko yayi yanda yakeso ga duka wanda yaso.
Yana fitowa wanka shirin bacci yayi ya haye lafiyayyan gadonsa ya dauki wayarsa dake kan gefen gadonsa ya nemo numbern ghaz princess ya saka kira.
Bata shiga ba dan haka bai damuba ya sake saka kiran har so kusan biyar amma sam kiran baya tafiya,
Time ya juya ya kalla yaga dare yayi dan haka bazai kira maa sakinah ba yaji ko lafiya baya samunta zai bari sai gobe tukuna duk da a yanzu sun saba babu daren da suke iya bacci batareda sunyi magana ba ko a wannan kwanakin dayake cikin damuwa da tension babu daren da basa waya.
Ajiye wayar yayi yana kwantawa ahankali tareda rufe idanuwansa cikin nutsuwa yana sake fidda numfashi da ajiyan zuciyar da tin rana yake saukewa baisan dalili ba.
A daidai wannan lokacin kuwa acan anjom likitoci sunyi nasarar tsayar da ciki bahar din dayake kokarin zubewa cikin ikon Allah,
Su Ammi dake cikin tashin hankali kashi kashi suna jin an samu tsaida cikin ajiyan zuciya suka ringa jerowa a tare suna godewa Allah musamman Ammin datake jin kaman wani barin jikin nata ne zata sake rasawa idan ta rasa jinin dayake asalin jininta dana Abaas kaman yanda suke fada dan kuwa hada yayansu aure ba shine asalin hada zuriarba abinda zaa haifa dinne.
Bacci mai karfi ne ya sauke Bahar din bayan azababbiyar wuyar data sha wanda ta dauka itama mutuwan zatai,
Bayan wucewan doctors din da gama fada musu hutu sosai na kwana biyu take buqata cikin ya sake tsayawa daidai ba abinda take buqata sai cire damuwa kwata kwata daga ranta.
Suna tafiya shiga dakin Ammi tayi tana isa bakin gadon da bahar din ke kwance tana bacci ta zauna tana dafa goshinta tareda shafawa tana jin tsananin kaunarta da tausayinta na wahalar datasha.
Tenya ce ta kwashi kayan jinin da aka lalata sosai ta fita dasu ta bawa su Naima su wanke.
Basu iya fadawa NUAB abinda ake ciki ba dan haka suma boyo suka hau sbd hana sabon tashin hankalin da zasu iya gani idan ya sani.
Kulawa da wani irin tattali na musamman aka fara nunawa bahar din wadda bata farka ba sai asuba,
Maa sakinah ce ta kwana tareda ita dan haka ruwan wanka masu zafi ta hada mata ta shiga ta dan gasa jininta ta jima kafin ta fito ruwan tayi wanka da alwala ta fito tayi sallah tana idarwa tea me zafi da baa saka shuga ba sedai zuma aka kawo mata da naman da aka dafa mata tin dare akai warming taci kadan tasha magani ta koma ta kwanta take wani baccin ya kuma dauketa.
Koda garin ya waye har rana Bahar na bacci dan haka suka sake tsayuwa akan kulawa da ita da cikin da yanzu shine hankalinsu ya taallaka akai,
Ammi ma hankalinta a rabe biyu yake matiqar gaske sbd bugun zuciyarta ya kasa dawowa daidai idan ba sultan taje ta duba yanda yake ba.
Su kansu su maa sakinah da suka fahimci hakan kuma ko babu komai tana tsananin buqatan kasancewa dashi a wannan lokacin da baida kowa a cikin matansa sai ita ga rashin lafiya dan haka maa sakinah ta nuna mata ta wuce boyem din kawai ita zata tsaya da bahar har saita warke sosai dan babu yanda zaayi doguwan tafiya da ita a wannan halin datake ciki.
Su zuhrah ma hakan sukaga ya kamata dan haka suka karfafa tafiyan tata,
Ita kanta Bahar tana tsananin son Ammin ta tafi sbd sultan da NUAB suna buqatarta.
Ganin Bahar din ta samu sauki ba laifi a cikin kwana daya da wuni kuma jinin ya tsaya cak alaman cikin ya tsaya sai kawai ta shirya tafiyar batareda NUAB ya saniba dan kwata kwata ta dena daukan wayansa dan batasan yasan abinda yake faruwa anan din.
Washe gari aka gama komai suka bar anjom zuwa Bahanian babban garin qasar da Airport yake dan bin jirgi zuwa boyem.
Ammi da tenya da zuhrah ne suka tafi sai bayi biyu aka barsu da tarin sauran duka bayin,
Suna wucewa Bahar ta sauke ajiyan zuciya tana jin samun nutsuwa tafiyan Ammin,
Wayarta ta saka Naimah ta dauko mata ta kunna take massages dinsa suka fara shigowa a hankali tana kallansu cikin nutsuwa da jiran su gama shigowa.
Suna gama shigowa babu wanda ta iya dubawa sbd zuciyarta datai rauni dan haka ta saka kiran numbernsa a natse tana sakawa a speaker ta ajiye gefen gadonta tareda zamewa ta kwanta kan gadon datake zaune ta kwantar da kanta a pillow tana jin wayar na ringing har saida kiran ya kusa yankewa tukuna ya daga a natse sbd yana bacci ne wanda bai samu yi ba tsawon kwanakin.
Cikin muryansa da sauran bacci yake cikinta me kauri da wani irin nauyi da bayyanarda zamtowansa cikakke kuma namiji ba kadan ba ya ambaci sunanta da wani irin slow daya sakata bude idanuwanta dake rufe ta zubawa wayar ido.
#MAMUH
09033181070
[16/01, 12:02 pm] Dasoo: HAYATEEM
Mamuhgee
174
Jin shiru ya sakasa bude baki a cikin nutsuwa ya sake ambatar sunan dayake kiranta dashi ghaz princess,
Ajiyan zuciya ta sake mai sanyi da nutsuwa wadda sautinta ya ratsa wayar ya shiga kunnuwansa ya bude idanuwansa dake da nauyi har lokacin dakyau tareda fidda numfashi me sanyi shima sbd daga karshe ya samu jin abinda ruhinsa yake tsananin buqatan ji wato koda sautin fitar numfashinta ne.
Kasa magana tayi tana ji ya fara mata magana a natse da wani irin kamewa da tsantsar soyayyarta data gama dashi yasan tana jinsa duk abinda yake fada.
Saida ya gama maganar ta fara fidda hawaye sautin kukanta na fita kadan ta ambaci sunansa sai kawai ta kasa cewa komai ta ringa kukan tana jin gabaki daya ma duk batada lafiya.
Shiru yayi sautin kukanta na ratsashi yana tayar da duk wata tsigar jikinsa a hankali zuciyarsa na sosuwa da jin duniyarsa ta tsaya cak ita kadai yake tsananin son gani a gabansa.
Wani sautin ihun kukan Meryam ne da nysah ke amsa kuwwa da amo tin daga nesa ya fara jiyowa kafafunsa suka fara neman sarewa daqyar ya iso bangaren yana shigowa a palonta na farko ya tadda gawarta a rufe gaban yan uwansa dake wani irin kuka me ratsa rai da kunnuwa da tashin hankali.
Zubewa yayi kan kafafunsa yana rintse idanuwansa hawaye na qafewa daga idanuwanta jikinsa na rawa cira ya rarrafo ya iso gaban gawar ya saka hannu ya bude fuskanta yana budewa ya saki rufar yana sunkuyar da kansa tareda dunqule hannuwansa dake fizga yana kasa dagowa.
Gabaki daya yan uwansa su ukun kuka sukeyi mai tsananin gaske kaman rayukansu zasu fita sbd iya su yayanta ne kadai suka sani tukuna dan an hana kowa zuwa bangaren.
Jikinsa Nysah ta fada ta qanqamesa tana kukan da sam bayajin komai shi sbd jinsa da ganinsa sun dauke dip na wucin gadi.
Babu wanda yayi yunkurin shigowa saida aka basu lokaci suna kukansu da tashin hankalinsu na farko tukuna aka janyesu ana ficewa dasu.
Acan ma dakin sultan bayan ficewan Asim kadir ya bude ido ya kalla yana buqatan a kawo wheelchair dinsa a ajiye a kusa sbd dole zaije gurin gawar haile yayi mata addua a matsayinsa na mijinta da harta bar duniya akwai aure a tsakaninsu.
NUAB kuwa shiru yayi yana kasa motsawa bare tashi daga zaunen dayake yana kallo Sultan ya saka kadir ya dauke takardar gabansa ya fice da ita dan qonawa sbd maganar saukansa mulki sam bama zata fita daga dakin ba bare wani yaji dan kuwa a yanxu babu sultan din da boyem take tsananin buqata da so kamarsa dan haka ko baya boyem matiqar yana raye NUAB bazai taba sauka mulki ba sai lokacin saukansa yayi hakama dole a yanxu bazaiyi zaman dindindin a anjom ba zai dawo boyem da Ayanah sbd su tsaya a karkashin mulkin 'dansu dan basa cikakkiyar albarkarsu a ko yaushe.
******kaman yanda masarautar take cikin shiru da jimamin halinda Sultan ya shiga haka ta sake daukan wani shirun na rasuwan haile wadda tini akace ayi shirinta dan janaizarta batareda bata lokaci ba dan babu amfanin sake kwananta a duniya ba rufeba akan tsarin musulunci.
Fadar irin mummunan halin da Yayanta suke ciki da iyayenta da Asim bame yiyuwa bane dan kuwa a abinda bai wuce awanni ba take suka sauya mummunar kama,
Suna ji suna gani akaiwa mahaifiyarsu sutura sai a lokacin aka turo sultan akan kujera baida kuzari ko kadan da lafiya har zuwa bangarenta cikin palonta gaban gawarta da aka gama shiryawa aka fito da ita,
Yayanta ne a zagaye da ita koda ya iso dan haka kowa ficewa yayi aka barsa daga shi sai yayan nata sukai mata addua.
Sun dan dauki lokaci a ciki kafin sultan ya fito aka turasa zuwa komawa bangarensa sbd bazai iya fita janaizar ba daqyar yake jan numfashinsa daidai ma.
Karfe biyar da mintina akai janaizar haile wadda ta tara dubban jamaa dik da anyi janaizar a lokacinda mutane ma basu gama ankarewa da labarin rasuwan tata ba.
Ankaita gidanta na gaskia an dawo kowa ya shige bangarensa sbd bazaayi zaman gaisuwan ba a bisa ga umarnin daya fito daga sultan yasar.
Shi kansa Asim ba iya matan kadai ba shima bangarensa ya shige ba shiga ba fita baya buqatan fitowa ko ganin kowa.
Leylah ce a tareda shi cikin tsananin damuwa da kulawa tana masa addua tana kokarin basa juriya da karfin zuciya da basa addua sbd kada damuwa ta sakasa mantawa da riqe fadan Allah a bakinsa.
Haka aka wuni a masarautar tsit kaman ba rasuwa akaiba tin karfe 8 da mintina kowane sahu ya dauke a cikin masarautar gabaki daya babu motsi ko sautin komai.
NUAB yana bangaren mahaifinsa tareda shi saida ya tabbatar angama basa dukkanin kulawan daya kamata dasu maganinsa tukuna ya fito ya fice zuwa bangarensa ya nufi bathroom kai tsaye ya cire komai na jikinsa ya sakarwa kansa ruwa yana rufe idanuwansa ahankali yana sauke numfashi me dumi sbd daga karshe Allah me iko yayi yanda yakeso ga duka wanda yaso.
Yana fitowa wanka shirin bacci yayi ya haye lafiyayyan gadonsa ya dauki wayarsa dake kan gefen gadonsa ya nemo numbern ghaz princess ya saka kira.
Bata shiga ba dan haka bai damuba ya sake saka kiran har so kusan biyar amma sam kiran baya tafiya,
Time ya juya ya kalla yaga dare yayi dan haka bazai kira maa sakinah ba yaji ko lafiya baya samunta zai bari sai gobe tukuna duk da a yanzu sun saba babu daren da suke iya bacci batareda sunyi magana ba ko a wannan kwanakin dayake cikin damuwa da tension babu daren da basa waya.
Ajiye wayar yayi yana kwantawa ahankali tareda rufe idanuwansa cikin nutsuwa yana sake fidda numfashi da ajiyan zuciyar da tin rana yake saukewa baisan dalili ba.
A daidai wannan lokacin kuwa acan anjom likitoci sunyi nasarar tsayar da ciki bahar din dayake kokarin zubewa cikin ikon Allah,
Su Ammi dake cikin tashin hankali kashi kashi suna jin an samu tsaida cikin ajiyan zuciya suka ringa jerowa a tare suna godewa Allah musamman Ammin datake jin kaman wani barin jikin nata ne zata sake rasawa idan ta rasa jinin dayake asalin jininta dana Abaas kaman yanda suke fada dan kuwa hada yayansu aure ba shine asalin hada zuriarba abinda zaa haifa dinne.
Bacci mai karfi ne ya sauke Bahar din bayan azababbiyar wuyar data sha wanda ta dauka itama mutuwan zatai,
Bayan wucewan doctors din da gama fada musu hutu sosai na kwana biyu take buqata cikin ya sake tsayawa daidai ba abinda take buqata sai cire damuwa kwata kwata daga ranta.
Suna tafiya shiga dakin Ammi tayi tana isa bakin gadon da bahar din ke kwance tana bacci ta zauna tana dafa goshinta tareda shafawa tana jin tsananin kaunarta da tausayinta na wahalar datasha.
Tenya ce ta kwashi kayan jinin da aka lalata sosai ta fita dasu ta bawa su Naima su wanke.
Basu iya fadawa NUAB abinda ake ciki ba dan haka suma boyo suka hau sbd hana sabon tashin hankalin da zasu iya gani idan ya sani.
Kulawa da wani irin tattali na musamman aka fara nunawa bahar din wadda bata farka ba sai asuba,
Maa sakinah ce ta kwana tareda ita dan haka ruwan wanka masu zafi ta hada mata ta shiga ta dan gasa jininta ta jima kafin ta fito ruwan tayi wanka da alwala ta fito tayi sallah tana idarwa tea me zafi da baa saka shuga ba sedai zuma aka kawo mata da naman da aka dafa mata tin dare akai warming taci kadan tasha magani ta koma ta kwanta take wani baccin ya kuma dauketa.
Koda garin ya waye har rana Bahar na bacci dan haka suka sake tsayuwa akan kulawa da ita da cikin da yanzu shine hankalinsu ya taallaka akai,
Ammi ma hankalinta a rabe biyu yake matiqar gaske sbd bugun zuciyarta ya kasa dawowa daidai idan ba sultan taje ta duba yanda yake ba.
Su kansu su maa sakinah da suka fahimci hakan kuma ko babu komai tana tsananin buqatan kasancewa dashi a wannan lokacin da baida kowa a cikin matansa sai ita ga rashin lafiya dan haka maa sakinah ta nuna mata ta wuce boyem din kawai ita zata tsaya da bahar har saita warke sosai dan babu yanda zaayi doguwan tafiya da ita a wannan halin datake ciki.
Su zuhrah ma hakan sukaga ya kamata dan haka suka karfafa tafiyan tata,
Ita kanta Bahar tana tsananin son Ammin ta tafi sbd sultan da NUAB suna buqatarta.
Ganin Bahar din ta samu sauki ba laifi a cikin kwana daya da wuni kuma jinin ya tsaya cak alaman cikin ya tsaya sai kawai ta shirya tafiyar batareda NUAB ya saniba dan kwata kwata ta dena daukan wayansa dan batasan yasan abinda yake faruwa anan din.
Washe gari aka gama komai suka bar anjom zuwa Bahanian babban garin qasar da Airport yake dan bin jirgi zuwa boyem.
Ammi da tenya da zuhrah ne suka tafi sai bayi biyu aka barsu da tarin sauran duka bayin,
Suna wucewa Bahar ta sauke ajiyan zuciya tana jin samun nutsuwa tafiyan Ammin,
Wayarta ta saka Naimah ta dauko mata ta kunna take massages dinsa suka fara shigowa a hankali tana kallansu cikin nutsuwa da jiran su gama shigowa.
Suna gama shigowa babu wanda ta iya dubawa sbd zuciyarta datai rauni dan haka ta saka kiran numbernsa a natse tana sakawa a speaker ta ajiye gefen gadonta tareda zamewa ta kwanta kan gadon datake zaune ta kwantar da kanta a pillow tana jin wayar na ringing har saida kiran ya kusa yankewa tukuna ya daga a natse sbd yana bacci ne wanda bai samu yi ba tsawon kwanakin.
Cikin muryansa da sauran bacci yake cikinta me kauri da wani irin nauyi da bayyanarda zamtowansa cikakke kuma namiji ba kadan ba ya ambaci sunanta da wani irin slow daya sakata bude idanuwanta dake rufe ta zubawa wayar ido.
#MAMUH
09033181070
[16/01, 12:02 pm] Dasoo: HAYATEEM
Mamuhgee
174
Jin shiru ya sakasa bude baki a cikin nutsuwa ya sake ambatar sunan dayake kiranta dashi ghaz princess,
Ajiyan zuciya ta sake mai sanyi da nutsuwa wadda sautinta ya ratsa wayar ya shiga kunnuwansa ya bude idanuwansa dake da nauyi har lokacin dakyau tareda fidda numfashi me sanyi shima sbd daga karshe ya samu jin abinda ruhinsa yake tsananin buqatan ji wato koda sautin fitar numfashinta ne.
Kasa magana tayi tana ji ya fara mata magana a natse da wani irin kamewa da tsantsar soyayyarta data gama dashi yasan tana jinsa duk abinda yake fada.
Saida ya gama maganar ta fara fidda hawaye sautin kukanta na fita kadan ta ambaci sunansa sai kawai ta kasa cewa komai ta ringa kukan tana jin gabaki daya ma duk batada lafiya.
Shiru yayi sautin kukanta na ratsashi yana tayar da duk wata tsigar jikinsa a hankali zuciyarsa na sosuwa da jin duniyarsa ta tsaya cak ita kadai yake tsananin son gani a gabansa.