Sashe 30
Hayateem Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shiru shiru har kukan nata ya dena fita tsawon lokaci kafin tayi shiru ajiyan zuciya kadai take iya saukewa mara karfi a jikin Sultan din wanda har lokacin yake rungume da ita batareda tace komaiba ya bata damar tayi kukan da duk ta buqata yi.
Wuni guda cur babu sakon komai daga bangaren Ammin zuwa na sultan LEUL hakama Sultan yasar sai daya tabbatarda ta samu wani irin dangana sbd adduoi da Bahar daya ringa tinatar mata da ita wanda ya saka zuciyarta jin danganar da bata taba tinanin samuba a irin wannan ranar.
Cikin nutsuwa sultan ya sanar da ita ta shirya a goben zai kaita har gaban kabarin Abaass.
Bayan fitar sultan babu wanda ta buqaci gani bayan Bahar wadda maa sakinah ta kawo mata ita har dakin ta fice ta basu guri.
Daga su maa sakinga har NUAB da har lokaci yake jiran kowane irin sako cikin rashin dadin zuciya shiru sukaji,
Leylah data kasa sanin meyake faruwa dakinta ta koma ta zauna bakin gado ta fasa wani kukan baqin cikin dayake cinta yana nukurkusan rayuwar ganin Bahar ta shige har dakin Ayanah shiru,
Wayarta ta dauka ta saka kiran mahaifiyarta wadda tana dauka kai tsaye batareda taji komai daga baki leylah din ba ta sanar da ita jirgin safe zata biyo zuwa boyem din a gobe.
#MAMUH
09033181070
[12/01, 10:50 am] Asia ahmd: HAYATEEM
Mamuhgee
101
Shiru bangaren yayi wanda babu motsin kowa bare na komai har safiya ta waye Bahar na dakin Ayanah wanda hakan ya bawa Sakinah nutsuwa sosai da samun kwanciyan hankali,
Kwantar da kan Bahar tayi a kafafunta suka kwana a hakan shiru batareda kowannensu yace komai ba ajiyan zuciya kawai take iya saukewa ahankali cikin tsananin sanyin jiki da jin dumin kan bahar na ratsata tamkar Abaas dinta ne a kan kafafunta kaman yanda yakeyi a baya da suna gaban iyayensu cikin mutuncinsu da gatansu tareda asalinsu ba yanzu da dukkaninsu suka rasa asali da rayuwarsu ba duniya ta rarrabasu ga kaddara daban daban.
Ita kanta Bahar shiru tayi kawai a lafe tinani kala kala a ranta a haka suka ratsa daren har zuwa asuba.
Sallar asubar ce ta fiddo Bahar din wadda har lokaci itama leylah ta kasa rintsawa taji motsin fitowanta ta dago idanuwanta da suka qanqance ta kalli kofar tareda sauke wata wahalallan ajiyan zuciya tana rintse ido har Bahar din ta qarasa ficewa daga palon.
Dakin maa ta nufa ta shiga tareda nufar bathroom kai tsaye wanda motsinta ne ya tada Maa din wadda ta farka tana miqewa zaune tana saukowa gadon kanta yayi nauyi sbd rashin samun baccin da wuri sbd halinda suka kasance a ranar da daren.
Bata wani jima sosai ba ta fito tana kallan Maa din wadda itama ita ta kalla tareda kama hannunta kadai ta sumbata ta shafa kanta tukuna ta wuce bathroom din itama dan sallar da aka tayar a masallacin masaurautar.
Bahar dinma Kayan jikinta ta sauya zuwa doguwar riga Abayar sallah ta tada sallar.
Kusan a tare da maa suka sallame sallar sukai addua sosai dasu azkar kafin suka gama Maa ta kalleta tareda sake rarrashinta da nasihu masu kyau akan hakuri da tawakkali na maraicin da Allah ya kaddaro mata kafin ta fara sake bayyanar mata da labarin asalin waye ayanah a gurin Abaas hakama waye Abaass a gurin Ayanaah dan haka kaman ayanzu da ayanah tasan waye ita tana tabbatar mata da kaf duniya babu wanda zaiso ta kaman yanda ayanah zata sota ta kaunaceta kaman ayanar.
Suna dakin basu fito ba har karfe goma na safe sbd Bahar sai a lokacin baccin ya dauketa me karfin gaske.
Maa sakinah ce ta fito karfe goman ta isa har bedroom din ayanah wadda ta tadda a shirye tsaf idanuwanta sunyi mugun kumbara da ja hakama fuskarta tayi jajir,
Hakuri ta fara bata akan boyewan da sukai mata kafin itama ta dora da tata nasihar ta girman daukan tawakkali akan kowace kaddarar ubangiji tareda tayata murnar kasancewan NUAB mijin Bahar wanda Abaas ya sheda hakan kafin barinsa duniya.
Numfashi me dumi da mutuwan jiki ayanah kawai ta iya saukewa tareda lumshe idanuwanta tana gyada kai kawai bata iya cewa komaiba.
Tenya ce ta shigo dakin ta hada luggages masu shegiyar tsada na tafiyar da Ayanah din zatai a safiyar tareda sultan yasar bama tareda Sultan NUAB ya sani ba har lokacin sbd tsawon daren bai rintsa ba jiran kowane irin kira daga bangaren yake.
Karfe goma da rabi Sultan yasar ya aika kiran Aslam batareda sanin kowaba ya sanar da ita su shirya yau suma jirginsu zai daga zuwa india ya gama hada musu komai batareda sanin kowa ba dan yasan komai da suke ciki hakama bayason kowama ya sani dan haka kai tsaye su ya fara tabbatarda barinsu boyem kafin shima karfe sha daya jirginsa ya daga da Ayanah batareda sanin NUAB ba wanda Ayanah din tayita kiran wayarsa bata shiga kuma bata cikin nutsuwan da zata iya aikawa kiransa dan ko magana kwata kwata batason yi idanuwanta da ruhinta babu abinda yake tsananin kewa da so kamar isa qasarta garinta cikin gidansu a gaban kabarin iyayenta da dan uwanta.
Daga ita sai sultan din sai tenya da wasu bayinta biyu sai kuma securities din Sultan din masu karfin gaske.
Suna ficewa daga masarautar motocin da suka dauko yunar da matarsa Zuhrah ghaz suna isowa gate din shigowa masarautar suka shigo cikin nasu securities din tareda babban danta 'dan uwan haihuwan Leylah Shuraim boyem.
Shigowansu masarautar wadda take da dibbin tarihi me girman gaske a rayuwar zuhrah da yan uwanta ya saka jikinta daukan wata irin rawa bugun zuciyarta na qaruwa da nauyin kirji idanuwanta sukai jajir,
'Danta shuraim dake gefenta juyowa yayi a natse ya kalleta cikin sanyi da nutsuwa sbd shine kadai yasan asalin tarihin mahaifiyarsa data fada masa a lokacin daya fahimci tana cikin quncin dayake ganinta a ciki tin tasowansa bai huta ba saida yasan tarihinta kuma yayi alkawarin sadata da yar uwarta wadda dokar mulkin boyem ta rabasu sunaji suna gani.
Hannunsa ya daga ahankali ya dora akan hannunta yana kamawa tareda kallanta dan bata nutsuwar abinda yasan tana ji a zuciyarta.
Bude motocin sukai suka fito securities suka fidda kayansu zuwa bangaren masaukin mai girma yunar din.
Suna isa bangaren nasu leylah ta iso bangaren cikin tsananin kewan iyayenta da damuwan datake ciki ta rungume mahaifiyarta tana jero ajiyan zuciya.
Sakin Mum din tata tayi ts juya gurin mahaifinta shima ta dan rungumesa tayi masa varka da zuwa kafin ta koma gurin dan uwanta twin dinta shuraim suka rungume juna yana jin tausayin ganin yanayinta dan kuwa yanada labarin qin karban auren ta da Sultan LEUL NUAB yayi.
Hutawa zasuyi na gajiyan da suka debo kafin neman Sultan NUAB zuwa gobe su tayasa murnar Hawansa mulki dan kuwa suna isowa aka sanar dasu tafiyar sultan yasar dan haka dole zasu jira saiya dawo yanda ma zasu huta dakyau sosai musamman a yanzu da yunar yake shawaran dawowa boyem da zama sbd yarsa da zata zama sarauniyar boyem tinda NUAB ya karbi sarautar mulkin boyem din.
Sai karfe biyun rana baya sallan azahar mai girma sultan LEUL NUAB ya tinkaro bangaren mahaifiyarsa wanda yake tsit ba motsi ko hayaniya ko kadan sbd babu kowa,
Maa sakinah bata bangaren ta nufi bangaren babban store na masarautar gabaki daya dan dauko abubuwan abincinsu da sukai qasa tareda bayin da zasu dauko mata da abinda ake turawa dan daukowa,
Bahar ce kadai a bangaren itama bata wani jima da tashi ba sallah ta fara yi tana idarwa ta fada toilet tayo wanka ta wanke kanta kaman yanda ta saba ta fito ruwa na tsiyayowa daga gashinta ahankali fatarta na daukan ido sbd lafiya da haske.
Towel qarami ta dauka ta goge kanta ra rage ruwan kanta sosai ta ajiye ta nufi gaban mirror ta dauki turare ta shafa bayan ta dan shafa mai kadan tana jona hand dryer zata fara busar da gashinta aka taba kofar dakin a natsen daya sakata juyowa ahankali ta kalli kofar da idanuwanta masu haske da saukai wani laushin baccin data jima tayi sunyi wani ciki cikin daukan hankali.
Bude kofar yayi kai tsaye kaman yanda ya saba tareda sako kai fuskarsa fresh komai nasa kaman bai taba shiga rana ba dan kuwa sosai kwanciyan hankali da hutunsa ya bayyana a tattare dashi,
Dakatawa tayi cak daga inda take tsaye tana kallansa zuciyarta na dan sauya bugawa
Shima idanuwansa akanta suka sauka dan haka ya fara kallan dakin a kame da izza baiga kowa a dakin ba sai ita din sbd yaje baiga Ammin ba hakama maa tenya dan haka yayo dakin,
Akanta ya dawo da idanuwansa ya tsayar yana kallan fuskarta data dauke idanuwanta akansa tareda kokarin juyawa tabar dakin ta koma bathroom amma takunsa data ji me cikeda zallan izza da iko ya sakata dakatawa tareda juyowa tana qin kallansa taga ita din yake tinkarowa dan haka ta fara ja baya a natse tana qin dagowa ta kallesa duk da tana jin idanuwansa masu kaifi da azabtarwa akanta,
Bata tsayaba sbd shima din bai tsayaba sai dataji ta isa jikin mirror batada gurin sake motsawa shi kuwa a gabanta gap da ita ya tsaya cak har lokacin idanuwansa masu gasa ruwan jikinta suna kanta,
Qamshinsa ne yayi mata yawan dap hancinta da gangar jikinta bazasu daukaba ta dago ahankali zata kalli fuskarsa sai kuma idanuwanta suka kasa qarasawa ta dauke kai tana kokarin juyawa ya qara taku daya zuwa gareta wanda ya sakata yin baya tana dafa hannuwanta da gaban babban mirror din take hannunta ya taba dryer data dauki dan zafi take tayi saurin sake yar qara mara karfi tana dago hannun da sauri wanda ya kama da hannunsa daya a cikin wata irin nutsuwa da wani irin kallan daya sakata kallansa batareda tasan tayi hakan ba.
Cikin idanuwanta yakewa natsatsen kallo yana shigar da dogayen lafiyayyun yartsun hannunsa cikin nata yana kama yatsar daya dan kone din tareda qarasa matseta jikin mirror din sanyin gashinta yana fidda qamshin man datake wanke kan dashi me sanyin kamshi yana shiga hancinta ya juyar da idonsa akan gashin nata yana binsa da kallo sanyin cikinsa na sake saukar masa a fuska,
Wuni guda cur babu sakon komai daga bangaren Ammin zuwa na sultan LEUL hakama Sultan yasar sai daya tabbatarda ta samu wani irin dangana sbd adduoi da Bahar daya ringa tinatar mata da ita wanda ya saka zuciyarta jin danganar da bata taba tinanin samuba a irin wannan ranar.
Cikin nutsuwa sultan ya sanar da ita ta shirya a goben zai kaita har gaban kabarin Abaass.
Bayan fitar sultan babu wanda ta buqaci gani bayan Bahar wadda maa sakinah ta kawo mata ita har dakin ta fice ta basu guri.
Daga su maa sakinga har NUAB da har lokaci yake jiran kowane irin sako cikin rashin dadin zuciya shiru sukaji,
Leylah data kasa sanin meyake faruwa dakinta ta koma ta zauna bakin gado ta fasa wani kukan baqin cikin dayake cinta yana nukurkusan rayuwar ganin Bahar ta shige har dakin Ayanah shiru,
Wayarta ta dauka ta saka kiran mahaifiyarta wadda tana dauka kai tsaye batareda taji komai daga baki leylah din ba ta sanar da ita jirgin safe zata biyo zuwa boyem din a gobe.
#MAMUH
09033181070
[12/01, 10:50 am] Asia ahmd: HAYATEEM
Mamuhgee
101
Shiru bangaren yayi wanda babu motsin kowa bare na komai har safiya ta waye Bahar na dakin Ayanah wanda hakan ya bawa Sakinah nutsuwa sosai da samun kwanciyan hankali,
Kwantar da kan Bahar tayi a kafafunta suka kwana a hakan shiru batareda kowannensu yace komai ba ajiyan zuciya kawai take iya saukewa ahankali cikin tsananin sanyin jiki da jin dumin kan bahar na ratsata tamkar Abaas dinta ne a kan kafafunta kaman yanda yakeyi a baya da suna gaban iyayensu cikin mutuncinsu da gatansu tareda asalinsu ba yanzu da dukkaninsu suka rasa asali da rayuwarsu ba duniya ta rarrabasu ga kaddara daban daban.
Ita kanta Bahar shiru tayi kawai a lafe tinani kala kala a ranta a haka suka ratsa daren har zuwa asuba.
Sallar asubar ce ta fiddo Bahar din wadda har lokaci itama leylah ta kasa rintsawa taji motsin fitowanta ta dago idanuwanta da suka qanqance ta kalli kofar tareda sauke wata wahalallan ajiyan zuciya tana rintse ido har Bahar din ta qarasa ficewa daga palon.
Dakin maa ta nufa ta shiga tareda nufar bathroom kai tsaye wanda motsinta ne ya tada Maa din wadda ta farka tana miqewa zaune tana saukowa gadon kanta yayi nauyi sbd rashin samun baccin da wuri sbd halinda suka kasance a ranar da daren.
Bata wani jima sosai ba ta fito tana kallan Maa din wadda itama ita ta kalla tareda kama hannunta kadai ta sumbata ta shafa kanta tukuna ta wuce bathroom din itama dan sallar da aka tayar a masallacin masaurautar.
Bahar dinma Kayan jikinta ta sauya zuwa doguwar riga Abayar sallah ta tada sallar.
Kusan a tare da maa suka sallame sallar sukai addua sosai dasu azkar kafin suka gama Maa ta kalleta tareda sake rarrashinta da nasihu masu kyau akan hakuri da tawakkali na maraicin da Allah ya kaddaro mata kafin ta fara sake bayyanar mata da labarin asalin waye ayanah a gurin Abaas hakama waye Abaass a gurin Ayanaah dan haka kaman ayanzu da ayanah tasan waye ita tana tabbatar mata da kaf duniya babu wanda zaiso ta kaman yanda ayanah zata sota ta kaunaceta kaman ayanar.
Suna dakin basu fito ba har karfe goma na safe sbd Bahar sai a lokacin baccin ya dauketa me karfin gaske.
Maa sakinah ce ta fito karfe goman ta isa har bedroom din ayanah wadda ta tadda a shirye tsaf idanuwanta sunyi mugun kumbara da ja hakama fuskarta tayi jajir,
Hakuri ta fara bata akan boyewan da sukai mata kafin itama ta dora da tata nasihar ta girman daukan tawakkali akan kowace kaddarar ubangiji tareda tayata murnar kasancewan NUAB mijin Bahar wanda Abaas ya sheda hakan kafin barinsa duniya.
Numfashi me dumi da mutuwan jiki ayanah kawai ta iya saukewa tareda lumshe idanuwanta tana gyada kai kawai bata iya cewa komaiba.
Tenya ce ta shigo dakin ta hada luggages masu shegiyar tsada na tafiyar da Ayanah din zatai a safiyar tareda sultan yasar bama tareda Sultan NUAB ya sani ba har lokacin sbd tsawon daren bai rintsa ba jiran kowane irin kira daga bangaren yake.
Karfe goma da rabi Sultan yasar ya aika kiran Aslam batareda sanin kowaba ya sanar da ita su shirya yau suma jirginsu zai daga zuwa india ya gama hada musu komai batareda sanin kowa ba dan yasan komai da suke ciki hakama bayason kowama ya sani dan haka kai tsaye su ya fara tabbatarda barinsu boyem kafin shima karfe sha daya jirginsa ya daga da Ayanah batareda sanin NUAB ba wanda Ayanah din tayita kiran wayarsa bata shiga kuma bata cikin nutsuwan da zata iya aikawa kiransa dan ko magana kwata kwata batason yi idanuwanta da ruhinta babu abinda yake tsananin kewa da so kamar isa qasarta garinta cikin gidansu a gaban kabarin iyayenta da dan uwanta.
Daga ita sai sultan din sai tenya da wasu bayinta biyu sai kuma securities din Sultan din masu karfin gaske.
Suna ficewa daga masarautar motocin da suka dauko yunar da matarsa Zuhrah ghaz suna isowa gate din shigowa masarautar suka shigo cikin nasu securities din tareda babban danta 'dan uwan haihuwan Leylah Shuraim boyem.
Shigowansu masarautar wadda take da dibbin tarihi me girman gaske a rayuwar zuhrah da yan uwanta ya saka jikinta daukan wata irin rawa bugun zuciyarta na qaruwa da nauyin kirji idanuwanta sukai jajir,
'Danta shuraim dake gefenta juyowa yayi a natse ya kalleta cikin sanyi da nutsuwa sbd shine kadai yasan asalin tarihin mahaifiyarsa data fada masa a lokacin daya fahimci tana cikin quncin dayake ganinta a ciki tin tasowansa bai huta ba saida yasan tarihinta kuma yayi alkawarin sadata da yar uwarta wadda dokar mulkin boyem ta rabasu sunaji suna gani.
Hannunsa ya daga ahankali ya dora akan hannunta yana kamawa tareda kallanta dan bata nutsuwar abinda yasan tana ji a zuciyarta.
Bude motocin sukai suka fito securities suka fidda kayansu zuwa bangaren masaukin mai girma yunar din.
Suna isa bangaren nasu leylah ta iso bangaren cikin tsananin kewan iyayenta da damuwan datake ciki ta rungume mahaifiyarta tana jero ajiyan zuciya.
Sakin Mum din tata tayi ts juya gurin mahaifinta shima ta dan rungumesa tayi masa varka da zuwa kafin ta koma gurin dan uwanta twin dinta shuraim suka rungume juna yana jin tausayin ganin yanayinta dan kuwa yanada labarin qin karban auren ta da Sultan LEUL NUAB yayi.
Hutawa zasuyi na gajiyan da suka debo kafin neman Sultan NUAB zuwa gobe su tayasa murnar Hawansa mulki dan kuwa suna isowa aka sanar dasu tafiyar sultan yasar dan haka dole zasu jira saiya dawo yanda ma zasu huta dakyau sosai musamman a yanzu da yunar yake shawaran dawowa boyem da zama sbd yarsa da zata zama sarauniyar boyem tinda NUAB ya karbi sarautar mulkin boyem din.
Sai karfe biyun rana baya sallan azahar mai girma sultan LEUL NUAB ya tinkaro bangaren mahaifiyarsa wanda yake tsit ba motsi ko hayaniya ko kadan sbd babu kowa,
Maa sakinah bata bangaren ta nufi bangaren babban store na masarautar gabaki daya dan dauko abubuwan abincinsu da sukai qasa tareda bayin da zasu dauko mata da abinda ake turawa dan daukowa,
Bahar ce kadai a bangaren itama bata wani jima da tashi ba sallah ta fara yi tana idarwa ta fada toilet tayo wanka ta wanke kanta kaman yanda ta saba ta fito ruwa na tsiyayowa daga gashinta ahankali fatarta na daukan ido sbd lafiya da haske.
Towel qarami ta dauka ta goge kanta ra rage ruwan kanta sosai ta ajiye ta nufi gaban mirror ta dauki turare ta shafa bayan ta dan shafa mai kadan tana jona hand dryer zata fara busar da gashinta aka taba kofar dakin a natsen daya sakata juyowa ahankali ta kalli kofar da idanuwanta masu haske da saukai wani laushin baccin data jima tayi sunyi wani ciki cikin daukan hankali.
Bude kofar yayi kai tsaye kaman yanda ya saba tareda sako kai fuskarsa fresh komai nasa kaman bai taba shiga rana ba dan kuwa sosai kwanciyan hankali da hutunsa ya bayyana a tattare dashi,
Dakatawa tayi cak daga inda take tsaye tana kallansa zuciyarta na dan sauya bugawa
Shima idanuwansa akanta suka sauka dan haka ya fara kallan dakin a kame da izza baiga kowa a dakin ba sai ita din sbd yaje baiga Ammin ba hakama maa tenya dan haka yayo dakin,
Akanta ya dawo da idanuwansa ya tsayar yana kallan fuskarta data dauke idanuwanta akansa tareda kokarin juyawa tabar dakin ta koma bathroom amma takunsa data ji me cikeda zallan izza da iko ya sakata dakatawa tareda juyowa tana qin kallansa taga ita din yake tinkarowa dan haka ta fara ja baya a natse tana qin dagowa ta kallesa duk da tana jin idanuwansa masu kaifi da azabtarwa akanta,
Bata tsayaba sbd shima din bai tsayaba sai dataji ta isa jikin mirror batada gurin sake motsawa shi kuwa a gabanta gap da ita ya tsaya cak har lokacin idanuwansa masu gasa ruwan jikinta suna kanta,
Qamshinsa ne yayi mata yawan dap hancinta da gangar jikinta bazasu daukaba ta dago ahankali zata kalli fuskarsa sai kuma idanuwanta suka kasa qarasawa ta dauke kai tana kokarin juyawa ya qara taku daya zuwa gareta wanda ya sakata yin baya tana dafa hannuwanta da gaban babban mirror din take hannunta ya taba dryer data dauki dan zafi take tayi saurin sake yar qara mara karfi tana dago hannun da sauri wanda ya kama da hannunsa daya a cikin wata irin nutsuwa da wani irin kallan daya sakata kallansa batareda tasan tayi hakan ba.
Cikin idanuwanta yakewa natsatsen kallo yana shigar da dogayen lafiyayyun yartsun hannunsa cikin nata yana kama yatsar daya dan kone din tareda qarasa matseta jikin mirror din sanyin gashinta yana fidda qamshin man datake wanke kan dashi me sanyin kamshi yana shiga hancinta ya juyar da idonsa akan gashin nata yana binsa da kallo sanyin cikinsa na sake saukar masa a fuska,