Sashe 17
Hayateem Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tsayuwa tayi a gabansa shi da Maa sakinah ta juya ta kalleta dakyau kafin ta dawo da kallanta akan Asim din ta Bude baki cikin kamewan mutunci da tattaro tata nutsuwar da itama take Neman kubuce mata tace
'barkan li'ul Asim da zuwa Amma nasan zuwan nan akwai Sakon dayake tafe dashi'
Bai iya batawa kansa lokaci ba sbd a matiqar matse yake da fitar hankali sbd ganin Bahar a yau din dolen dolene ko zai juya masarautar tas da bincike Dan haka Bude Baki yayi yafara jeho mata tambayar da baa cikin hayyacinsa yayi ta ba kawai amsa daya yake son fara ji duk da Babu abinda amsar Zata haifar ko hanawa akan mallakar da zaiwa Bahar da tsananin son dayake mata wanda shima a karan farko bai karbi hukuncin sultan ba,
'Menene gaskiyar auren da NUAB yace yanada shi da Bahar?
Dumm ayanah taji kunnuwanta sunyi da maganar ta sauka cikinsu wadda ta sakata juyowa a hankali ta kalli Maa sakinah taga ko taji zancen da Asim din yake fada,
Sake maimaita tambayarsa yayi wannan karan kaman kirjinsa zai Bude da tsabar tsananin baqin ciki da mummunan tashin hankalin sbd yawun bakinsa ma harsun qafe tsaf Babu komai a baki da maqoshin nasa sai kumfa,
Sauke Kai sakinah tayi zuciyarta da jikinta suna mutuwa da Sanyin data kasa furta komai bare iya kallan ayanah,
Dawo da kallo kansa ayanah tayi tana taqaita mamakin tambayarsa datazo mata a bazata tace
'NUAB baida auren kowa a yanzu ne zaiyi auren kaman yanda duniya ta sani.....
Katseta Asim yayi da cewa
'a Ina take yanzu?
A Ina tenya take shirinsu?
A Ina ne zan ganta kafin wayewan garin gobe da Zata fuskanci hukuncin kisar da mahaukacin masarautar nan ya ja mata....
Dan Allah idan kunsan a inda suke ku sanar Dani...
Kasa Dena karyata mamakinta da shakkarta ayanah tayi tana juyowa gabaki daya ta kalli sakinah wadda har lokacin kanta a qasa yake taqi fadar komai akan komai Dan bazata taba iya karya alkawarinta ba Dan haka ta zabi shiru a daidai wannan lokacin da komai ma ya kwabe Dan idan har maganar Asim gaskia ce kenan maganar auren ta fitarwa sultan,
Wasu zafafan hawaye masu tsananin ciwon gaske take riqewa tana hanasu sauko mata har Asim din ya kasa gane komai da samun komai daga garesu ya juya a fusace kaman zararre ya fice,
Yana ficewa barin gurin sakinah tayi ta nufi dakinta tana isa tura Kofa kawai ta iya yi ta Zame qasa tareda fasa wani irin kuka me tsima zuciya sbd batajin Zata iya rayuwa a yanzu Kam idan akaiwa Bahar irin wannan hukun dayake zallan zalinci,
Ayanah turo kofar dakin tayi tareda tsananin tashin hankalin abinda kunnuwanta suke kasa fahimtar koma menene,
Kukan data tarar sakinah na yi me karfin gaske jikinta na wata irin rawan ya sakata tsayawa cak a bakin kofar dakin tana kasa dauke idonta akanta zarginta akan sakinar yana tabbatuwa gabaki daya akwai abinda take boye mata,
Cikin karfin Hali ayanah datake jin tsananin tsoron amsar da Zata Samu akan tambayarta ta Bude Baki muryanta na rawan gaske tace
'Waye Bahar???
#MAMUH
09033181070
[12/01, 10:50 am] Asia ahmd: HAYATEEM
Mamuhgee
87
Kasa dagowa sakinah tayi tana sake cusa kanta a qasa kukanta mara sauti yana fara fidda sautin daya saka gabaki daya gashin jikin ayanah miqewa tana jin bugun zuciyarta na qaruwa me tsananin gaske,
Kasa iya Bude Baki ta furta wata tambayar tayi sbd yanda kirjinta ya toshe da fara tinanin Bahar din wadda bata taba sanin ko Kamannin dake kan fuskarta ba Amma a yanzu a yanda take ji bata buqatar kowa yayi mata bayanin komai akan Bahar din wadda abubuwa da dama suke da rudani akan,
NUAB wanda bai taba ko kallan kowace mace ba bare sanin Lamarinta Amma sosai abubuwa suke Linkin yarinyar dashi wanda take son sani ayau hakama tanada abubuwan datake son zuciyarta ta Samu tabbacinsu akan yarinyar ko Zata Samu sukunin data rasa na zuciya da ruhi tin daga ranar da idanuwanta suka sauka akan lambar bautar datake jikinta wadda tinawa kadai hana numfashinta futa daidai yakeyi,
'AYANAH BAHAR shine suna cikakken da sakinah ta ambaci yarinyar dashi idan bata manta ba,
Hakama a dakin sakinah yarinyar tamkar take rayuwa shima idan ta Tina daidai kenan,
Hakama NUAB idan ta Tina daidai Kai tsaye ya hada fatar hannunsa data yarinyar a gaban idanuwansu yana ficewa da ita batareda ya raba fatar tafin hannunsa da tata ba gurin Janta??
Bahar,Bahar' sunan ya maimaitu a zuciyarta wadda gabaki daya ta rikice Dan haka bata sake cewa kala ba ta juya ta fice bayi kusan biyar suna biye da ita ta fice daga bangaren nata idanuwanta suna wata irin sauyawa sbd matsananin bugu da mummunan tashin hankalin daya cike zuciyarta,
Itace mutum ta daya datasan inda su Leylah suke shima Leylah dince ta sanar mata a waya a waya sbd tenya sultan ya umarceta da kashe wayarta ma kwata kwata dan haka Kai tsaye can ta nufa batareda barin kowa yaganta ba,
Tana barin bangaren nata Salman dayake boye yana gadin bangaren Dan tabbatarda duk wanda ya fito ya bisa yaga inda zasu sbd sun tabbatarda bazaa rasa wanda yasan inda suke ba,
A sace baya fidda sautin ko numfashi me karfi yabi bayan Wishmah da bata ko ganin gabanta da bayinta.
Asim kuwa daga wannan bangaren na Wishmah daya bari bangaren mahaifiyarsa ya fada Babu abinda yake amfanin arziki bare cikakken hankali a jikinsa hatta kafafuwansa rawa sukeyi,
Haile dake zaune cikin matsanancin ciwon Rai me zafin gaske tana ganinsa wani irin qaruwa taji baqin cikinta yanayi sbd shine yake kokarin lalata komai na shekarun da suka debo suna tsarawa da gwagwarmaya,
Qarasowa yayi gaban hailen ba tsammani ya zube a qasa kan gwiwoyinsa tareda fasa mata wani irin kukan daya sakata kusan sumewa a zaune sbd tsananin mamaki da tashin hankalin abinda zai saka namiji kamarsa kuka Dan bata tinanin ko mutuwa tayi a yanda yake namiji kuma magajin da zai mulki boyem yayi kuka irin hakan.
Kafafunta ya kama da hannuwansa duka biyu cikin wani irin mummunan Hali ya Bude Baki yace
'mamee Dan Allah ki bawa Sultan hakuri kada a kashe Bahar wlh Kila bazan rayuba idan ta bar duniya,
Mamee wlh tsananin son gaskia da bantaba tsammanin zanyiba nake mata,
Dan Allah Ina rokon ku tayani Neman mata tsira a gurin sultan
Mamee bazan taba moruwaba idan ba.......
Turesa haile tayi daga gabanta da sauri hannuwanta da dukkanin jikinta suna daukan rawar da komai nata yake shiga zullumin daga Ina wannan masifar ta Samu 'danta da Babu mace a tsari da qaidar rayuwansa a yanzu Amma a lokaci daya ya sauya mata yana Neman zama mara amfani duka akan mace,macen ma baiwa yakewa irin wannan soyayyar??
Zufa ne ya fara keto mata tana rintse idanuwanta tayi baya ta zube a kujera tana dafe kanta ta Bude Baki tace
'wannan wace sabuwar masifar ce kuma ta bullo wa rayuwata ko yanzu data bangaren ayanah,
Ayanah kin gama zama masifa da balain rayuwata data zuriata'
Aslam da meryam ne suka shigo a tare sbd samun cikakken labarin mummunan abinda yake faruwa a fada,
Ganin halinda Asim yake ciki ya saka dukkaninsu tsayawa cikeda mamaki da qarin baqin cikin da suka taho dashi na sanin kukan dayake zubawa tin a fada,
Mameen suka kalla a tare wadda take tsananin kokarin danne abinda take ji a zuciya da jininta sbd zuwa yanzu ta gama tabbatarda sun Samu babbar matsala a rayuwa tinda Asim ya kamu da soyayyar da Zata rusa su Tin daga sama har qasa Dan haka zabi dayane gareta shine ta tabbatarda yarinyar ayau ta bar duniya kafin gobe sbd idan bata nemeta a daren yau ba ta gani a idanuwan Asim ta tabbatarda bazai kwana ayau ba batareda yayi yunqurin tseratar da ita ba ta hanyar guduwa da ita wanda hakan na faruwa Babu inda zasu Kai baa kamasu bama a cikin masarautar bare sukai ga fita kuma hakan hukuncin kisar ne shima zai hau kansa tareda tsinanniyar baiwar Dan haka kafin ma yayi hakan Zata je ta tattabarda yarinyar tabar duniya a daren kafin Asim ya isa,
Aslam da kusan bugawa zuciyarta ke gap dayi sbd baqin cikin Asim kasa magana tayi ta isa gefen mahaifiyar tasu ta zauna tareda kama hannunta daya ta Dora a cinyarta tana Dan riqewa sbd bata sassaucin wutar baqin cikin dayake cin jinin jikinta,
Meryam data kasa tinanin komai sbd mamaki gurin Asim din ta nufa tareda zubewa gabansa tana kamo hannuwansa biyu dake wata irin rawa sosai wadda ta sake daga hankalinsu Dan kamar shima mutuwan zeyi kafin goben,
Rungumesa Meryam tayi da sauri tana ji a jikinta shikenan wlh sun gama samun rashin nasara sbd har abada sbd Asim ya kamu da mummunan zafaffiyar soyayyar da zai iya komai akanta,
Shikenan daga yanzu suma nasu burin ya Kai karshe ya mutu akan idanuwansu,
Wasu hawayen radadin zuciya ne suka gangaro da idanuwanta tana sake rungume Asim din wanda jikinsa ke rawa sosai,
Shiru sukai dukkaninsu a wannan mummunan yanayin kafin Asim din ya kuma miqewa kaman zararre ya fice ya koma bangaren sultan ya zube gwiwoyinsa a qasa sbd sultan din ya bada umarnin baya son ganin kowa sai zuwa dare,
Meryam biyo Asim din tayi itama ta zube a gefensa sbd tayasa rokon sultan ya basa abinda yake so din na afuwa da sassaucin hukuncinsa sbd ita a gurin ta idan samun abinda Asim din yake so zai saka ya dawo hayyacinsa akan abinda suma suke so tabbas Zata tayasa gurfana a cikin ranar har zuwa faduwanta da sultan zai gansu.
#MAMUH
09033181070
[12/01, 10:50 am] Asia ahmd: HAYATEEM
Mamuhgee
88
*****Aleey ne a tsaye cikin yaransu suna tsananta mugun binciken da sukeyi tin dazu din Babu Hutun ko daqiqa daya sbd tabbatarda Neman inda Bahar din take a cikin masarautar,
Maa sakinah ya daga waya ya kira wadda tana ganin Kiran bata ma amsa ba ta nufo bangaren sbd ko gani sosai batayi,
Tana isowa kofar palon NUAB ta kalla wadda tinda ya shiga aka rufe bata budeba sbd yau Kam idan ba shi dinne ya fito da kansa ba Babu wanda ya isa yaje yako bugata bare budewa.
'barkan li'ul Asim da zuwa Amma nasan zuwan nan akwai Sakon dayake tafe dashi'
Bai iya batawa kansa lokaci ba sbd a matiqar matse yake da fitar hankali sbd ganin Bahar a yau din dolen dolene ko zai juya masarautar tas da bincike Dan haka Bude Baki yayi yafara jeho mata tambayar da baa cikin hayyacinsa yayi ta ba kawai amsa daya yake son fara ji duk da Babu abinda amsar Zata haifar ko hanawa akan mallakar da zaiwa Bahar da tsananin son dayake mata wanda shima a karan farko bai karbi hukuncin sultan ba,
'Menene gaskiyar auren da NUAB yace yanada shi da Bahar?
Dumm ayanah taji kunnuwanta sunyi da maganar ta sauka cikinsu wadda ta sakata juyowa a hankali ta kalli Maa sakinah taga ko taji zancen da Asim din yake fada,
Sake maimaita tambayarsa yayi wannan karan kaman kirjinsa zai Bude da tsabar tsananin baqin ciki da mummunan tashin hankalin sbd yawun bakinsa ma harsun qafe tsaf Babu komai a baki da maqoshin nasa sai kumfa,
Sauke Kai sakinah tayi zuciyarta da jikinta suna mutuwa da Sanyin data kasa furta komai bare iya kallan ayanah,
Dawo da kallo kansa ayanah tayi tana taqaita mamakin tambayarsa datazo mata a bazata tace
'NUAB baida auren kowa a yanzu ne zaiyi auren kaman yanda duniya ta sani.....
Katseta Asim yayi da cewa
'a Ina take yanzu?
A Ina tenya take shirinsu?
A Ina ne zan ganta kafin wayewan garin gobe da Zata fuskanci hukuncin kisar da mahaukacin masarautar nan ya ja mata....
Dan Allah idan kunsan a inda suke ku sanar Dani...
Kasa Dena karyata mamakinta da shakkarta ayanah tayi tana juyowa gabaki daya ta kalli sakinah wadda har lokacin kanta a qasa yake taqi fadar komai akan komai Dan bazata taba iya karya alkawarinta ba Dan haka ta zabi shiru a daidai wannan lokacin da komai ma ya kwabe Dan idan har maganar Asim gaskia ce kenan maganar auren ta fitarwa sultan,
Wasu zafafan hawaye masu tsananin ciwon gaske take riqewa tana hanasu sauko mata har Asim din ya kasa gane komai da samun komai daga garesu ya juya a fusace kaman zararre ya fice,
Yana ficewa barin gurin sakinah tayi ta nufi dakinta tana isa tura Kofa kawai ta iya yi ta Zame qasa tareda fasa wani irin kuka me tsima zuciya sbd batajin Zata iya rayuwa a yanzu Kam idan akaiwa Bahar irin wannan hukun dayake zallan zalinci,
Ayanah turo kofar dakin tayi tareda tsananin tashin hankalin abinda kunnuwanta suke kasa fahimtar koma menene,
Kukan data tarar sakinah na yi me karfin gaske jikinta na wata irin rawan ya sakata tsayawa cak a bakin kofar dakin tana kasa dauke idonta akanta zarginta akan sakinar yana tabbatuwa gabaki daya akwai abinda take boye mata,
Cikin karfin Hali ayanah datake jin tsananin tsoron amsar da Zata Samu akan tambayarta ta Bude Baki muryanta na rawan gaske tace
'Waye Bahar???
#MAMUH
09033181070
[12/01, 10:50 am] Asia ahmd: HAYATEEM
Mamuhgee
87
Kasa dagowa sakinah tayi tana sake cusa kanta a qasa kukanta mara sauti yana fara fidda sautin daya saka gabaki daya gashin jikin ayanah miqewa tana jin bugun zuciyarta na qaruwa me tsananin gaske,
Kasa iya Bude Baki ta furta wata tambayar tayi sbd yanda kirjinta ya toshe da fara tinanin Bahar din wadda bata taba sanin ko Kamannin dake kan fuskarta ba Amma a yanzu a yanda take ji bata buqatar kowa yayi mata bayanin komai akan Bahar din wadda abubuwa da dama suke da rudani akan,
NUAB wanda bai taba ko kallan kowace mace ba bare sanin Lamarinta Amma sosai abubuwa suke Linkin yarinyar dashi wanda take son sani ayau hakama tanada abubuwan datake son zuciyarta ta Samu tabbacinsu akan yarinyar ko Zata Samu sukunin data rasa na zuciya da ruhi tin daga ranar da idanuwanta suka sauka akan lambar bautar datake jikinta wadda tinawa kadai hana numfashinta futa daidai yakeyi,
'AYANAH BAHAR shine suna cikakken da sakinah ta ambaci yarinyar dashi idan bata manta ba,
Hakama a dakin sakinah yarinyar tamkar take rayuwa shima idan ta Tina daidai kenan,
Hakama NUAB idan ta Tina daidai Kai tsaye ya hada fatar hannunsa data yarinyar a gaban idanuwansu yana ficewa da ita batareda ya raba fatar tafin hannunsa da tata ba gurin Janta??
Bahar,Bahar' sunan ya maimaitu a zuciyarta wadda gabaki daya ta rikice Dan haka bata sake cewa kala ba ta juya ta fice bayi kusan biyar suna biye da ita ta fice daga bangaren nata idanuwanta suna wata irin sauyawa sbd matsananin bugu da mummunan tashin hankalin daya cike zuciyarta,
Itace mutum ta daya datasan inda su Leylah suke shima Leylah dince ta sanar mata a waya a waya sbd tenya sultan ya umarceta da kashe wayarta ma kwata kwata dan haka Kai tsaye can ta nufa batareda barin kowa yaganta ba,
Tana barin bangaren nata Salman dayake boye yana gadin bangaren Dan tabbatarda duk wanda ya fito ya bisa yaga inda zasu sbd sun tabbatarda bazaa rasa wanda yasan inda suke ba,
A sace baya fidda sautin ko numfashi me karfi yabi bayan Wishmah da bata ko ganin gabanta da bayinta.
Asim kuwa daga wannan bangaren na Wishmah daya bari bangaren mahaifiyarsa ya fada Babu abinda yake amfanin arziki bare cikakken hankali a jikinsa hatta kafafuwansa rawa sukeyi,
Haile dake zaune cikin matsanancin ciwon Rai me zafin gaske tana ganinsa wani irin qaruwa taji baqin cikinta yanayi sbd shine yake kokarin lalata komai na shekarun da suka debo suna tsarawa da gwagwarmaya,
Qarasowa yayi gaban hailen ba tsammani ya zube a qasa kan gwiwoyinsa tareda fasa mata wani irin kukan daya sakata kusan sumewa a zaune sbd tsananin mamaki da tashin hankalin abinda zai saka namiji kamarsa kuka Dan bata tinanin ko mutuwa tayi a yanda yake namiji kuma magajin da zai mulki boyem yayi kuka irin hakan.
Kafafunta ya kama da hannuwansa duka biyu cikin wani irin mummunan Hali ya Bude Baki yace
'mamee Dan Allah ki bawa Sultan hakuri kada a kashe Bahar wlh Kila bazan rayuba idan ta bar duniya,
Mamee wlh tsananin son gaskia da bantaba tsammanin zanyiba nake mata,
Dan Allah Ina rokon ku tayani Neman mata tsira a gurin sultan
Mamee bazan taba moruwaba idan ba.......
Turesa haile tayi daga gabanta da sauri hannuwanta da dukkanin jikinta suna daukan rawar da komai nata yake shiga zullumin daga Ina wannan masifar ta Samu 'danta da Babu mace a tsari da qaidar rayuwansa a yanzu Amma a lokaci daya ya sauya mata yana Neman zama mara amfani duka akan mace,macen ma baiwa yakewa irin wannan soyayyar??
Zufa ne ya fara keto mata tana rintse idanuwanta tayi baya ta zube a kujera tana dafe kanta ta Bude Baki tace
'wannan wace sabuwar masifar ce kuma ta bullo wa rayuwata ko yanzu data bangaren ayanah,
Ayanah kin gama zama masifa da balain rayuwata data zuriata'
Aslam da meryam ne suka shigo a tare sbd samun cikakken labarin mummunan abinda yake faruwa a fada,
Ganin halinda Asim yake ciki ya saka dukkaninsu tsayawa cikeda mamaki da qarin baqin cikin da suka taho dashi na sanin kukan dayake zubawa tin a fada,
Mameen suka kalla a tare wadda take tsananin kokarin danne abinda take ji a zuciya da jininta sbd zuwa yanzu ta gama tabbatarda sun Samu babbar matsala a rayuwa tinda Asim ya kamu da soyayyar da Zata rusa su Tin daga sama har qasa Dan haka zabi dayane gareta shine ta tabbatarda yarinyar ayau ta bar duniya kafin gobe sbd idan bata nemeta a daren yau ba ta gani a idanuwan Asim ta tabbatarda bazai kwana ayau ba batareda yayi yunqurin tseratar da ita ba ta hanyar guduwa da ita wanda hakan na faruwa Babu inda zasu Kai baa kamasu bama a cikin masarautar bare sukai ga fita kuma hakan hukuncin kisar ne shima zai hau kansa tareda tsinanniyar baiwar Dan haka kafin ma yayi hakan Zata je ta tattabarda yarinyar tabar duniya a daren kafin Asim ya isa,
Aslam da kusan bugawa zuciyarta ke gap dayi sbd baqin cikin Asim kasa magana tayi ta isa gefen mahaifiyar tasu ta zauna tareda kama hannunta daya ta Dora a cinyarta tana Dan riqewa sbd bata sassaucin wutar baqin cikin dayake cin jinin jikinta,
Meryam data kasa tinanin komai sbd mamaki gurin Asim din ta nufa tareda zubewa gabansa tana kamo hannuwansa biyu dake wata irin rawa sosai wadda ta sake daga hankalinsu Dan kamar shima mutuwan zeyi kafin goben,
Rungumesa Meryam tayi da sauri tana ji a jikinta shikenan wlh sun gama samun rashin nasara sbd har abada sbd Asim ya kamu da mummunan zafaffiyar soyayyar da zai iya komai akanta,
Shikenan daga yanzu suma nasu burin ya Kai karshe ya mutu akan idanuwansu,
Wasu hawayen radadin zuciya ne suka gangaro da idanuwanta tana sake rungume Asim din wanda jikinsa ke rawa sosai,
Shiru sukai dukkaninsu a wannan mummunan yanayin kafin Asim din ya kuma miqewa kaman zararre ya fice ya koma bangaren sultan ya zube gwiwoyinsa a qasa sbd sultan din ya bada umarnin baya son ganin kowa sai zuwa dare,
Meryam biyo Asim din tayi itama ta zube a gefensa sbd tayasa rokon sultan ya basa abinda yake so din na afuwa da sassaucin hukuncinsa sbd ita a gurin ta idan samun abinda Asim din yake so zai saka ya dawo hayyacinsa akan abinda suma suke so tabbas Zata tayasa gurfana a cikin ranar har zuwa faduwanta da sultan zai gansu.
#MAMUH
09033181070
[12/01, 10:50 am] Asia ahmd: HAYATEEM
Mamuhgee
88
*****Aleey ne a tsaye cikin yaransu suna tsananta mugun binciken da sukeyi tin dazu din Babu Hutun ko daqiqa daya sbd tabbatarda Neman inda Bahar din take a cikin masarautar,
Maa sakinah ya daga waya ya kira wadda tana ganin Kiran bata ma amsa ba ta nufo bangaren sbd ko gani sosai batayi,
Tana isowa kofar palon NUAB ta kalla wadda tinda ya shiga aka rufe bata budeba sbd yau Kam idan ba shi dinne ya fito da kansa ba Babu wanda ya isa yaje yako bugata bare budewa.