← Book details Hayateem Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 91 OF 112

Sashe 91

Hayateem Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tafiyarta ta saka Hankalin haile dake mummunan tashi sbd ta tabbatarda ba dawowa Maraki zatai ba tabarwa Ayanah sultan kenan,
Ita ma hakan ta fara hangowa kanta amma kuma bazatai taba yiyuwaba sbd yayanta da bazata iya barin su mutu a yanda suke a wulaqance ba hakama Asim tafiyarsa sai sake matsowa take ba gudu ba ja da baya ga ayanah sai hidima sukeyi,

Da wane baqin cikin zataji?
Tana nan tana qunci da kwana kukan baqin ciki ayanah ghaz na can na murna da farin cikin samun sultan ga kanta ita kadai Wanda ita kam bazata taba yadda ba bazai taba yiyuwaba,
Idan har bazasu samu sultan ba wlh a yanzu kam zata tabbatarda ayanah ma bazata samesa ba gwara ya mutu suyi takaba kowa ya kama gabansa.
#MAMUH
09033181070
[12/01, 10:12 am] Dasoo: HAYATEEM
Mamuhgee

164
Tinda aka fara hidimar Bahar bata sake haduwa da NUAB ba sbd kwata kwata Maa tenya bata barinsu fita koina sbd gyaran hatta kofar palon barin bangaren basu taba bari ba hakama shi kansa NUAB din ta hanasa zuwa bangaren dan haka iyakacinsa da Bahar din a waya hakama Amminsa ma a waya duk da baisan dalilin hakan ba kawai dai tace masa sai zaa tafi zai sake ganin Bahar kokuma kila saima anjom.

Jin hakan ya shiga mamaki da shakkar ko zai iya dan haka ya dawo kan bahar din da lallabata da rudar da kwakwalwanta da soyayyarsa dan kawai ta samu ta fito ya ganta tin kafin ya zare amma sam ta kasa samun dama sbd ita kanta sai ahankali kwanakin bata jin daidai tana ganin kaman gyaran da ake mata ne da abubuwan shan da ake bata.

Ita kanta leylah ma da aka hanata komai sai a lokacin Asim ya samu kansa a cikin wani irin rashin sukuni da nutsuwa sbd rashin ganinta kwata kwata na kusan sati biyu.

Bai dauka ganinta a kowane dare ba ko rana ya zama dabiar da zata iya hana zuciyarsa nutsuwarta kwata kwata ba sai yanzu dan kuwa hakanan ya zama dan zuwa gaisuwan su Ammi safe da dare amma baa taba barinsa ya ganta ba dan haka ya susuce soyayyarsa dabai saniba ta gama bayyana amma tenya ta masa karfin hali kaman kowa dan sultan ma shiru yake ji.

Yawon Asim ya fara zama abinda ya zama dan kuwa bakin fama ya riqe wuta yaqi saduda hakama sultan kusan umarnin dayake badawa na son gani da magana da Ayanah sunyi yawan daya saka Tenya yanke shawaran su wuce kawai gabaki dayansu a satin maimakon sati me zuwa sbd su qarasa shirinsu acan kafin Su sultan din suzo nan da sati uku daurin aure.

Itama Ayanaah hakan ya mata dan haka ta sanar da sultan ta waya ba gaddama ya amince musu aka fara yi musu shirin wucewa banda gobe.

NUAB a waya shima Ammi ta sanar dashi tafiyar a banda gobe shiru yayi na tsawon mintina kafin yace ba damuwa sukai sallama ya kashe wayar.

Asim ma yanaji a bakin maa tenya dayaxo da daddare suna yar fira sama sama dasu Ammin rikicewa yayi daqyar ya iya riqe kansa ya fice batareda ya zubar da kafafunsa qasa ya rokesuba subarsa yaga leyalah kafin wucewan.

Yana fitowa tinanin yanda zai ganta a daren ya fara yana rasa yanda zaiyi.

Bangaren Mamensa ya tafi ya kasa barin bangaren gabaki daya ya koma nasa,

Bangaren ya rasa dukkanin haske da walwala sbd Mamin dake cikin tsananin baqin ciki da dahun zuciya hakama su Aslam sun dawo bangaren na mamin sbd kowannensu a inda yake damuwa kashesa zatai da qunci dan haka suka dawo bangaren suka dasa wani sabon zaman baqin ciki da kallan ikon Allah da yanda wasu suke rayuwar farin ciki a masarautar tamkar babu su sbd kaman ko uban daya haifesu ya manta su duk sbd sun bijire masa a baya lokacinda yaso sosai inganta rayuwarsu ta hanyar aura musu mazan da daa yanzu suna can suna rayuwar jin dadi da kwanciyan hankali harma da zuria.

Asim da sam ya cire damuwa da baqin ciki da quncin halinda suka samu kansu a ransa sai abin ya zo masa a sauki bayajin ma radadin komai sbd ya yadda da rayuwar bata tsaya anan ba lokaci bai qure ba duka zasu iya wankewa su dasa sabuwar rayuwa,

Su kuwa da basu gane hakanba da mamin tasu daidaicewa kawai sukeyi suna sake dasa baqin ciki da zafi a ransu karshema ganin sukeyi ya juya musu baya bayan akansa sukaita abinda sukaita yi din har suka samu kansu a halinda ake ciki yanzu,

Ya zauna dasu harda mamin tasu gabaki daya yayi musu nasihar cire damuwa da rufe babin rayuwar baya a bude sabuwa wanda hakanne ma ya saka zai bar nan din amma sam sun kasa ganewa su yadda sai ikirarin bazasu taba tafiya subarwa Ayanah ghaz masarautar boyem ba itada ta samesu anan a matsayin baiwa amma ace sun tafi sun bar mata masarautar itada 'danta wanda tarihi acan qarnika na gaba zai taho a tabbacen Baiwa kuma imebēti ta karbi masarautar boyem duka itada 'danta sun karbe komai na qasar sun karbe wanda ya mulketa wato sultan yasar.

Tinanin hakan kadai idan haile dasu aslam din sukai sai suji kaman zasu mutu,
A baya akai lokacinda kaf boyem ba mace me darajarta kasancewanta matar sultan ta farko kuma wadda tafi masa mata duka,hakama mace mafi kyau da ado,hakama mace me karfin iko da isa a cikin matan dake boyem kaf,hakama yayanta sune yaya mafi daraja a qasar amma ayau kamar ma duniya ta manta dasu kwata kwata ko tina da suna raye baa yi sedai ayanah da qasarta Anjom ghaz sbd kawai danta yana mulkin boyem,
Wannan dalilin ya saka taso danta yayi mulki koda zata rasa komai da kowa sbd tasan har abada bazata dena daraja ba harta bar duniya koda kuwa danta ya tsufa ya sauka mulki ne tarihi bazai dena girmamata ba a matsayin uwar sultan da yayi mulki kuma kilama kalar sultan dazai cigaba da mulki idan 'dan Asim ya hau kenan.

Numfashi me sanyi da kokarin dedeta nutsuwa Asim ya sauke yana zaunawa a palon mamin a kujeran datake kallan ta Aslam sbd suna zaune a palon dukansu meryam ta zubawa wayarta ido da hankalinta tana magana ta chat da Nysah kanwarsu akan auren data rufe ido ta fada mata ta samo mata miji acan bangaren dangin mijinta kokuma ta saka mijinta tinda babban mutum ne kuma ya manyanta sosai ya samo mata wanda zai hadasu.

Tin kwanaki sukai maganar kuma nysah taji dadin hakan dan haka taiwa mijinta magana baiji komaiba ya tabbatarda insha Allah zai kawo wanda zai nema aurenta.

Tinda akai hakan yanzu wani kusanci ne sosai ya dawo tsakaninsu biyun dan koyaushe suna kan waya suna maganganunsu tana boyewa maminsu dan kada tai tir da ita akan taje rokon neman miji da kanta kokuma kada islam taji itama tace tanaso azo a bata mata lamari tin bata kama komaiba.

Aslam dake zaune tv take kalla sbd yanxu kallan dole da karfin hali takeyi sbd batada kowane aikin yi a rayuwarta bayan damuwa da janye janyen tinani dan haka take kallan films da series yanzu dan hana zuciya bugawa.

Maminsu na bedroom dinta tana nata ciwon ran daya zama jiki,

Gyara zamansa yayi yana daga wayarsa ya turawa leylah sakon cewa taje tayiwa maminsa bankwana kafin ta wuce goben.

Yana tura sakon wata ajiyan zuciya ya sauke yana jin kaman ya koma kofa ya tsaya kafin ta taho.

Wayar maa tenya data maa sakinah ya nemo ya turawa sakon a tare yana rokar taje taiwa maminsa bankwana sbd a bata girmanta.

Adduar suga sakon akan lokaci yayi yana ajiye wayar zuciyarsa na tsalle da wata irin qaguwa.

Su Maa dama leylah dake daki kusan a tare suka ga sakon dan haka kallan wayarta tayi tana murmushi me sanyi sbd tasan ya fada ne kila sbd ta fito.

Su maa kuwa suna karanta sakon murmushi sukai tareda yaba hankalinsa sbd tabbas yayi tinani me kyau na hakan tinda koba komai uwar miji ce dole a bata girmanta.

Maa tenya dince da kanta ta samu leylah din har daki bayan ta tabbatarda dare ya sake yi sosai dole Asim ya bar bangaren kwata kwata yana nasa tace ta shirya tashiga bangaren haile tai mata sallama.

Ba musu leylan ta amince ta shirya ta fito Maa ta hadata da bayi uku su rakata sbd ita kam bazata iya zuwa bangaren hailen ba sbd gudun fitina da wata damuwar tace su tafi.
#MAMUH
09033181070
[12/01, 2:39 pm] Dasoo: HAYATEEM
Mamuhgee

165
Fitowa sukai daga bangaren bayinta na biye da ita wainda tasan maa ta hadota dasu ne sbd ma kada taje koina dan haka suna fitowan batama kalli kowace hanya ba sai hanyar bangaren Hailen tana sanye da babbar doguwar hijabi har qasa sbd kayan cikin jikinta marasa nauyi ne dan tayi shirin bacci.

Wayarta ma baa bari ta fito da itaba dan haka daga ita sai ita suka iso bangaren.

Acan ciki kuwa mamaki ne su Aslam keyi na yanda Asim ya kasa nutsuwa sai wani kallan waya yakeyi yana kallan kofa hakama har dare sosai yana bangaren,

Babu wanda yace masa komai akan hatta Mamin data fito ta gansa mamaki ta shiga me girma tana Qarasowa ta zauna gefensa tana kallansa zatai magana baiwarta ta shigo a natse ta sanar da ita zuwan leylah wanda ya saka ajiyan zuciya me sanyi tahowa Asim din yana dago kansa ya sauke idanuwansa a kofar shigowa cikin nutsuwa da wata irin kewan dake bayyana a idanuwansa da gangar jikinsa.

Baiwar hailen ce dake gabanta tana mata iso ta bude kofar palon na kurya inda suke a zazzaune tana janyewa daga kofar dan bata damar shigowa.

Kafarta ta fara sakowa a natse cikin palon ita kadai bayinta na palon farko dan basa shigowa nan din.
Chapter 91 · 0% Book details