Sashe 96
Hayateem Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Mahaifinsu wannan shine yancin dayaso tin yanada kuruciyarsa akan mulkin harya manyanta bai cire rai ba saida ya samu yancinsa ya zama free daga duka matakai da daurin da mulkin yake dashi gashi a yanxu ya samu zai bar boyem din ya je ya samu free rayuwar da bai samu a kuruciya ba sai tsufa da macen dazaiso babu kowane irin shamaki sbd mulkin hatta matarka datake rayuwarka akwai sharuddan dasuke hanaka samun soyayyar da kukeso ku nunawa juna,
Bai taso da shaawa ko kaunar mulki ba,
Bai taba tinani ko kawo cewan zai taba hawa karagar mulkin boyem ba,
Baida abinda ya saba dashi ya zama cikon rayuwarsa kaman 'yanci da shimfida rayuwansa akan nasa matakan da raayin da juya rayuwansa yanda yaso wanda a yanxu shima a yanxu karagar mulkin tana kwace masa hakan daya bayan daya dan kuwa duk yanda zai tsara nasa dokokin da yin rayuwan dayake so dole tinda mulkin mutane ne akanka zaka aje wasu da yawan naka abubuwan da kake so ka kama na dokan mulkin.
Rufe idanuwansa da sukai jajir yayi yana jin a karo na babu adadi tinda ya hau shima bazai iyaba,
Bashi karagar mulkin jamaar boyem take buqata ba kaman yanda shima ba ita yake buqata ba kansa yake buqata a matsayin LEUL NUAB me Moscow,
Shi kansa Asim jajir idanuwansa sukai sosai yana kallan NUAB din zuciyarsa na danne duk wani irin radadi da ciwon dayake ji na rabuwa da qasarsa mahaifarsa dama mahaifiyarsa da abubuwa da yawa kuma tafiya da har abada ba dawowa sedai yaxo ganin gida ko wata hidimar ya koma amma ya gama zaman qasar.
Shiru sukai kafin NUAB ya dago idanuwansa ya kalli Asim ya kalli takardar ya maida idanuwansa akan seal din dayake kan table dake can gaban kujeran girmansa.
Nutsuwa ya sake yi ya tsaida idanuwansa akan Asim yana kallansa da dukkanin tinani da tausayin Asim din dashi kansa da yasan bazai iya zama sultan na boyem ba har manyanci da tsufansa ba dan haka bayajin xai taba iya saka hannu ya bari Asim yabar boyem din.
Bude baki yayi zaiyi magana bayan ya sauke numfashi yana tsayar da tinaninsa akan abu daya dan inganta rayuwansu duka aka bude office din.
Aleey ne ya qaraso gurinsu idanuwansa jajir yana hana kansa bayyanarda kowane irin tashin hankali sbd hana jinin sarautar biyu dake zaune shiga kowane irin tashin hankali ko shock.
Da sauti me kokarin bayyanarda kulawa ya sanar dasu ba lafiya ana buqatansu da gaggawa.
Asim dayaji hakan wani nauyi ne dayake kirjinsa ya fada sbd tinda ya zauna yake jin kirjinsa a toshe da nauyi me tsanani.
NUAB kuwa jin yayi duniyarsa dayake ji gabaki daya tin dazu a bushe ta qarasa bushewa tana rushewa.
Kallan Aleey yayi da jajayen idanuwansa sbd jin cikakken abinda yake nifi sbd yasan bayason bayani a taqaice.
Kasa kallan kwayar idanuwansa aleey yayi jikinsa na fidda rawa ya sanar dashi sultan ne lamarin yayi munin fada.
Bai qarasa ba NUAB din ya miqe tsaye yana nufar kofa da wani irin yanayi dake dumama wajen gabaki daya sbd har wani sauti me tada tsigar jiki takunsa ke bayarwa Asim ma na gefensa kusan a tare suke kowane taku cikin zafaffen yanayin daya saka Aleey shima tsananta shiga tashin hankali me tsananin gaske duk da babu wanda ya samu daman shiga cikin bangaren na sultan kadir ne kawai ya kirasa ya sanar masa dan haka ya shigo dan sanar dasu shikuma Keelah ya nufi can din.
Koda suka iso gabaki daya securities da bayin bangaren suna tsaye cak a kofa cikin matsanancin tashin hankali da tsoro da firgici me yawan gaske sbd wani irin magana da kadir keyi cikin matsanancin daga murya dake cike da mummunan tashin hankalin da basu taba jin ya shiga ba.
NUAB da idanuwansa suke wani zafi sbd ja basa kalluwa shine ya fara sako kai bangaren take kowa ya ja baya sosai suna qasa da kai masu zubewa qasa kuwa suna zubewa batareda dagowaba.
Kai tsaye keelah dake tsaye gurin ya bude masa kofa da sauri cikin yanayin qamewa shima
Saka kai NUAB din yayi yana shigewa tareda Asim wanda hannuwansa ke wata irin rawa hakama kirjinsa.
Suna shiga palon na kurya cikin matsanancin tashin hankali suka tsaya cak dukkaninsu sbd ganin kadir yayi kaca kaca da jinin sultan wanda babu alaman rai a tattare dashi kuma har lolacin jini fitowa yakeyi ta hancinsa.
Sarewa kafafun Asim sukai sbd tsananin rawan da suka dauka ya zube a gurin durqushe yana rarrafawa idanuwansa na cikowa da hawayen tashin hankali da tsoro da rikicewa duka a lokaci daya.
Shi kansa NUAB baya yayi kadan saida ya dafa qatuwar verse din glass dake gefensa ta fadi qasa da karfi ta fashe yana neman sake faduwa ya dafa bango da karfi idanuwansa na tsananta radadin da suke masa yaja wani numfashi me zafin gaske yana jin ihun kiran sultan da kadir yakeyi yana ratsa kunnuwansa zuwa kwakwalwansa.
Daqyar ya iya fizgo kansa daga halinda ya shiga na shock ya qaraso gurin cikin taku uku ya zube gaban sultan din yana cirosa daga jikin Kadir ya dawo dashi jikinsa gabaki daya tareda cirasa sukutum yana bude murya da karfin gaske ya qwala kiran aleey wanda amo me karfi ya amsa har zuwa wajen wanda kowa ya sake shiga faduwan gaba aleey kuwa kai tsaye ya shigo cikin rashin bata kowane irin lokaci.
Yana shigowa yaga halinda ake ciki Asim kuka yakeyi sosai yana kasa motsawa hakama kadir a cikin tashin hankali yake da baimasan me zaiyiba.
Hannuwansa na rawa ya ciro wayarsa ya saka kiran likitocinsu gabaki daya daya bayan daya.
Juyawa yayi ya fita yana kallan keelah yace a hana kowa shigowa ko fita daga bangaren da zagayensa ayi sauri a kira securities dinsu.
NUAB bedroom ya wuce da Sultan din da saurin gaske jikinsa na rawa shima kadir na biye dashi hakama Asim miqewa yayi da sauri ya bisu.
Da gaggawa NUAB yace a kawo towels
Jiki na rawa Kadir da Asim na karo da ture juna gurin sauri suka dauko daga inda towels din dakin suke a jere suka kawo masa.
Jinin hancinsa suke kokarin tsayarwa da goge fuskansa data rufe gabaki daya tai kaca kaca da jini Asim kuwa hannuwansa da suka sanqame ya riqe yana dannesu dan a tsaye suke qam.
Kaman Aleey zai tashi sama haka ya tada daren lafiyar masarautar gabaki daya gurin hana kowane motsi koda na dabbane yace a riqesa a inda dik zaa gansa sbd tsayar da komai kafin a samu sanin halinda sultan yake ciki,
Doctors kuwa take wainda ke cikin masarautar akai gaggawar tahowa dasu suna shigewa ciki da wanda yake na mata da wanda yake na yara da wanda yake na shuga da duk ma kowane iri haka aka janyosu tas aka zuba duka a cikin bangaren wanda dole suka taru akan Sultan din kafin isowan babban likitan da NUAB yafi yadda dashi wanda tini keelah ya buga mota cikin mugun speed yaje daukosa dan baa cikin masarautar yake ba shi.
Fitowa sukai suka bawa likitocin daman yin aikinsu akan sultan da babu alaman zai tashi koma ba alaman akwai sauran rai a tattare da jikinsa.
A palon da bedroom din nasa yake suke dukansu kowannensu jikinsa kaca kaca da jini da duk ya bata jikinsu da hannuwansu babu wanda yake jin daidai a kirjinsa sbd yanda suke jin fargaban abinda zai samu Sultan.
Aleey daya shigo NUAB ya kalla wanda idanuwansa suke cak akan kofar dakin yana zaune idon sunyi jajir ya qaraso gefensa ya tsaya yana ciro hankerchief me kyau da tsafta daya dauko sabbi kusan guda biyar ya miqa masa dan goge hannunsa da gefen fuskansa da har acan jinin yakai sbd yanda ya ringa rungumosa.
NUAB din bai karba ba rintse ido kawai yayi yana jin kansa kaman zai tsage biyu,
Abu biyu ne ke neman raba zuciyarsa biyu a lokacin shine tsoron rasa mahaifinsa a matsayinsa na 'da sai kuma tsantsar tsoron halinda Amminsa zata shiga idan ta rasa wani maqoyinta again a rayuwa sbd zuwa yanzu ya yadda da sultan shine wani babban bangaren dayake bawa Ammin farin ciki da nutsuwa.
Kadir ma kansa ne a qasa ya kasa dagowa yana zaune hannuwansa dake lalace ya hadasu guri daya ya riqe yana jin tsoron rasa ubangida kuma Amininsa kwalli daya a duniya tin kuruciya suna tare har tsufa.
Asim da idanuwansa suka gama kumbura da jajir a cikin qanqanin lokaci dagowa yayi ya kalli inda yaji motsi a gefensa Maminsa ta bayyana a gabansa idanuwanta a bushe tana wata irin rawar jikin daya sakasa ambatar sunanta sbd babu wanda ya lura da ita tinda suka shigo tana tsaye a guri daya.
Ambatar sunanta ya saka Kadir dayake cikeda tsananin tsanarta da jin zafinta dagowa ya kalleta yana miqewa tsaye shima Asim tsayen ya miqe sbd ganin kallan da Kadir ke mata me bayyanarda zallan tsana.
Aleey dake gefen NUAB zuba mata ido yayi yana gyara tsayuwa batareda NUAB ya dago ba.
#MAMUH
09033181070
[15/01, 11:27 am] Dasoo: HAYATEEM
Mamuhgee
170
Cikin tsananin daci da baqin ciki kadir ya kalleta yana bude baki yace
'Me yayi zafi da zaki shayar dashi poinson irin wannan?
Cak Asim ya tsaya daga qarasawa inda take yana kallan kadir da jajayen idanuwansa da sauri,
Aleey kuwa gyara tsayuwa yayi yana qarasa maida dukkanin hankalinsa akan abinda yake shirin faruwa tareda sake kallan NUAB yaga bai dago kai ba bare motsawa ko kallan inda hailen take.
Asim ma cikin sauri ya juya ya kalli NUAB din jikinsa na sake daukan sabuwan rawa ya dawo da kallansa akan kadir yana bude baki cikin mummunan yanayi yace
'Me yake faruwa?
Me ya faru?
Ya akai?
Menene ya samu sultan?
Ya kuma akai ya shiga wannan halin?
A rude duka yake jero tambayoyi a rikice yana kallan Kadir.
Wani sabon zufan tsantsan tashin hankali ne ya gangaro daga goshin kadir ya dago jajayen idanuwansa ya kalli Asim din ya bude baki yace
'Mummunan guba ta shayar da sultan gatanan a tsaye,
Ko dana iso tana tsaye a kansa tana kokarin qarasa shi da hannuwanta bayan da bakinta tana fadar idan gubar bata kashesa ba zata qarasa shi da hannuwanta....'
Bai taso da shaawa ko kaunar mulki ba,
Bai taba tinani ko kawo cewan zai taba hawa karagar mulkin boyem ba,
Baida abinda ya saba dashi ya zama cikon rayuwarsa kaman 'yanci da shimfida rayuwansa akan nasa matakan da raayin da juya rayuwansa yanda yaso wanda a yanxu shima a yanxu karagar mulkin tana kwace masa hakan daya bayan daya dan kuwa duk yanda zai tsara nasa dokokin da yin rayuwan dayake so dole tinda mulkin mutane ne akanka zaka aje wasu da yawan naka abubuwan da kake so ka kama na dokan mulkin.
Rufe idanuwansa da sukai jajir yayi yana jin a karo na babu adadi tinda ya hau shima bazai iyaba,
Bashi karagar mulkin jamaar boyem take buqata ba kaman yanda shima ba ita yake buqata ba kansa yake buqata a matsayin LEUL NUAB me Moscow,
Shi kansa Asim jajir idanuwansa sukai sosai yana kallan NUAB din zuciyarsa na danne duk wani irin radadi da ciwon dayake ji na rabuwa da qasarsa mahaifarsa dama mahaifiyarsa da abubuwa da yawa kuma tafiya da har abada ba dawowa sedai yaxo ganin gida ko wata hidimar ya koma amma ya gama zaman qasar.
Shiru sukai kafin NUAB ya dago idanuwansa ya kalli Asim ya kalli takardar ya maida idanuwansa akan seal din dayake kan table dake can gaban kujeran girmansa.
Nutsuwa ya sake yi ya tsaida idanuwansa akan Asim yana kallansa da dukkanin tinani da tausayin Asim din dashi kansa da yasan bazai iya zama sultan na boyem ba har manyanci da tsufansa ba dan haka bayajin xai taba iya saka hannu ya bari Asim yabar boyem din.
Bude baki yayi zaiyi magana bayan ya sauke numfashi yana tsayar da tinaninsa akan abu daya dan inganta rayuwansu duka aka bude office din.
Aleey ne ya qaraso gurinsu idanuwansa jajir yana hana kansa bayyanarda kowane irin tashin hankali sbd hana jinin sarautar biyu dake zaune shiga kowane irin tashin hankali ko shock.
Da sauti me kokarin bayyanarda kulawa ya sanar dasu ba lafiya ana buqatansu da gaggawa.
Asim dayaji hakan wani nauyi ne dayake kirjinsa ya fada sbd tinda ya zauna yake jin kirjinsa a toshe da nauyi me tsanani.
NUAB kuwa jin yayi duniyarsa dayake ji gabaki daya tin dazu a bushe ta qarasa bushewa tana rushewa.
Kallan Aleey yayi da jajayen idanuwansa sbd jin cikakken abinda yake nifi sbd yasan bayason bayani a taqaice.
Kasa kallan kwayar idanuwansa aleey yayi jikinsa na fidda rawa ya sanar dashi sultan ne lamarin yayi munin fada.
Bai qarasa ba NUAB din ya miqe tsaye yana nufar kofa da wani irin yanayi dake dumama wajen gabaki daya sbd har wani sauti me tada tsigar jiki takunsa ke bayarwa Asim ma na gefensa kusan a tare suke kowane taku cikin zafaffen yanayin daya saka Aleey shima tsananta shiga tashin hankali me tsananin gaske duk da babu wanda ya samu daman shiga cikin bangaren na sultan kadir ne kawai ya kirasa ya sanar masa dan haka ya shigo dan sanar dasu shikuma Keelah ya nufi can din.
Koda suka iso gabaki daya securities da bayin bangaren suna tsaye cak a kofa cikin matsanancin tashin hankali da tsoro da firgici me yawan gaske sbd wani irin magana da kadir keyi cikin matsanancin daga murya dake cike da mummunan tashin hankalin da basu taba jin ya shiga ba.
NUAB da idanuwansa suke wani zafi sbd ja basa kalluwa shine ya fara sako kai bangaren take kowa ya ja baya sosai suna qasa da kai masu zubewa qasa kuwa suna zubewa batareda dagowaba.
Kai tsaye keelah dake tsaye gurin ya bude masa kofa da sauri cikin yanayin qamewa shima
Saka kai NUAB din yayi yana shigewa tareda Asim wanda hannuwansa ke wata irin rawa hakama kirjinsa.
Suna shiga palon na kurya cikin matsanancin tashin hankali suka tsaya cak dukkaninsu sbd ganin kadir yayi kaca kaca da jinin sultan wanda babu alaman rai a tattare dashi kuma har lolacin jini fitowa yakeyi ta hancinsa.
Sarewa kafafun Asim sukai sbd tsananin rawan da suka dauka ya zube a gurin durqushe yana rarrafawa idanuwansa na cikowa da hawayen tashin hankali da tsoro da rikicewa duka a lokaci daya.
Shi kansa NUAB baya yayi kadan saida ya dafa qatuwar verse din glass dake gefensa ta fadi qasa da karfi ta fashe yana neman sake faduwa ya dafa bango da karfi idanuwansa na tsananta radadin da suke masa yaja wani numfashi me zafin gaske yana jin ihun kiran sultan da kadir yakeyi yana ratsa kunnuwansa zuwa kwakwalwansa.
Daqyar ya iya fizgo kansa daga halinda ya shiga na shock ya qaraso gurin cikin taku uku ya zube gaban sultan din yana cirosa daga jikin Kadir ya dawo dashi jikinsa gabaki daya tareda cirasa sukutum yana bude murya da karfin gaske ya qwala kiran aleey wanda amo me karfi ya amsa har zuwa wajen wanda kowa ya sake shiga faduwan gaba aleey kuwa kai tsaye ya shigo cikin rashin bata kowane irin lokaci.
Yana shigowa yaga halinda ake ciki Asim kuka yakeyi sosai yana kasa motsawa hakama kadir a cikin tashin hankali yake da baimasan me zaiyiba.
Hannuwansa na rawa ya ciro wayarsa ya saka kiran likitocinsu gabaki daya daya bayan daya.
Juyawa yayi ya fita yana kallan keelah yace a hana kowa shigowa ko fita daga bangaren da zagayensa ayi sauri a kira securities dinsu.
NUAB bedroom ya wuce da Sultan din da saurin gaske jikinsa na rawa shima kadir na biye dashi hakama Asim miqewa yayi da sauri ya bisu.
Da gaggawa NUAB yace a kawo towels
Jiki na rawa Kadir da Asim na karo da ture juna gurin sauri suka dauko daga inda towels din dakin suke a jere suka kawo masa.
Jinin hancinsa suke kokarin tsayarwa da goge fuskansa data rufe gabaki daya tai kaca kaca da jini Asim kuwa hannuwansa da suka sanqame ya riqe yana dannesu dan a tsaye suke qam.
Kaman Aleey zai tashi sama haka ya tada daren lafiyar masarautar gabaki daya gurin hana kowane motsi koda na dabbane yace a riqesa a inda dik zaa gansa sbd tsayar da komai kafin a samu sanin halinda sultan yake ciki,
Doctors kuwa take wainda ke cikin masarautar akai gaggawar tahowa dasu suna shigewa ciki da wanda yake na mata da wanda yake na yara da wanda yake na shuga da duk ma kowane iri haka aka janyosu tas aka zuba duka a cikin bangaren wanda dole suka taru akan Sultan din kafin isowan babban likitan da NUAB yafi yadda dashi wanda tini keelah ya buga mota cikin mugun speed yaje daukosa dan baa cikin masarautar yake ba shi.
Fitowa sukai suka bawa likitocin daman yin aikinsu akan sultan da babu alaman zai tashi koma ba alaman akwai sauran rai a tattare da jikinsa.
A palon da bedroom din nasa yake suke dukansu kowannensu jikinsa kaca kaca da jini da duk ya bata jikinsu da hannuwansu babu wanda yake jin daidai a kirjinsa sbd yanda suke jin fargaban abinda zai samu Sultan.
Aleey daya shigo NUAB ya kalla wanda idanuwansa suke cak akan kofar dakin yana zaune idon sunyi jajir ya qaraso gefensa ya tsaya yana ciro hankerchief me kyau da tsafta daya dauko sabbi kusan guda biyar ya miqa masa dan goge hannunsa da gefen fuskansa da har acan jinin yakai sbd yanda ya ringa rungumosa.
NUAB din bai karba ba rintse ido kawai yayi yana jin kansa kaman zai tsage biyu,
Abu biyu ne ke neman raba zuciyarsa biyu a lokacin shine tsoron rasa mahaifinsa a matsayinsa na 'da sai kuma tsantsar tsoron halinda Amminsa zata shiga idan ta rasa wani maqoyinta again a rayuwa sbd zuwa yanzu ya yadda da sultan shine wani babban bangaren dayake bawa Ammin farin ciki da nutsuwa.
Kadir ma kansa ne a qasa ya kasa dagowa yana zaune hannuwansa dake lalace ya hadasu guri daya ya riqe yana jin tsoron rasa ubangida kuma Amininsa kwalli daya a duniya tin kuruciya suna tare har tsufa.
Asim da idanuwansa suka gama kumbura da jajir a cikin qanqanin lokaci dagowa yayi ya kalli inda yaji motsi a gefensa Maminsa ta bayyana a gabansa idanuwanta a bushe tana wata irin rawar jikin daya sakasa ambatar sunanta sbd babu wanda ya lura da ita tinda suka shigo tana tsaye a guri daya.
Ambatar sunanta ya saka Kadir dayake cikeda tsananin tsanarta da jin zafinta dagowa ya kalleta yana miqewa tsaye shima Asim tsayen ya miqe sbd ganin kallan da Kadir ke mata me bayyanarda zallan tsana.
Aleey dake gefen NUAB zuba mata ido yayi yana gyara tsayuwa batareda NUAB ya dago ba.
#MAMUH
09033181070
[15/01, 11:27 am] Dasoo: HAYATEEM
Mamuhgee
170
Cikin tsananin daci da baqin ciki kadir ya kalleta yana bude baki yace
'Me yayi zafi da zaki shayar dashi poinson irin wannan?
Cak Asim ya tsaya daga qarasawa inda take yana kallan kadir da jajayen idanuwansa da sauri,
Aleey kuwa gyara tsayuwa yayi yana qarasa maida dukkanin hankalinsa akan abinda yake shirin faruwa tareda sake kallan NUAB yaga bai dago kai ba bare motsawa ko kallan inda hailen take.
Asim ma cikin sauri ya juya ya kalli NUAB din jikinsa na sake daukan sabuwan rawa ya dawo da kallansa akan kadir yana bude baki cikin mummunan yanayi yace
'Me yake faruwa?
Me ya faru?
Ya akai?
Menene ya samu sultan?
Ya kuma akai ya shiga wannan halin?
A rude duka yake jero tambayoyi a rikice yana kallan Kadir.
Wani sabon zufan tsantsan tashin hankali ne ya gangaro daga goshin kadir ya dago jajayen idanuwansa ya kalli Asim din ya bude baki yace
'Mummunan guba ta shayar da sultan gatanan a tsaye,
Ko dana iso tana tsaye a kansa tana kokarin qarasa shi da hannuwanta bayan da bakinta tana fadar idan gubar bata kashesa ba zata qarasa shi da hannuwanta....'