← Book details Hayateem Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 102 OF 112

Sashe 102

Hayateem Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Daga kan takunta daya tsaya ya dauke idanuwansa yana dawowa dasu akan fuskanta cikeda nutsuwa da kewa da wata irin kauna me tsafta da karfi ya kalli fuskanta dukkanin jikinsa na mutuwa.

Takowa taci gaba dayi ta iso har inda yake zaune tsakiyar gadonsa yana kallanta ta zauna a cikin nutsuwa tareda kallansa tana bayyanarda dukkanin kulawa da tausayi da alhininta ta fara yi masa gaisuwan rashin haile kafin ta tambayi jikinsa tana dora hannunta daya akan nasa daya bude mata alaman ta saka nata akai.

Hade tafin hannunsu yayi a cikin nutsuwa yana sarqe yatsun hannunsu ya sauke ajiyan zuciya me zafi da radadin abubuwa da dama ciki hadda na rashin uwar yayansa matarsa ta farko.

Amsata yayi batareda doguwan hayaniya ko motsiba daganan sukai shiru kafin ya sake tambayansa yanayin yanda yake ji a yanzu yana bata amsa tana dubasa a natse damuwanta na bayyanuwa.

Ganin halin datake neman shiga na damuwa me yawa na gani wheelchair a dakin ya sakasa janta jikinsa ahakali ya rumgume batareda yace komaiba sbd shirun yake buqata a yanzu.

Lafewa tayi itama tana dauke numfashi dan basa nutsuwa da shirun dayake buqatan.

Haka sukai shiru babu motsi ko kalman komai a hakan suka kwana.

Washe gari bata bar bangarenba saida tai masa komai da kanta ta basa breakfast ta basa magani tana nan dr yazo ya dubasa ya sake mata bayanan komai wanda hankalinta ya kwanta dan haka ta sake basa kulawa sosai dakyau tukuna saida NUAB yaxo anan bangaren suka gaisa a palon Sultan din itace ta turosa a kujeransa har palon suka gaisa da NUAB daga nan ta fice ta basu guri suna magana akan likitocin da aka gayyato daga wata qasar dan dubasa amma an riga an musu komai na anjom zasu samesa gashi kuma Ammin ta baro anjom tazo dan haka dole dai komawan zaayi acan anjom ayi jinyar inda babu ko yan dubiya ko kadan ya samu yayi jinyar nutsuwa.

Sai anyi sati daya da rasuwan haile kowa ya watse tumuna sultan din zai tafi dan haka kulawa dashi kwata kwata ya dawo hannun Ammin wadda a yanxu saita kwana ta wuni batama baro bangarensa ba sedai kullum tana zuwa ta gaida mahaifiyar haile ta sake musu gaisuwa musamman Asim da suke nuna masa wata irin kauna da kulawa sosai dan kuwa ko abincin da zaici daga bangaren Ammin tenya takeyi da kanta tana aika masa acan bangaren wani lokacin ma anan bangaren yake cin abinci da Leylah sun taru sun tsayu akansa sbd kada ya shiga damuwa yana samun kulawan dama bai samu ba a baya rayuwansa dan kuwa kai tsaye kaman NUAB suke jinsa yanzu.

Da daddare Aleey ya gama hada bayanan umarnin LEUL din kuma yayi magana da likitocin amma bai buqaci jin komaiba da kansa sbd yana kiyaye huruminda iya na ubangidansa ne kadai dan haka jin menene yake damun queen din boyem iya gurin me boyem dinne.

Saida suka gama komai Sun iso palon bangaren NUAB din aleey ya kallesa yana daga gefensa cikin girmamaw ya sanar dashi yayi magana da likitocin kuma dukansu suna jiran kiransa kowane lokaci.

Sofa ya nufa yana zaunawa tareda fasa shigewa yana dagowa ya kalli aleey din yace ya kirasu yanzu yaji.

Biyosa aleey yayi yana saka kiran dr Ibrahim wanda shine babba yana dauka ya miqawa NUAB din wayar cikin nutsuwa da girmamawa.

Amsar wayar yayi yana dorawa akan kunnensa take dr Ibrahim ya bude baki ya fara miqo gaisuwansa cikin zallan girmamawa da nutsuwa.

A taqaice NUAB ya amsa yana buqatan bayanin komai a yanda yake na abinda yake damun princess din ghaz.

Shiru dr Ibrahim ya danyi sbd Ammin data ce bata son kowa yasan da cikin da zubewan daya tashi yi amma kuma babu ta yanda zaayi ya kasa amsa tambayar sultan din gabaki daya da kansa dan haka numfashi ya sauke yana farawa da neman afuwan Sultan din akan rashin fadarsu da kuma jajanta masa akan abinda ya kusan faruwan tukuna ya fada masa miscarriage Bahar ta kusan samu amma dai cikin ya tsaya yanxu....

Dagowa da idanuwansa da girmansu da haskensu da wani irin kwarjininsu tareda abinda aleey ya gani cikinsu ya kalli aleey din wanda zuciyarsa ta girgiza da karfi sbd kallan yana bayyanarda dukkanin tashin hankalin da ido zai iya bayyanawa.

Bude baki yayi cikin sauti me dauke da tsantsar nutsuwa data shigesa ta kai tsaye akan abinda kunnuwansa suke ji masa da yama kasa ganewa yacewa Aleey

'Wat does miscarriage mean??

Kallansa aleey yayi shima yana rikicewa da amsar dazai bada sbd bace masa kalman tayi take a cikin kai dan haka ya fara kokarin daga wayarsa yana kokarin budewa yana son tabbatarda abinda ya tina da maanar kalman.

A cikin wayar dr Ibrahim ya sake tattaro nutsuwansa yace

'Ranka ya dade miscarriage na nufin zubewan sabon ciki a jikin mace ko fitarsa'

Dawo da hankalinsa yai duka kaf akan dr Ibrahim din yace

'Cikin ne a jikin Ayanaah BAHAR??
And maganar nan da kake fadamun yanzu cikin ya fita kenan daga jikinta??
Are you like for real ko me?

Qarasa rikicewa Aleey yake neman yi yana fasa bude wayarsa jin abinda LEUL ke fada,

Dr Ibrahim cikin sauri da kokarin qarasa bayaninsa cikin nutsuwa ya sanar dashi cikin bai fita ba allah ya basu ikon tsaidasa dan haka.......

Ko gama sauraron kalamansa NUAB baiyiba ya datse wayar yana jefarwa gefensa tareda rufe idanuwansa da suka sauya a take,

Su Ammi kuwa sun san me sukai na boye masa Bahar na dauke da cikinsa?
Sun san me sukai na hana ya sani?
Da cikin ya fita shikenan ya shiga ya fita bai saniba a matsayinsa na ubansa ko me?

Gashin jikinsa ne suka miqe gabaki daya cikin wani irin yanayin dayake jin jikinsa duka yana zafi kaman wutar zazzabi ta dokesa a take.

A hakan ma suna nufin bazaa sanar dashi ba har sai Bahar din tayi ciwon ta warke,
A hakan ana nufin dai yaushe zaa sanar masa?

Rintse idanuwansa yayi da har sun dan fara masa radadi ya dauki mintina a hakan zuciyarsa na shiga fargaban da bai taba samun kansa a cikinta ba sai a lokacinda yaga sultan a kwance cikin halin mutuwa ko rai a gabansa sai yanzu dayake jin fargaban me yawa tana shigarsa na abinda yaji.

Bude idanuwansa yayi ya kalli Aleey da
Yake tsaye cikin shirin jiran kowane irin umarninsa,

Kallonsa yayi ya dauke kai yana bude baki yace

'Ina buqatan ganinta da kaina tareda likitocin dana yadda dasu akan wannan'

'Aiit Sir' Aleey ya fada kai tsaye yana juyawa yabar palon shima yanajin wani irin karfi da zimmar dole ya hada kan manyan likitocinsu dan zuwa duba cikakkiyar lafiyan Magajin boyem,Moscow da ghaz.

Yana ficewa shima miqewa yayi kai tsaye yana wucewa ciki tareda saka kiran wayarta tana dauka saukan sautin muryanta kadai yaji a kunnuwansa yaji ya qarasa rasa nutsuwansa idan ba isa yayi gareta ba ya duba lafiyanta data jininsa dabai san dashiba dayake cikinta yana rasa yama yakeji a zuciyarsa.

Aleey kuwa kai tsaye tin a cikin daren ya fara shirin tafiyan likitan dazasu dashi sbd ba buqatan jiran komai bayan tafiyar.

Washe gari babu wanda ma ya samu ganinsa kaf har iyayensa kuwa dan sedai ta waya yayi magana dasu yaji ya jikin Sultan din,

Baicewa Ammi komaiba hatta ita Bahar din baice mata komai ba akan cikin kawai ganinta yake mutuwan son yi.

Cikin nutsuwa da kulawa sukai wayarsu suka gama bai nuna mata komaiba sbd kadama ta shiga damuwan dazata sake taba lafiyansu.

A cikin kwanaki biyu Aleey ya gama hada tafiyarsu wadda ba wanda ya sani bayan likita da aka sanar,

Ammi sosai take kulawa da sultan itama duk da hankalinta yana rabuwa sosai rabi akan Bahar da cikinta datake jin kaman ta daukota ta dawo da ita nan gabanta amma kuma bazata iya daukan risk na doguwar tafiya ga Bahar din ba ya sakata ta daure kawai tinda Sakinah kaman itace tana can tana kulawa da bahar kaman zata tayata renan cikin a jikinta.

Ana adduar kwana biyar iyayen haile zuka wucewansa tareda duka sauran yayan Nysah aka bar Nysah din kawai sai daga baya sbd baa zaman gaisuwan komai iya sune kadai a zaune koyaushe cikin kunci da damuwa bama kaman Aslam da meryam da zaa bari su kadai gwanin tausayi ba kowa a tareda su sai bayinsu da zasuyi rayu dasu,

Ga dukiya da daula da dukkanin jin dadin duniya da tarin arziki me yawa gaba da baya amma ba farin ciki ko kadan ba uwa ba miji ba uba sbd har lokacin babu kauna ko kulawa sosai a tsakanin sultan dasu duk da kullum suna bin Nysah da Asim gurin dubasa da gaidasa amma kulawansa da tsantsar kaunarsa tana bayyane ne akan Asim da nysah dan haka duk suka sake shiga damuwa da zama kalan tausayi.

Ranar da akai sati da rasuwan a ranar bayan addua da yamma da daddare Jirgin NUAB zai tashi dan haka a daren yayi bankwana da iyayensa yayi tafiya me mahimmanci abinda kawai ya fada musu.

Bayan tafiyarsa masarautar ta sake sanyi sbd me ita baya nan yayi tafiya sai kuma ya dawo.
#MAMUH
09033181070
[16/01, 5:31 pm] Dasoo: HAYATEEM
Mamuhgee

176
Bayan tafiyar NUAB washe gari itama Nysah ta tattara ta koma bayan da ita da Asim harma da Ayanah sun taru sun rokarwa su Aslam yafiya da afuwan Sultan ya kuma sauko ya yafe musu.

Nysah na wucewa shirin tafiya umrah suma suka fara su biyun dan suna buqatan dan tafiya kansu ya sake warwarewa ko zasu dawo ma sai angama bikin kadir da sakinah da aka daga dole sai nan da wani watan sati hudu dai masu zuwa kenan.

Asim ya san da cikinsa da leylah shima take dauke dashi bayan datai rashin lafiyan wuni daya na rashin hutu da kwanciyan hankalin da sukaita fama dashi a kwanakin.

Farin cikin farko kenan daya iya shigarsa bayan rasuwan mahaifiyarsa dan kuwa ya tabbatarda data raye zatafi kowa farin cikin ganin 'dansa.
Chapter 102 · 0% Book details