Sashe 1
Hayateem Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
HAYATEEM part 2
[12/01, 10:49 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_*
Mamuhgee
71
Ruwan wanka me tsafta,qamshi da dumi aka hada mata Maa sakinah ta taimaka mata har bakin toilet din ta shigar da ita ta Baro bathroom din ta kalli Salmah tace ta taimaka mata gurin tubewa da nuna mata komai.
Salmah ce ta shiga har ciki ta taimaka mata sosai a gurin nuna mata komai da sabulun da zatai wanka dashi me qamshi da kyau da tsada tukuna taje ta kawo mata towels har guda biyu masu dan girma kafin ta fice dan zuwa hado mata abincin da Maa tace a hado mata.
Duk da baa irin wannan daular da duniyar ta tashi ba batada duhun kai dan haka a sanyaye tayi wankan ta fito tareda alwala tana daure da towel daya ta rifo jikinta da Wani Dayan gashinta dayake a sake har lokacin duk ya dan jiqe.
Tana qarasowa Maa sakinah ta miqe ta kamota ta zaunar a gaban mirror tana goge mata fatar jikinta da towel din cikin kulawa tareda bude baki a sanyaye da nutsuwa tace
‘BAHAR,Bahar kiyi hakuri ki zama me tawakkali da karban kaddarar ubangiji a dik yanda tazo miki,
Mahaifinki bake kadaice kikai rashinsa ba Muma mun rasa Wani bangare ne na jikin mu rashinsa a wannan duniyar,
Muna tsananin kaunarsa fiyeda kanmu amma Allah baiyi zamu sake cigaba da rayuwa ba ya rabamu dashi a daidai lokacinda muke saka ran mun sake haduwa,
Addua da dangana itace kadai abinda zaki sakawa iyayenki dashi,
Karki manta dangana da hakurin da zakiyi shine zai baki kwarin gwiwa da nutsuwar yi musu addua da fatar rahamar ubangiji ako da Yaushe dan haka a yanzu sassautawa zuciyarki kada ki saka quncin dazai hanaki ringa aika musu adduar ki ako yaushe,
Anan cikinmu kinsani rayuwar gata da kauna zakiyi sbd muna tsananin so da kaunarki,
Ki saka a ranki cewa ke din hasken rayuwa da idaniyar mu ce koda baki ga hakan daga kowa ba a yanzu zaki gani daga gareni kafin yan uwan mahaifinki susanki susan ke wacece,
Ke Amanata ce da zan bawa kowace irin kauna da kariya da karfina da rayuwata,
Ke hasken idaniyata ce da zuciyata Bahar ki Bari na kaunaceki kaman nice na haifeki da cikina idan har kika sassautawa zuciyarki banason ganinki a wannan yanayin.’
Qarasa maganar tayi tana goge mata kyakkyawar fuskarta me daukan ido sbd bata shiga rana Sam a cikin duhun masarautar GHAZ ta tashi ta rayu ta kuma girma da towel tana daukan body oil na Neutrogena tana shafa mata a jikinta cikin kulawa da gata.
Tana gama shafa mata ta Kama gashinta dan busar mata dashi inda yake a jiqe kafin ta Kama mata shi ba sosai ba da band.
Babu Kayan da zata bata tasaka sbd kayansu bazasu mata ba su manya ne ita kuma budurwa ce me qaramin jiki hakama batada ikon bata wasu kayan ta saka idan ba Wanda duk Wanda baida matsayi yake sakawa ba a masarautar dan haka rigarta me tsayi ta bata hakanan ta saka tukuna ta tashi tafara sallah ita kuma ta fada toilet dan wanka da sallah.
Sallolin dake kanta tafara jerowa a hankali harta kammala ta daga hannu zata fara addua kawai Wani irin kuka me tsananin karfin daya ratsa zuciyarta data qame jin Wani irin azababben radadi na ratsata ya kubce mata ta cusa fuskarta a tafin hannuwan tana wata irin jijjiga kukan na tsananta sbd ta tabbata dai ta rasa mahaifinta dashi kadai ne ya rage mata,ta rasa Abaa dinta sai lahira,
Ta rasa rayuwarta,ta rasa haskenta,ta rasa hope da kuzarin da shi kadai gareta a dare daya,
Abaa ya tafi yabarta a duniyar da batasan komai da kowaba idan bashi ba gashi ta tsinci kanta a inda batajin zata iya rayuwa.
Kuka takeyi sosai mai tsima zuciya da tada tsigar jiki tana jin kirjinta na mata Wani tsananin ciwon da kaman gangar jikinta bazata daukaba.
Maa dake toilet tana jinta tayi shiru jikinta na mutuwa da tsananin tausayinta da jin kaman ta zare kuncin Bahar din ta dawo dashi kanta sbd yarinyar ta samu sassauci da nutsuwan zuciyar da bata taba samuba.
Kasa fitowa Maa tayi ko bayan data gama komai sbd bawa Bahar din damar fidda kukan quncin dayake zuciyarta tin jiyan da mahaifinta ya bar duniya.
Sai Bayan mintina masu tsayi ta fito itama idanuwanta jajir ta zauna ta shirya tana gamawa gefen Bahar din tazo ta tada tata sallar a natse.
Shiru Bahar din take Zaune idanuwanta sunyi jajir sun kumbura hancinta ma yayi jajir sbd kuka ta samu dan sassaucin nauyin daya danne kirjinta ta Lumshe idanuwa tareda kwantar da kanta a hannun couch din dayake gefenta.
Maa ma tana gama sallar aka fara shigowa da abinci aka a gabansu nan qasa kan carpet din dasuke,
Kallan Bahar Maa tayi tana zuba mata abincin Wanda yake lafiyayye da vegetables tareda fruits da madara me Zafi da zuma tace
‘Bahar kici abinci kinji’
Bude idanuwanta tayi ahankali cikin sanyi tareda tasowa daga kwancen da kanta yake sbd Sam rayuwarta bata iya gaddama da hayaniya ba dan haka bazata iya tsayawa cewa aa ba Maa din taci gaba da rokonta ya zamansa anyi hayaniyar hakan dan haka kai tsaye juyowa tayi jiki a mace tareda dago manyan idonta da sukai ja ta kalli Maa sakina a sanyaye.
Jin dadi Maa tayi har cikin zuciyarta na yanda Bahar din batai mata gardama ba dan haka apple tafara yanke mata fatar ta bata kafin ta zuba mata abincin jikinta har rawa yakeyi sbd sauri Wanda ya saka Bahar ta zuba mata ido tana kallanta tausayinta na shigarta dan haka takai apple din bakinta ta fara ci ahankali.
Abincin ma a bakinta Maa sakina a ringa bata har taci bada yawa ba
Maa ta dauki madarar me Zafi ta bata Tasha itama kafin itama taci abincin a natse tana gamawa aka fice da kayan.
Sallar ishai da akai ne ya sakasu miqewa suka gabatar da sallar a tare,
Suna gamawa sukai shiru a Zaune babu me cewa komai har tsawon sama da awa daya zuwa lokacin Wani gajiyayyen baccin dole ya dauke Bahar a gurin sbd maganin dayake cikin madarar na saka bacci sbd zuciya da kwakwalwanta su samu hutawa daga qunci idan ta farka zata ji sassaucin komai insh Allah.
Salmah ta kira ta Kama mata ita suka kwantar da ita a lafiyayyan gadon dakin Maa ta rufeta da bargo me tsananin Laushi ta zauna gefen gadon ta tofa mata addua tukuna ta miqe ta fice daga dakin dan waya da tenya data kirata tana sallah.
Palo ta dawo ta zauna a natse ta saka kiran tenya din wadda tariga ta Baro asibiti itama ta dawo masaukinsu.
Waya sukai sosai tsawon lokaci Akan yanayin jikin Ayanaah har suka gama ko kadan Maa sakinah bata fada komai daya danganci Abaas bama bare rasuwarsa bare ma azo kan Bahar wadda zata rayu a hannunsu tamkar matsayin baiwar masarautar sbd kawar da kowace irin zargi da bincike akanta dan haka kafin ma su dawo zata kula da ita da bata kauna tareda tattali.
Suna gama wayar Zaunawa tayi na dan lokaci tana duba abubuwa a wayarta kafin ta tashi ta koma dakin tayi abinda zatai ta kwanta Dayan gefen gadon cikin nutsuwa tana kallan fuskar Bahar dake bacci sosai a cikin sanyi da nutsuwa.
****Washe gari da safe da dan sassaucin data tsammata Bahar ta tashi dan haka taji itama ta sake samun nutsuwa,
Breakfast sukai a tare kaman jiyan a bakinta ta bata kafin ta hada mata ruwan wanka da kanta wannan karanma itace ta taya Bahar din ta wanke matan kanta tas Wanda yayi qura kafin ta fito tabarta tayi wanka ta fito.
Busar mata da gashinta tayi ta sake bata rigarta ta saka wadda tayi mugun yi mata yawan gaske amma tinda babu inda zata fita hakan ba damuwa bane.
Shiru suka wuni tsit babu dogon motsin komai sbd Sam Bahar bata iya maganar komai idanuwanta koyaushe a guri daya suke tsayawa da tinani Wanda hakanne yake saka Maa sakinah damuwa dan haka tafara kokarin ajiye tata damuwan tana Janta a jikinta sosai tareda ringa mata hirar mahaifinta tin yana yaronsa.
Da wannan tafara saka Bahar din ringa bata dukkanin hankalinta sbd koyaushe hirar mahaifinta idan zaa wuni a kwana Ana mata baa gajiya dan haka tafara sabawa ahankali ahankali da hirar Maa sakinah wadda ta dage sosai da nunawa Bahar menene kauna da walwala.
Kullum tana waya da tenya taji yaya jikin Ayanah wadda ayanzu ake maganar sati uku da rasuwar Abaas din amma bata farfado ba.
******lokaci da kwanaki sosai sun tafi Wanda ya saka kauna me sanyi da sabo tareda yar shaquwa shiga tsakanin Bahar da Maa sakinah wadda ta fara kawo wata rayuwar cikin matacciyar rayuwarta datake ganin bazata taba gyaruwa ba.
Maa sakinah ta sakata bude mata zuciyarta datake a kulle ta shige sbd itace mutum ta farko dataji tana yiwa kauna da shaquwa Bayan mahaifinta kaf duniyarta sai kuma Salmah wadda itama take kulawa sosai da ita tana hayata hira da labarai bisa umarnin Maa sbd Bahar din na buqatan sabawa da mutane.
Farin ciki ne ya cike rayuwar Maa ganin Bahar din tafara kokarin fuskantar rayuwa harma tana zuwa kitchen tareda Salmah sbd tayata ayyukan dasuke yi tareda Sauran bayin bangaren na wishmah hakama tana mata magana yanzu sosai.
Ana cikin wannan halin na farin cikin da Maa sakinah ke yi kwatsam kiran tenya ya shigo mata tareda albishir me dadin cewa Ayanah ta farfado hakama tareda cikakkiyar lafiyayyar memory dinta kawai Sauran rashin karfin jiki ne data rasa ya rage mata Wanda shima insha Allah tana qarasa warware wa zasu dawo gabaki dayansu kowane lokaci.
#MAMUH
KUYI HAKURI MASOYAN ABAAS DA MASU GANIN KASHE KASHEN YAYI YAWA WANDA BANAJIN KUN FAHIMCENI KO KUN FAHIMCI LABARIN,
Amma dai koma yayane ina Bau hakuri tareda miqo taaziyata gareku Allah yaji qansa ya huci zuciyarku kunji Rabin ran Mamuh🙏💋
HAYATEEM
by
Mamuhgee
700
0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi
09033181070
Yan Nijar kuma
89825722
Depot my nita
Nissaiba laouali
[12/01, 10:49 am] Asia ahmd: _*HAYATEEM*_
Mamuhgee
[12/01, 10:49 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_*
Mamuhgee
71
Ruwan wanka me tsafta,qamshi da dumi aka hada mata Maa sakinah ta taimaka mata har bakin toilet din ta shigar da ita ta Baro bathroom din ta kalli Salmah tace ta taimaka mata gurin tubewa da nuna mata komai.
Salmah ce ta shiga har ciki ta taimaka mata sosai a gurin nuna mata komai da sabulun da zatai wanka dashi me qamshi da kyau da tsada tukuna taje ta kawo mata towels har guda biyu masu dan girma kafin ta fice dan zuwa hado mata abincin da Maa tace a hado mata.
Duk da baa irin wannan daular da duniyar ta tashi ba batada duhun kai dan haka a sanyaye tayi wankan ta fito tareda alwala tana daure da towel daya ta rifo jikinta da Wani Dayan gashinta dayake a sake har lokacin duk ya dan jiqe.
Tana qarasowa Maa sakinah ta miqe ta kamota ta zaunar a gaban mirror tana goge mata fatar jikinta da towel din cikin kulawa tareda bude baki a sanyaye da nutsuwa tace
‘BAHAR,Bahar kiyi hakuri ki zama me tawakkali da karban kaddarar ubangiji a dik yanda tazo miki,
Mahaifinki bake kadaice kikai rashinsa ba Muma mun rasa Wani bangare ne na jikin mu rashinsa a wannan duniyar,
Muna tsananin kaunarsa fiyeda kanmu amma Allah baiyi zamu sake cigaba da rayuwa ba ya rabamu dashi a daidai lokacinda muke saka ran mun sake haduwa,
Addua da dangana itace kadai abinda zaki sakawa iyayenki dashi,
Karki manta dangana da hakurin da zakiyi shine zai baki kwarin gwiwa da nutsuwar yi musu addua da fatar rahamar ubangiji ako da Yaushe dan haka a yanzu sassautawa zuciyarki kada ki saka quncin dazai hanaki ringa aika musu adduar ki ako yaushe,
Anan cikinmu kinsani rayuwar gata da kauna zakiyi sbd muna tsananin so da kaunarki,
Ki saka a ranki cewa ke din hasken rayuwa da idaniyar mu ce koda baki ga hakan daga kowa ba a yanzu zaki gani daga gareni kafin yan uwan mahaifinki susanki susan ke wacece,
Ke Amanata ce da zan bawa kowace irin kauna da kariya da karfina da rayuwata,
Ke hasken idaniyata ce da zuciyata Bahar ki Bari na kaunaceki kaman nice na haifeki da cikina idan har kika sassautawa zuciyarki banason ganinki a wannan yanayin.’
Qarasa maganar tayi tana goge mata kyakkyawar fuskarta me daukan ido sbd bata shiga rana Sam a cikin duhun masarautar GHAZ ta tashi ta rayu ta kuma girma da towel tana daukan body oil na Neutrogena tana shafa mata a jikinta cikin kulawa da gata.
Tana gama shafa mata ta Kama gashinta dan busar mata dashi inda yake a jiqe kafin ta Kama mata shi ba sosai ba da band.
Babu Kayan da zata bata tasaka sbd kayansu bazasu mata ba su manya ne ita kuma budurwa ce me qaramin jiki hakama batada ikon bata wasu kayan ta saka idan ba Wanda duk Wanda baida matsayi yake sakawa ba a masarautar dan haka rigarta me tsayi ta bata hakanan ta saka tukuna ta tashi tafara sallah ita kuma ta fada toilet dan wanka da sallah.
Sallolin dake kanta tafara jerowa a hankali harta kammala ta daga hannu zata fara addua kawai Wani irin kuka me tsananin karfin daya ratsa zuciyarta data qame jin Wani irin azababben radadi na ratsata ya kubce mata ta cusa fuskarta a tafin hannuwan tana wata irin jijjiga kukan na tsananta sbd ta tabbata dai ta rasa mahaifinta dashi kadai ne ya rage mata,ta rasa Abaa dinta sai lahira,
Ta rasa rayuwarta,ta rasa haskenta,ta rasa hope da kuzarin da shi kadai gareta a dare daya,
Abaa ya tafi yabarta a duniyar da batasan komai da kowaba idan bashi ba gashi ta tsinci kanta a inda batajin zata iya rayuwa.
Kuka takeyi sosai mai tsima zuciya da tada tsigar jiki tana jin kirjinta na mata Wani tsananin ciwon da kaman gangar jikinta bazata daukaba.
Maa dake toilet tana jinta tayi shiru jikinta na mutuwa da tsananin tausayinta da jin kaman ta zare kuncin Bahar din ta dawo dashi kanta sbd yarinyar ta samu sassauci da nutsuwan zuciyar da bata taba samuba.
Kasa fitowa Maa tayi ko bayan data gama komai sbd bawa Bahar din damar fidda kukan quncin dayake zuciyarta tin jiyan da mahaifinta ya bar duniya.
Sai Bayan mintina masu tsayi ta fito itama idanuwanta jajir ta zauna ta shirya tana gamawa gefen Bahar din tazo ta tada tata sallar a natse.
Shiru Bahar din take Zaune idanuwanta sunyi jajir sun kumbura hancinta ma yayi jajir sbd kuka ta samu dan sassaucin nauyin daya danne kirjinta ta Lumshe idanuwa tareda kwantar da kanta a hannun couch din dayake gefenta.
Maa ma tana gama sallar aka fara shigowa da abinci aka a gabansu nan qasa kan carpet din dasuke,
Kallan Bahar Maa tayi tana zuba mata abincin Wanda yake lafiyayye da vegetables tareda fruits da madara me Zafi da zuma tace
‘Bahar kici abinci kinji’
Bude idanuwanta tayi ahankali cikin sanyi tareda tasowa daga kwancen da kanta yake sbd Sam rayuwarta bata iya gaddama da hayaniya ba dan haka bazata iya tsayawa cewa aa ba Maa din taci gaba da rokonta ya zamansa anyi hayaniyar hakan dan haka kai tsaye juyowa tayi jiki a mace tareda dago manyan idonta da sukai ja ta kalli Maa sakina a sanyaye.
Jin dadi Maa tayi har cikin zuciyarta na yanda Bahar din batai mata gardama ba dan haka apple tafara yanke mata fatar ta bata kafin ta zuba mata abincin jikinta har rawa yakeyi sbd sauri Wanda ya saka Bahar ta zuba mata ido tana kallanta tausayinta na shigarta dan haka takai apple din bakinta ta fara ci ahankali.
Abincin ma a bakinta Maa sakina a ringa bata har taci bada yawa ba
Maa ta dauki madarar me Zafi ta bata Tasha itama kafin itama taci abincin a natse tana gamawa aka fice da kayan.
Sallar ishai da akai ne ya sakasu miqewa suka gabatar da sallar a tare,
Suna gamawa sukai shiru a Zaune babu me cewa komai har tsawon sama da awa daya zuwa lokacin Wani gajiyayyen baccin dole ya dauke Bahar a gurin sbd maganin dayake cikin madarar na saka bacci sbd zuciya da kwakwalwanta su samu hutawa daga qunci idan ta farka zata ji sassaucin komai insh Allah.
Salmah ta kira ta Kama mata ita suka kwantar da ita a lafiyayyan gadon dakin Maa ta rufeta da bargo me tsananin Laushi ta zauna gefen gadon ta tofa mata addua tukuna ta miqe ta fice daga dakin dan waya da tenya data kirata tana sallah.
Palo ta dawo ta zauna a natse ta saka kiran tenya din wadda tariga ta Baro asibiti itama ta dawo masaukinsu.
Waya sukai sosai tsawon lokaci Akan yanayin jikin Ayanaah har suka gama ko kadan Maa sakinah bata fada komai daya danganci Abaas bama bare rasuwarsa bare ma azo kan Bahar wadda zata rayu a hannunsu tamkar matsayin baiwar masarautar sbd kawar da kowace irin zargi da bincike akanta dan haka kafin ma su dawo zata kula da ita da bata kauna tareda tattali.
Suna gama wayar Zaunawa tayi na dan lokaci tana duba abubuwa a wayarta kafin ta tashi ta koma dakin tayi abinda zatai ta kwanta Dayan gefen gadon cikin nutsuwa tana kallan fuskar Bahar dake bacci sosai a cikin sanyi da nutsuwa.
****Washe gari da safe da dan sassaucin data tsammata Bahar ta tashi dan haka taji itama ta sake samun nutsuwa,
Breakfast sukai a tare kaman jiyan a bakinta ta bata kafin ta hada mata ruwan wanka da kanta wannan karanma itace ta taya Bahar din ta wanke matan kanta tas Wanda yayi qura kafin ta fito tabarta tayi wanka ta fito.
Busar mata da gashinta tayi ta sake bata rigarta ta saka wadda tayi mugun yi mata yawan gaske amma tinda babu inda zata fita hakan ba damuwa bane.
Shiru suka wuni tsit babu dogon motsin komai sbd Sam Bahar bata iya maganar komai idanuwanta koyaushe a guri daya suke tsayawa da tinani Wanda hakanne yake saka Maa sakinah damuwa dan haka tafara kokarin ajiye tata damuwan tana Janta a jikinta sosai tareda ringa mata hirar mahaifinta tin yana yaronsa.
Da wannan tafara saka Bahar din ringa bata dukkanin hankalinta sbd koyaushe hirar mahaifinta idan zaa wuni a kwana Ana mata baa gajiya dan haka tafara sabawa ahankali ahankali da hirar Maa sakinah wadda ta dage sosai da nunawa Bahar menene kauna da walwala.
Kullum tana waya da tenya taji yaya jikin Ayanah wadda ayanzu ake maganar sati uku da rasuwar Abaas din amma bata farfado ba.
******lokaci da kwanaki sosai sun tafi Wanda ya saka kauna me sanyi da sabo tareda yar shaquwa shiga tsakanin Bahar da Maa sakinah wadda ta fara kawo wata rayuwar cikin matacciyar rayuwarta datake ganin bazata taba gyaruwa ba.
Maa sakinah ta sakata bude mata zuciyarta datake a kulle ta shige sbd itace mutum ta farko dataji tana yiwa kauna da shaquwa Bayan mahaifinta kaf duniyarta sai kuma Salmah wadda itama take kulawa sosai da ita tana hayata hira da labarai bisa umarnin Maa sbd Bahar din na buqatan sabawa da mutane.
Farin ciki ne ya cike rayuwar Maa ganin Bahar din tafara kokarin fuskantar rayuwa harma tana zuwa kitchen tareda Salmah sbd tayata ayyukan dasuke yi tareda Sauran bayin bangaren na wishmah hakama tana mata magana yanzu sosai.
Ana cikin wannan halin na farin cikin da Maa sakinah ke yi kwatsam kiran tenya ya shigo mata tareda albishir me dadin cewa Ayanah ta farfado hakama tareda cikakkiyar lafiyayyar memory dinta kawai Sauran rashin karfin jiki ne data rasa ya rage mata Wanda shima insha Allah tana qarasa warware wa zasu dawo gabaki dayansu kowane lokaci.
#MAMUH
KUYI HAKURI MASOYAN ABAAS DA MASU GANIN KASHE KASHEN YAYI YAWA WANDA BANAJIN KUN FAHIMCENI KO KUN FAHIMCI LABARIN,
Amma dai koma yayane ina Bau hakuri tareda miqo taaziyata gareku Allah yaji qansa ya huci zuciyarku kunji Rabin ran Mamuh🙏💋
HAYATEEM
by
Mamuhgee
700
0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi
09033181070
Yan Nijar kuma
89825722
Depot my nita
Nissaiba laouali
[12/01, 10:49 am] Asia ahmd: _*HAYATEEM*_
Mamuhgee