← Book details Hayateem Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 31 OF 112

Sashe 31

Hayateem Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Motsawa tayi cikin tsananin sanyi tana kokarin zare yatsun hannunta daga nasa sbd yanda qamshinsa yake shigarta sosai ta dago idanuwanta masu sakasa kallanta ta kallesa zatai magana ya matse inda take jin yar zafin ta kallesa da sauri tana bude baki da sauti me tata kamewan tace

'Kada ka manta nan ba bangarenka bane na Ammi ne kuma a dakin Maa.....

Bata qarasa ba ya sake latsa hannun wanda ya sakata yunqurowa da dan karfin daya hade kirjinta da nasa take ya dago idanuwansa ya sauke mata wani kallan daya sakata kokarin yin baya da sauri tana kokarin faduwa ya tarota da cikin sanyi da kamewa tareda dawo da ita jikinsa ta fado kirjinsu ya hade da kyau suna mannuwa da juna ya a jikin madubin.
#MAMUH
09033181070
[12/01, 10:50 am] Asia ahmd: HAYATEEM
Mamuhgee

102
Dago kanta tayi idanuwanta na dan matsewa ta qi yadda ta sake kallansa ta motsa ahankali tana sbd yanda take hade dashi sosai gashi a jikin mirror din suke sosai,

Turesa takeson yi amma yanda suke din hannuwanta ma bazasu iya shiga tsakaninsu ba bare ta iya turesa din dan haka ta daure ta sake dagowa batada xabin daya wuce daga idanuwanta ta saukesu akansa wanda hakan yake jira sbd idanuwansa suna kafe da ita hannunsa daya yana xagaye da ita dayan kuma yana sarqe da yatsun hannunta daya har lokacin.

Kallo daya tayiwa cikin idanuwansa ta cire idonta a cikinsu sbd bazata iyaba bakuma dan komai ba sai dan yanda tsigan jikinta ke tashi daga kallan cikinsu amma bawai dan tsoro ko shakkarsa ba,

Bude baki tayi zatai magana cikin karfin hali da kame fuska maganar Maa ta bayyana daga wajen palon,

Kallan kofar shigowa dakin tayi da sauri kirjinta na bugawa da karfi,

Zamewa tayi kokarin yi amma riqon bame zarewa bane hakama karfinsu ba daya ba duk da ko kwatan rabin karfinsa bai saka ba,

Kallansa tayi cikin ido ta bude baki tace

'Kasan me kakeyi kuwa?

Shigarsa kalman tayi da kyau da kaifi sbd itace kadai take wuce iyakarta gurin fada masa maganar da zata iya zama ajalin wani idan ya fada akansa,

Bai saketa ba ya bude baki yace

'Kinsan waye a gabanki??
Bakinki da kalamanki zasu iya sanadin wainda kike tareda su idan baiyi naki ba akan abinda yake furtawa.....

Turesa take kokarin yi tana dauke kallanta daga kansa da sautin hankali a kwance daga kalamansa da kuma fargaban dawowan maa tace

'A yanzu dai inaga kana buqatar barin dakin nan kafin me shi ta shigo ta sameka a cikinsa sbd......

Bata qarasa ba ya saketa ya juya a natse ya kalli kofar dakin kafin ya kama hannunta ya juya ya nufi kofar da ita zai kira Maa sakinah din ta shigo dakin ta samesa a hakan yanda bahar din take.

Da sauri taso kwacewa amma ya riqeta da kyau yana nufar kofar batareda kunya ko daya ba dan baima santa ba,

Ganin da gaske yakeyi kiran maa din zeyi ta samesu a hakan tinda tasan zai iya a yanda tasan hankalinsa dan haka da sauri suna kaiwa kofar tasha gabansa tareda dafe kofar da bayanta tana hanasa budewa idanuwanta duka biyu akansa tana kallansa da wani irin yanayin jin zafi,

Daga kafafunta ya fara kallanta zuwa samanta yana qarewa lafiyayyan farar fatarta kallo kafin ya tsayar da idanuwansa akan sarkar kafarta asalin farar azurfar data gada ta mahaifiyarta me tsananin sanyin kyau da rashin ado sosai data zauna da kyau a farar kafarta wadda itace abin farko daya fara gani akanta a ranar farko ta haduwansu a duniya a kuma ranar data zama ta farkon ta zama ta aurensa daya doru akanta,

Hannunsa daya ya miqa zai matsar da ita ya bude kofar ta miqa hannunta ta riqe nasa din batareda tinanin komaiba,

Hannunta daya kama nasa ya saukarwa idanuwansa ya kalla dakyau cikin nutsuwa da yanayin da bata iya gane komai akansa kafin ya dago ya zubawa fuskarta idanuwansa da suka jikinta da babu kaya jin wani irin sanyi na feso mata kaman ana watso mata ruwan sanyi.

Sakinsa tayi a hankali tana dauke idanuwanta akansa sbd ganin irin kallan dayake binta dashi ta sake tare kofar tana jinginar da bayanta jikinta tana dannewa idonta na qin kallansa zuciyarta har lokacin bugawa takeyi sbd idan ya kira maa dakin a cikin wannan yanayin datake kuma tareda dashi a dakin bazata iya kallan Maa din ba dan haka gwara tinda tasan sake komawa maa din zatai dauko wasu kayan idan sun sake juyawa sun koma saiya fice ta shirya batareda maa tasan ya shigo dakin ya sameta a hakan ba harma ya shigo an rufe kofa.

Yanda ta tare kofar ya tana dauke kanta daga kallansa ya sakasa rankwafowa sosai yana dafe jikin kofar da ita gabaki daya,

Ba tsammani taji saukan dumin numfashinsa a fatar saman kirjinta da wuyanta har gefen kunnenta wanda ya sakata juyowa da dan sauri sedai fuskarsa na gap da tata ashe take fuskar tasu ta hade hancinsu na haduwa tayiwa qamshinsa da numfashinsa wani shaqa me karfi batareda saninta ba take ta rufe ido tana fidda wani numfashi daya saka kirjinta yin sama tana qanqame hannun kofar ta bayanta da hannunta daya daya tsananin fara rawa.

Nata Numfashin data fitar shima ya shigesa sosai har cikin kansa da kwakwalwansa yaji saida idanuwansa suka nuna hakan dan haka ya dauke idanuwansa daga kanta yana buqatan ficewa sbd abinda yake yawo a cikin kansa da kirjinsa harma da zuciyarsa.

Hannunsa daya ya saka a bayanta ya kama hannun kofar ta sake dora hannunta akai itama tana dagowa ta kallesa idanuwanta suna tausasa da yanayin damuwan halinda zata shiga idan yayi mata hakan sbd maa din na nan har lokacin dan suna jin maganarta kaman waya takeyi.

Kafesa da idanuwanta tayi wanda yanajinsu akansa amma yaqi kallanta dan hakan nada hadari a lokacin dan haka kokarin janyeta yayi dan ficewa yakeson yi kai tsaye a dakin kwata kwata,

Wasu hawaye ne suka ciko idanuwanta ta dan sake dafewa tana kasa dauke idanuwanta akansa ta bude baki cikin wata irin sanyayyar murya me tsananin taushi da magiyar da batada zabi bayan yi tace

'Dan Allah kada ka......

Bata qarasa ba ya riqota gabaki dayanta da hannuwansa biyu ya ciro daga jikin kofar ya maida jikin bango ya jinginar da ita yana dafeta da kirjinsa cikin wata irin yanayin daya sakata rintse ido zuciyarta na harbawa da karfi ta qanqame hannuwansa batareda ta sani ba sbd tinanin jefar da ita zaiyi.

Numfashinsa ne me tsananin dumi yake sauka a fatar fuskarta da wuyanta sbd fuskarsa dake hade da tata fatarsu na gogan juna da jin dumin fatan tana rata dayan fatar.

Kirjinsa dayake hade da nata ya saka numfashinta sauyawa yana fita daqyar dan haka itama kai tsaye nata Numfashin saukar masa yayi a gefen kunnensa wanda take ya saka fuskarsa gabaki daya fara yin jan daya sakasa sakinta kai tsaye batareda ya juyoba ya bude dakin ya fice.

Yana fita kai tsaye barin bangaren yayi sbd babu wanda zai gani a yanayin da fuskarsa din take.

Yana fitowa Maa sakinah data san yana bangaren sbd taga aleey shiyasa ma taqi shiga ta qirqiri wani aikin tinda sai angama juye wancan din kafin su sake komawa.

Ganinsa babu rahama a fuskarsa hakama baida Alama ko fuskar magana da kowa ko tsayawa ya sakata bata ma fito daga kitchen din datake hangosa ba ta kyalesa.

Aleey ma na ganinsa kai tsaye ya sauke kai suna bin bayansa ba kalma ko daya data fita.

Aleey daya samu labarin Sultan me murabus Yasar yabar qasar tareda Ammi a ranar hakama ya fitar da Haile da yayanta duka daga boyem sun daga zuwa wata qasar da bai gama tabbatarwa ba tukuna, yana son sanarwa Sultan LEUL din amma ganin yanayinsa ya sakasa shiru tukuna sbd labarin zai tada fushinsa me tsananin gaske dan kuwa a yanzu dayake sultan me mulkin boyem shine yakeda cikakken ikon mahaifiyarsa fiyeda sultan yasar sbd babu igiyoyin aure a tsakaninsu dan haka baida cikakken ikonta duk da tana matsayin wishmah dinsa a yanzu shi danta dayake sultan ma zai iya sauketa matsayin ya kuma yiwa sultan yasar iyaka da ita wannan haka yake dan a yanzu duk abinda sultan yake nema a gareta saida izini da umarnin 'dan SULTAN LEUL NUAB wanda zamowansa sultan duka ya basa wannan ikon akan uwarsa da batada iko da yancin kanta a masarautar har yanzu,
Duka hakan ya sake tabbatuwa ne sbd ta kasance mahaifiyar Sarki me mulki a yanzu dan haka bazaayi ikonta a matsayin imebēti ko wishmah ba darajarta ta uwar boyem ce gabaki daya,
A yanzu itace uwa mafi daraja a kaf boyem sbd itace uwar me mulkin.

Bayan isowansu bangaren NUAB da aleey dake bayansa ne kadai suka shige palon sa na farko,

Tsayawa aleey yayi daga bayansa bayan ya zauna ya dan sassauta tareda tausasa sautinsa yace

'Sultan me murabus baya qasar baifi awanni hudu da dagawaba shi da Ammi wanda a lissafin dana dora tafiyar ina kyautata zaton Anjom zai tafi da ita wanda kuma hakan na nufin yasan komai akanta da 'yan uwanta a cikin video din Abaas......

Wani daci da radadin zuciya me zafin gaske ne ya ratso tin daga kansa zuwa zuciyarsa ya dago idanuwansa da har lokacin basu dawo daidai ba bacin rai na qarasa sauyasu yace

'Tayaya yasan da video din Abaas??

Dan sake sauke numfashi aleey yayi yace

'Shine ya wuni tareda ita jiyan a lokacinda take cikin halin sanin rasuwar har dare yana bangaren'

Kafe Aleey din yayi da idanuwansa yana kallo take aleey yayi qasa da nasa idanuwan sbd yasan yayi kuskuren rashin fada masa tin jiyan wanda shi kuwa yayi hakan ne sbd NUAB din bazai taba iya ganin kuka da dacin zuciyar mahaifiyarsa ba shi kuwa Sultan zai iya tsayawa ya hadiye kowane irin baqin cikinta da kukanta dan dole itama a wannan lokacin tana buqatan daya daga cikinsu biyun ko 'danta ko sultan din su kasance da ita.
Chapter 31 · 0% Book details