← Book details Kibiyar Ajali Part 1 And 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 6 OF 114

Sashe 6

Kibiyar Ajali Part 1 And 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

“Amma wannan yarinya ko yar bankadaddiya. Abincin Mudikallen zan baki ku cinye keda yuyar kawayen ki? Nace abincin Mudikallen? Zaki magana ko sai na lakada miki na jaki?”

Ruwan ciki na ta hau bugu tana yakushi na. Takaici da zugin da ciki na yake yasa na fara kuka mai kara, Cikin haka ‘Dara’ifa makociyar mu ta shigo da alamun kuka na ne ya kawota. Dakyar ta banbare Gajiyalle daga jiki na,

“Haba Gaji! Haba! Kashe ta zaki yi? Yarinya kamar wannen fisabilillahi ya za’ai ki dinga hayewa ruwan cikin ta kina duka? Tsakani fa da Allah. Shi fa da na kowa ne Gajiyalle, Idan ka kyautata wa dan wani sai a kyautatawa naka kai ma. Marainiya c...”

“Ishiru dakata, dakata min ‘Dara’ifa, kefa dama akwai ki da shisshigi da gutsiri tsoma, Ina ruwan ki? Dan tsabar tsagwaran gulma irin ta ki menene na shiga abinda babu ruwan ki? Shysa akeyi dake a garin nan.. Kinsan meta min ne da zakizo kina min wa’azi?”

Dara’ifa ta girgiza kai cikin takaici tace,

“Koma meta miki Gaji sai ki hak’uri, Amma akan me zaki dinga dukan ta kamar kinsamu katako? ‘Ya mace kamar wannan da zaki kyautata mata bafa kisan inda rana zata fa’di ba. Shi maraya kokarin kyautata masa kake ba kuntata masa ba.”

“Yau za’ai tsallen badake. Abincin Mudikalle na fa mumugunciyar yarinyar nan ta kaiwa kawayenta suka cinye. Tafa tambaye ni nasa ne? Na daga mata kai alamun eh amman yarinyar nan dake ba tsoron Allah a ranta sai tai mirsisi takai musu suka cinye.”

Ina daga kwance na mike dakyar saboda yadda jiki na ke tsamin jibgar da tamin.

“Walle ba haka bane, Kina ji Dara’ifa? Sai dana tambaye ta nace na mu duka ne? Ni da kawaye na nake nufi. Saboda tun farko sai dana ce mata tazuba mana ni da su. Bayan ta kirani ta mikomin abincin na tambayeta fa ta daga kai alamun eh”

Gajiyalle taja tsaki tana bubbuga hannu a katangar gidan mu, Har gefen dake lilo ya zubo a kasa.

“Guzuma. Yarinyar nan ko yar makaryaciya. Aina akai haka? Na mudika ne? Kika tambaye ni? Na daga kai alamun Eh. Dara’ifa ki ky’ale ni na kacaccala yarinyar nan”

‘Dara’ifa ta shiga tsakanin mu tana janye Gajiyalle tana bata hak’uri,

“Toh Kiyi hak’uri akasi aka samu. Ke dije ita Gajiyalle na nufin abincin Mudi. (Na Mudika) ke kuma Gajiyalle, Dije na tambayar ki ne (Na mu duka?) ma’ana nasu itafa kawayen ta? To adai Yi hak’uri . Abinci dai anci sai kasayarwar sa. Bazai dawo ba, Duka bashi bane. Ke kuma dije Idan kinyi laifi Ki zama mai bada hak’uri kinji”

Daga kai nayi alamun Toh, haka Dara’ifa tagama maganar ta ta tafi. Tana fita Gajiyalle ta hau rankwashi na ji kake ‘qwas’ gwaf’ Kif’ duk a kwanyar kai na. Da alamun Dara’ifa ta jiyo. Ai kuwa ta sake yo sallama ta kirawo ni wai zan kai mata nik’a. Arcewa nai a guje har yin karo da dan akuyar Mudi. Rike hannu na Dara’ifa tayi muka shiga gidan ta, Koina yasha siminti abun sha’awa wallahi kamar na lashe shi. Zama nayi a gefen kitchen kofar dakin ta Ita kuma ta shiga ciki,

“Dara’ifa ina ku’din aiken?”

“Ki hutawar ki Dije babu abunda zaki siyo min, Kawai kiran ki dai nayi naga yadda take nadar ki.”

Dashe baki nayi kawai na cigaba da shasshafa simintin dake malale a k’ofar dakin. Dara’ifa nada kirki, Ita ba tsohuwa bace irin Gajiyalle, Amarya ce amma bata taba haihuwa ba. Daga kauyen alfindi mijinta ya aurota, Shine dan karkarar mu. Sam batada gulma ko biyewa mata n auren karkarar mu dake yawon gidajen juna suna gulma, Ita kullum tana gida tana harkokin gabanta bata shiga lamuran su. Shiyasa suka tsane ta, Kullum cikin yi da ita suke, Wai tacika girman kai, Takance ba girman kai bane gudun zucia ne.

Ina nan zaune har aka kira sallah, Dara’ifa ta fito tayi alwala tayi sallar ta, Inata bin yadda take Sallah gwanin sha’awa. Ta mike ta cire hijabin jikin ta,

“Dije ta shi kiyi alwala kiyi sallah.”

Baki na na bude kafin na rufe shi Ina mai jinjina kai na,

“Ban iya ba. Daga alwalar har sallar.”

“Wai har yanzu bakya sallah dije? Shin ba’a saki a Islamiyya bane ko allo?”

Na daga kai hade da kafad’a ko ajiki na.

“Tashi kiyi alwala mu gani.”

Mikewa nai dakyar na kamfanci ruwa a buta tamkar yadda naga Baffa yana yi wani lokacin. Na wanke hannu na da k’afa sau dai dai sannan na kuskure baki na na zuba ruwa a gashi na, Na gantsare na mike zan bar wajen Dara’ifa ta hanani,

“Innalillahi wa inna ilaihir raji’un! Koma ki zauna, Haka ake alwalar? Shikenan har kin kammala? Oh ni Dara’ifa!”

“Shin dije, Gaji bata koya miki? Anya kin iya karatun sallah ma kuwa?”

Na tabe baki kafin nace

“Itama fa battai, Yasin seta kwan nawa batai ba. Yo alhaki akanta tunda bata koyan.”

Dara’ifa ta girgiza kai kawai, Ta sake debo ishasshen ruwa a buta ta mikamin, Na karba na koma na zauna. Ahankali take koyamin tana min bayani tamkar malama da daliba, Ba lefi na fara ganewa gaskiya. Daga nan tace nayi sallah, Nan ma ban iya ba, Na dudduka kawai na mike na jefar da hijabin data bani a gefe, Nan ma sai data sake koyamin yadda zan dinga yi. Na gane wani abun, Wani kuma ban gane ba. Mudi ne ya leko yace gaji tace naje, Na mike dakyar banso zan koma gida ba har ga Allah. Saboda sam Dara’ifa bata da fada ko hantara irin na Gaji. Har na Kai kofa zan fita ta yafito ni da hannu na koma. Wazobiya ta mikomin hade da radamin a kunne,

“Ki sai sabulun wanka kinji? Sai da safe nagode.”

“Nima nagode Dara’ifa. Allah dai ya biya ki da alkhairi.”

Sallama mu kaiwa juna na tafi gidan mu zuciya ta sam ba dadi. Ji nake dama Dara’ifa ce babata dana more. Take ummata ta fadomin arai na. Uwa mai dadi, Da ace tana raye nasan bazan taba tagayyara kmar haka ba. Wasu zafafan hawaye ne suka zubomin, Cikin sarkakiyar murya nace,

“Allah ka jik’an Umma tah..!”

Tun daga zauren gidan mu nake jiyo sautin suratan Innarajo mahaifiyar Balki K’awata itada Gajiyalle. Sam innarajo bata sona batasan kawancen da muke da Balki ‘yarta. Shiyasa nima na dena shiga harkar Balkin. Wai ashe barar (kudin aure) Balkin aka kawo. Mamman mai shayi ne zai aure ta. Gajiyalle sai guda take tana yada magana.

“Ai wallahi innarajo Gwara ka aurar da yar ka tun tana karama kana iya tankwarata. Yanzu ba gashi ba xatai auren ta tabar yuyar su hannu na mai kafada( Wai ni)”

Ta karasa fada tana mun zunde da baki. Yi nayi tamkar Bansan suna tsakar gidan ba na kauda kai na gefe. Band’aki na shige na rage ciki na kafin na fito nai ficewata yar kasuwa siyo sabulu da kayan k’walam da wazobiyar (hamsin/50 Naira) da Dara’ifa ta bani.


ZAFAFA BIYAR
NA KUDI NE:::

Duka BIYAR 5 zaku samesu akan garabasar naira 700 kacal,

Guda hudu 4 Kuma 500,

Guda uku 3 Kuma 450,

Guda biyu 2 Kuma 400,

Guda daya akan 300.

Ma'ana
Each one is 300
2 is 400
3 is 450
4 is 500
5 is 700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

ACCOUNT NO- *0812652655*
ACCOUNT NAME- *HAFSAT LAWAN GAMBO*
BANK NAME: *ACCESS BANK*

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

*+234 903 234 5899*

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

*09033181070*

Karku Bari ayi Babu ku domin wannnan salon na daban ne
SABUWAR SHEKARA
SABON SALO

TEAM#ZAFAFABIYAR🔥
*KIBIYAR AJALI.....!!!!*
_(Sulke baya tsare ta sai ta wuce)_
🏹👑👩‍❤️‍👨💝

*MALLAKAR:- NANA HAFSAT* 🧕🏼
*(MISS XOXO)*

*©️®️ZAFAFA 5 2021*
(NA KUDI NE! NEMI:+234 903 318 1070 KO +234 903 234 5899 DAN MALLAKAR NA KI!)

*BABI NA 4*
(Free page)

*Cikin* kankanin lokaci aka fara kawo malamai daga cikin birni wadanda zasu koyar da mutanan karkarar mu karatun boko, a cewar mai gari harda na addini duk za'a koyar kuma kyauta, abinda kawai ake bukata shine iyaye su yarda su dinga tura yaransu makaranta. Yaran mai gari dana mai unguwa da liman da sauran masu faɗa aji a kyauyan mu su aka fara sakawa a makarantar saboda ma kar wasu iyayen sunce gashi gashi, su ance su kai yara makaranta amman wadanda suka ce ayi su basu saka nasu can ba, hakan yasa suka fara yiwa tufkar hanci.

Tun daga kan su kuma ba'a kara kai wasu ba, ba wai rashin yaran zuwa makarantar ne babu ba. A'a tsabar su yan garin basu yarda da karatun bokon ba shine ya hana su kai yaran su. Ganin haka ne yasa hakimi da kanshi ya yi magana cewar dole ne kowa ya kai dansa makaranta tun daga kan dan shekara uku zuwa goma sha biyar maza da mata. Amman iyaye mata suka ki barin yaransu mata suyi, a cewar su babu abinda ya kamaci suyi irin talla dan su tara abin da za'a siya musu lokacin aure. Ni kuwa da dama bani da wani mafadi idan ba Baffa na ba, kuma shi ɗin ma ba wani tsoro yake bani ba. Sai ya zamana babu mai cewa Dije shirya na kai ki makaranta, ko kuma Dije zoki je makaranta.

Ranar da aka fara yin karatu naje makarantar amman ba wai shiga nayi ba, lekawa nayi ta taga na hangi su Abu yar gidan mai unguwa zaune a kan benci ta kurawa malamar ido kamar zata hadiye ta, na kwashe da dariya tare da sake yin ɗage yadda zan dinga hangowa sosai nace.

“Kai Abu hekace kin samu talabijin sai kallon matar can kike yi.”

A dai dai lokacin malamar ta juyo da yake rubutu take yi a jikin allo. Ita kam Abu turo baki tayi ko bata fada ba nasan bacin rai ne a zuciyar ta dan itama ba son makarantar take yi ba. Malamar ta saki murmushi cike da tsantsar kulawa ta kalle ni tace.

“Zagayo ki shigo kema.”

Cikin dafe kirji da zaro ido duk a lokaci guda nace mata.

“Wa?” Malamar tace,

“Ke mana, shigo ki zauna a yi karatun dake.”

Budar baki na sai cewa nayi.
Chapter 6 · 0% Book details