Sashe 29
Kibiyar Ajali Part 1 And 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tuni labari yaje wajan Alhaji Isma'il yana kan hanyar shi ta zuwa filin sauka da tashi na malam Aminu Kano zai je birnin Lagos. 'Innalillahi wa'ina ilaihir rajiun' ita kawai yake furtawa tare da juyo da motarsa ya nufi asibitin cike da tashin hankali. Yana hanya ya kira Mami ya sanar da ita cewa tayi maza-maza taje asibitin shima gashi nan zai je. Cikin mamaki duk kuwa da cewa tana cike da tsantsar mamakin jin cewar Dije na kwance a asibiti tace dashi.
“Toh bari na shirya naje, amman kai ya zaka ce ka fasa yin tafiyar bayan ka riga kayi booking d'in tafiyar.?”
“Hajiya wannan ba wata matsala ba ce, jin lafiya marainiyar Allah shine kawai burina. Karki manta Dije amanace a gare ni, kuma ya ce a waje na kamar yadda su Shukrah suke.”
Yana gama maganar ya katse kiran yana jin mamakin matarsa da sam ba ta son ganin yana kyautatawa yarinyar nan. Ta kasa fahimtar cewa wata rana itama zata rabu da nata ya'yan kuma ba ta san waye zai kular mata da su ba. Mata duk lissafin su guda d'aya ne wato za'a riga su mutuwa, duk kuwa da cewa sun sha ganin Allah yana dauke wanda yaso a lokacin kuma yaga dama. Ita kuwa bayan taji ya katse wayar sai ta rike habarta, abin da mijin ta yake yi sam bata jin dadin shi. Haka ta mike taje ta shirya tasa driver ya kai ta bayan ta tambayi wane asibiti ne, aka sanar da ita.
Alhaji Isma'il na zuwa ya sanar da yan sandan dake tsare da gare cewar shine mahaifin Dije, suka barshi ya shiga inda suka bar yan jarida guda uku suka bi bayan shi ciki kuwa harda Mas'oud. Mami ma tana zuwa aka barta ta shiga ta tarar da Alhaji Isma'il ya fito daga wajan likita yana gyaran babbar riga. Ta karasa suka hadu a center, kallon da ya yi mata shine kawai ya tabbar mata da cewar tayi masa laifi wanda ba zai rasa nasaba da nuna cewa aikin shi yafi Dije da ta nuna masa.
“Ashe zaki zo?”
Ya tambaye ta yana mai lasar lebensa da ya fara bushewa saboda kaduwar da ya shiga. Kanta yana kasa tana murza zoben zinarin ta tace.
“Me zai hana Alhaji.?”
“Naga kamar baki damu ba ne shi yasa, har na fara tunanin dakko wacce zata kular min da ita.”
Kamar tace ai yanzu ma ba ita zata zauna ba, sai kuma ta hadiye kasan cewar yaki sakar mata fuska ta kasa ganin walwalar shi kamar yadda ya sabar mata.
“A a zan zauna mana Alhaji, yanzu me yaje faruwa da ita?”
Yaja numfashi yace.
“Yanzu likitan ya kira ni yace ta farfado, gefen goshinta ya fashe. Dole sai ta d'an kwana ko biyu ne a asibitin dan bata kulawar likita.”
“Daman ban da fitina ina Dije ina aikin jarida tsakani da Allah fa. Duk irin karatukan duniyar nan ta rasa wanne za ta yi sai shi saboda kawai taso ta dinga shiga cikin ridan-ridan maza. Gashi nan yanzu taje an....”
“Ya isa haka Hajiya naji. Duk da haka ma dai zan kawo wacce zata kula da Dije, ke sai ki koma gida saboda yara.”
Ta fi nono fari daman ba so take ta zauna d'in ba kawai fushin sa ne bata so shi yasa ta yadda cewa zata zauna. Yanzu kuwa da yace ta tafi idan ta gama abin da zata yi bata ja ba saboda kar taje yace ya fasa dole ita zata zauna. Ya nufi room din da aka kwanta da Dije wacce ke ta faman bacci tamkar babu abinda ya same ta. Sunkuye suka tarar da Mas'oud a gefen ta yana sharar hawaye, Alhaji Isma'il ya tambayi waye shi suka tabbatar masa da cewa abokin aikin ta ne, gidan radio d'in su d'aya.
“Allah sarki, hakuri zaka yi muma duk shi zamu yi. Dubi goshinta duk da cewar an rufe kasan cewar ciwon ba kadan bane ba. Allah ya baki lafiya Dije, yasa kaffara ne.”
Sun jima sosai a dakin kafin su fito dan gabar da sallah. Addu'a kam Dije tasha a gurin Alhaji Isma'il da Mas'oud wanda ya kasa bayyana mishi alakarshi da ita. Mami ta zauna akan kujera suna waya da Hameedah tana sanar mata da abin da ya faru wanda taji a bakin wani d'an jarida da abin ya faru a gaban su.
“Kinji yarinya Mami, ko tayi zaton har yanzu a kauye take ne?”
“Kema dai kya fada.” Cewar Mami.
“Sarki fa! Taya Dije zata ce zata yiwa sarki interview banda dai ta latsawa kanta tunani. Ai gashi nan ta jawowa kanta an ji mata ciwo a banza. Kuma ance masarautar bata yi wani abu ba akan lamarin ko?”
“Uhmmm! Kin san dai ba sarauta bace ta kauye, kuma yanzu ma rufe maganar aje son yi saboda kar a batawa masarautar suna.”
Haka Mami ta zauna a gurin Dije babu wata alfarma da take yi mata saboda tsabar wulakanci, Allah ya taimaka ma bacci take ta yi, da watakila sai tayi hawaye da idanunta. Suna idar da sallah Alhaji Isma'il ya lallaba Mas'oud ya tafi kar ya damu zata ji sauki harma ta koma aiki da ikon Allah. Ya tafi ba dan yaso ba sai dan kar Alhajin yaga kamar bashi da kunya ko sabanin haka.
Gabaki d'aya Alhaji Isma'il ya kasa samun sukuni ko fita ya yi yanzu zaka ga ya dawo har dare lokacin da Allah yasa Dije ta farka. Da Mas'oud ta fara yin karo da idanuwanta, kasan cewar ya sake dawowa asibiti da aka yi salla magariba, ya kasa zama sam shi yasa ya dawo. Dishi-dishi haka ta dinga ganinshi, ta gane shi tsab sai dai bata iya ganinshi tar-tar kamar yadda ta saba kallon abu. Ya mike tsaye tare da karasawa gurin ta yana cewa
“Alhamdulillahi ta farka Allah mun gode maka.”
Alhaji Isma'il ya shigo da sauri cike da tsantsar farin ciki juyowa da ya yi cewar Dije ta farka. Kallon mutane kawai take ba baki taki koda motsa shi bare a saka ran zata yi magana. Nurse ta shigo wacce ita ce ya bawa kwangilar kular masa da Dije. Sannu a hankali ya taje ta gyara mata inda ya kamata cikin haka ne ma suka ji ta furta.
“Kawu daddy.”
Tamkar ta tsira masa wani abun, haka yaji ya nufe ta ya riko hannunta, hawaye suka biyo ta cikin kyawawan idanuwanta, yasa hannu d'aya da yake kusa da fuskar ya share mata yana cewa.
“Bar kukan nan Dije, dena kuka zaki warke da ikon Allah.”
Still bakin ba wai budewa ya yi da yawa ba wajan son yin magana, ta kuma cewa.
“Kawu daddy sarki ne ya harbe ni ko? Wallahi ba bu abin da nayi masa kawai daga tam......”
“Yi shiru Dije, tsautsayi ne kawai da kuma kaddara suka fad'a kanki. Allah ya riga ya kaddara cewa hakan zata faru dake tun farko. Kiyi hakuri zan tsaya tsayin daka, da ikon ubangiji zaki dawo kamar baki yi ba kinji yarinya ta?”
Lumshe ido kawai tayi saboda yadda take jin kanta ya yi mata wani irin kato tamkar an dora mata duniya haka take jinsa, saboda raunin da yake a goshin ta shine ya yi sanadiyyar hakan. Ta sunkuyar da kanta kasa ba tare da ta kuma cewa komai ba sai zuciyar ta da ta addabeta akan ganin rashin imani da rashin mutunci a gurin bafaden da ya ce mata yar talakawa. Bata taba zato ku tsammanin cewa haka suke ba, ashe ba su da kirki kansu kawai suka sani. Amman ban da haka ba ta ga dalilin da zai sanya su dinga yiwa mutane abin da suke yi ba. Mas'oud ya dinga kallanta yana son su sake had'a ido ko zai ji sassauci akan zugi da rada din da yake zuciyar shi, yana son ta nuna masa wata alama da zata tabbatar mishi da cewa a kowane yanayi take ciki zata iya gane shi da kuma matsayin da yake a gurin ta.
Ganin tsawon lokaci taki dagowa ya sanya shi juyawa zai fita daga dakin, kamar an ce ya kuma kallon ta sai yaga ta dago ta kalleshi tana rausayar da kai alamar damuwa. Ya koma tare da cewa.
“Sannu kinji?”
Ta kifta idanuwa alamun ta amsa gashi yaga taki kawar da ido daga kansa yace.
“A kawo tea ko?”
Tayi shiru ba ta ce komai ba dan magana da kyar take iyawa. Nurse d'in tace ya bari a had'a mata suma zasu so ganin ta d'an ci wani abun ko ya ya ne. Alhaji Isma'il da kanshi ya dinga bata a hankali kasan cewar da kyar take iya daga lebeanta har a samu tea ɗin. Kadan tashi ba ne yawa ba sannan aka kuma kwantar da ita.
Haka taci gaba da kwanciya a asibiti tana samun kulawar likitoci. Yan dubiya kuwa ba'a magana, ta ko'ina zuwa ake ana duba ta, har ta fara samun lafiya fuskarta tasabe kumburin ya baje sai gurin ciwon kawai. Mas'oud kam kullum yana asibitin tun safe har dare, hakan ya kuma tabbatarwa da Dije cewar Mas'oud shine farin ciki da walwalarta a rayuwa. Soyayyarsa ta kuma ninkewa a duk wasu sassan jikinta masu motsi da kai sakonnin gamsuwa ga abin da aka hakikance akan shi. Su Hameedah da Shukrah ma kullum sai sunje, a wannan zuwan ne kuma Shukrah ta fara nanikewa Mas'oud, ko be kulata ba sai ta kula shi saboda Mas'oud ba baya ba wajan tsarin halitta.
Duk da cewa Dije ba ta da lafiya hakan be hanata jin kishi ba, yadda Shukrah take nanikewa abin alfaharinta abin yana mata ciwo dan yafi raunin goshinta zafi da radadi. Yau kwanaki biyar kenan wajan karfe hudu suna zazzune ana ta hira, duk da cewa shi baya kula su amman wata maganar idan an sako shi yana magana, yanzu ma hakan ce ta faru, Shukrah tace.
“Abokin aiki gaskiya kana da kirki.” Ba tare da ya kalleta ba yace.
“Da nayi mene?” Shukrah ta saki murmushi tare da cewa.
“Gani muka yi tunda wannan abin ya faru da Dije kullum kana nan har ka fimu zama a gurin ta.”
“Toh bari na shirya naje, amman kai ya zaka ce ka fasa yin tafiyar bayan ka riga kayi booking d'in tafiyar.?”
“Hajiya wannan ba wata matsala ba ce, jin lafiya marainiyar Allah shine kawai burina. Karki manta Dije amanace a gare ni, kuma ya ce a waje na kamar yadda su Shukrah suke.”
Yana gama maganar ya katse kiran yana jin mamakin matarsa da sam ba ta son ganin yana kyautatawa yarinyar nan. Ta kasa fahimtar cewa wata rana itama zata rabu da nata ya'yan kuma ba ta san waye zai kular mata da su ba. Mata duk lissafin su guda d'aya ne wato za'a riga su mutuwa, duk kuwa da cewa sun sha ganin Allah yana dauke wanda yaso a lokacin kuma yaga dama. Ita kuwa bayan taji ya katse wayar sai ta rike habarta, abin da mijin ta yake yi sam bata jin dadin shi. Haka ta mike taje ta shirya tasa driver ya kai ta bayan ta tambayi wane asibiti ne, aka sanar da ita.
Alhaji Isma'il na zuwa ya sanar da yan sandan dake tsare da gare cewar shine mahaifin Dije, suka barshi ya shiga inda suka bar yan jarida guda uku suka bi bayan shi ciki kuwa harda Mas'oud. Mami ma tana zuwa aka barta ta shiga ta tarar da Alhaji Isma'il ya fito daga wajan likita yana gyaran babbar riga. Ta karasa suka hadu a center, kallon da ya yi mata shine kawai ya tabbar mata da cewar tayi masa laifi wanda ba zai rasa nasaba da nuna cewa aikin shi yafi Dije da ta nuna masa.
“Ashe zaki zo?”
Ya tambaye ta yana mai lasar lebensa da ya fara bushewa saboda kaduwar da ya shiga. Kanta yana kasa tana murza zoben zinarin ta tace.
“Me zai hana Alhaji.?”
“Naga kamar baki damu ba ne shi yasa, har na fara tunanin dakko wacce zata kular min da ita.”
Kamar tace ai yanzu ma ba ita zata zauna ba, sai kuma ta hadiye kasan cewar yaki sakar mata fuska ta kasa ganin walwalar shi kamar yadda ya sabar mata.
“A a zan zauna mana Alhaji, yanzu me yaje faruwa da ita?”
Yaja numfashi yace.
“Yanzu likitan ya kira ni yace ta farfado, gefen goshinta ya fashe. Dole sai ta d'an kwana ko biyu ne a asibitin dan bata kulawar likita.”
“Daman ban da fitina ina Dije ina aikin jarida tsakani da Allah fa. Duk irin karatukan duniyar nan ta rasa wanne za ta yi sai shi saboda kawai taso ta dinga shiga cikin ridan-ridan maza. Gashi nan yanzu taje an....”
“Ya isa haka Hajiya naji. Duk da haka ma dai zan kawo wacce zata kula da Dije, ke sai ki koma gida saboda yara.”
Ta fi nono fari daman ba so take ta zauna d'in ba kawai fushin sa ne bata so shi yasa ta yadda cewa zata zauna. Yanzu kuwa da yace ta tafi idan ta gama abin da zata yi bata ja ba saboda kar taje yace ya fasa dole ita zata zauna. Ya nufi room din da aka kwanta da Dije wacce ke ta faman bacci tamkar babu abinda ya same ta. Sunkuye suka tarar da Mas'oud a gefen ta yana sharar hawaye, Alhaji Isma'il ya tambayi waye shi suka tabbatar masa da cewa abokin aikin ta ne, gidan radio d'in su d'aya.
“Allah sarki, hakuri zaka yi muma duk shi zamu yi. Dubi goshinta duk da cewar an rufe kasan cewar ciwon ba kadan bane ba. Allah ya baki lafiya Dije, yasa kaffara ne.”
Sun jima sosai a dakin kafin su fito dan gabar da sallah. Addu'a kam Dije tasha a gurin Alhaji Isma'il da Mas'oud wanda ya kasa bayyana mishi alakarshi da ita. Mami ta zauna akan kujera suna waya da Hameedah tana sanar mata da abin da ya faru wanda taji a bakin wani d'an jarida da abin ya faru a gaban su.
“Kinji yarinya Mami, ko tayi zaton har yanzu a kauye take ne?”
“Kema dai kya fada.” Cewar Mami.
“Sarki fa! Taya Dije zata ce zata yiwa sarki interview banda dai ta latsawa kanta tunani. Ai gashi nan ta jawowa kanta an ji mata ciwo a banza. Kuma ance masarautar bata yi wani abu ba akan lamarin ko?”
“Uhmmm! Kin san dai ba sarauta bace ta kauye, kuma yanzu ma rufe maganar aje son yi saboda kar a batawa masarautar suna.”
Haka Mami ta zauna a gurin Dije babu wata alfarma da take yi mata saboda tsabar wulakanci, Allah ya taimaka ma bacci take ta yi, da watakila sai tayi hawaye da idanunta. Suna idar da sallah Alhaji Isma'il ya lallaba Mas'oud ya tafi kar ya damu zata ji sauki harma ta koma aiki da ikon Allah. Ya tafi ba dan yaso ba sai dan kar Alhajin yaga kamar bashi da kunya ko sabanin haka.
Gabaki d'aya Alhaji Isma'il ya kasa samun sukuni ko fita ya yi yanzu zaka ga ya dawo har dare lokacin da Allah yasa Dije ta farka. Da Mas'oud ta fara yin karo da idanuwanta, kasan cewar ya sake dawowa asibiti da aka yi salla magariba, ya kasa zama sam shi yasa ya dawo. Dishi-dishi haka ta dinga ganinshi, ta gane shi tsab sai dai bata iya ganinshi tar-tar kamar yadda ta saba kallon abu. Ya mike tsaye tare da karasawa gurin ta yana cewa
“Alhamdulillahi ta farka Allah mun gode maka.”
Alhaji Isma'il ya shigo da sauri cike da tsantsar farin ciki juyowa da ya yi cewar Dije ta farka. Kallon mutane kawai take ba baki taki koda motsa shi bare a saka ran zata yi magana. Nurse ta shigo wacce ita ce ya bawa kwangilar kular masa da Dije. Sannu a hankali ya taje ta gyara mata inda ya kamata cikin haka ne ma suka ji ta furta.
“Kawu daddy.”
Tamkar ta tsira masa wani abun, haka yaji ya nufe ta ya riko hannunta, hawaye suka biyo ta cikin kyawawan idanuwanta, yasa hannu d'aya da yake kusa da fuskar ya share mata yana cewa.
“Bar kukan nan Dije, dena kuka zaki warke da ikon Allah.”
Still bakin ba wai budewa ya yi da yawa ba wajan son yin magana, ta kuma cewa.
“Kawu daddy sarki ne ya harbe ni ko? Wallahi ba bu abin da nayi masa kawai daga tam......”
“Yi shiru Dije, tsautsayi ne kawai da kuma kaddara suka fad'a kanki. Allah ya riga ya kaddara cewa hakan zata faru dake tun farko. Kiyi hakuri zan tsaya tsayin daka, da ikon ubangiji zaki dawo kamar baki yi ba kinji yarinya ta?”
Lumshe ido kawai tayi saboda yadda take jin kanta ya yi mata wani irin kato tamkar an dora mata duniya haka take jinsa, saboda raunin da yake a goshin ta shine ya yi sanadiyyar hakan. Ta sunkuyar da kanta kasa ba tare da ta kuma cewa komai ba sai zuciyar ta da ta addabeta akan ganin rashin imani da rashin mutunci a gurin bafaden da ya ce mata yar talakawa. Bata taba zato ku tsammanin cewa haka suke ba, ashe ba su da kirki kansu kawai suka sani. Amman ban da haka ba ta ga dalilin da zai sanya su dinga yiwa mutane abin da suke yi ba. Mas'oud ya dinga kallanta yana son su sake had'a ido ko zai ji sassauci akan zugi da rada din da yake zuciyar shi, yana son ta nuna masa wata alama da zata tabbatar mishi da cewa a kowane yanayi take ciki zata iya gane shi da kuma matsayin da yake a gurin ta.
Ganin tsawon lokaci taki dagowa ya sanya shi juyawa zai fita daga dakin, kamar an ce ya kuma kallon ta sai yaga ta dago ta kalleshi tana rausayar da kai alamar damuwa. Ya koma tare da cewa.
“Sannu kinji?”
Ta kifta idanuwa alamun ta amsa gashi yaga taki kawar da ido daga kansa yace.
“A kawo tea ko?”
Tayi shiru ba ta ce komai ba dan magana da kyar take iyawa. Nurse d'in tace ya bari a had'a mata suma zasu so ganin ta d'an ci wani abun ko ya ya ne. Alhaji Isma'il da kanshi ya dinga bata a hankali kasan cewar da kyar take iya daga lebeanta har a samu tea ɗin. Kadan tashi ba ne yawa ba sannan aka kuma kwantar da ita.
Haka taci gaba da kwanciya a asibiti tana samun kulawar likitoci. Yan dubiya kuwa ba'a magana, ta ko'ina zuwa ake ana duba ta, har ta fara samun lafiya fuskarta tasabe kumburin ya baje sai gurin ciwon kawai. Mas'oud kam kullum yana asibitin tun safe har dare, hakan ya kuma tabbatarwa da Dije cewar Mas'oud shine farin ciki da walwalarta a rayuwa. Soyayyarsa ta kuma ninkewa a duk wasu sassan jikinta masu motsi da kai sakonnin gamsuwa ga abin da aka hakikance akan shi. Su Hameedah da Shukrah ma kullum sai sunje, a wannan zuwan ne kuma Shukrah ta fara nanikewa Mas'oud, ko be kulata ba sai ta kula shi saboda Mas'oud ba baya ba wajan tsarin halitta.
Duk da cewa Dije ba ta da lafiya hakan be hanata jin kishi ba, yadda Shukrah take nanikewa abin alfaharinta abin yana mata ciwo dan yafi raunin goshinta zafi da radadi. Yau kwanaki biyar kenan wajan karfe hudu suna zazzune ana ta hira, duk da cewa shi baya kula su amman wata maganar idan an sako shi yana magana, yanzu ma hakan ce ta faru, Shukrah tace.
“Abokin aiki gaskiya kana da kirki.” Ba tare da ya kalleta ba yace.
“Da nayi mene?” Shukrah ta saki murmushi tare da cewa.
“Gani muka yi tunda wannan abin ya faru da Dije kullum kana nan har ka fimu zama a gurin ta.”