← Book details Kibiyar Ajali Part 1 And 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 1 OF 114

Sashe 1

Kibiyar Ajali Part 1 And 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

*KIBIYAR AJALI.....!!!!*
_(Sulke baya tare ta sai ta wuce)_
🏹👑👩‍❤️‍👨💝

*MALLAKAR:- NANA HAFSAT 🧕🏼*
*(MISS XOXO)*

*©️®️ZAFAFA 5: 2021*
(PAID NOVELS)

BABI NA: 1

[1:1] بسم الله الرحمن الرحيم

In the name of Allah, the Gracious, the Merciful.

_*KAUYEN DURB’UN*_

“Mudi!Mudi! Mudikalle na dan albarka! Dan Allah duba waje ko zaka gano min keyar yarinyar nan tunda tafita siyo koko tun duhun safiya bata dawo ba har yanzu.. Oh ni salamatu wannan yarinya ko yar bankadaddiya. Fita ka nemo min ita na casata a gidan nan.”

Mudi dake goge hakoran sa da gawayi yaja dogon tsaki yana mai kuskure korayen hakoran sa da sukai tamkar gansa kuka, Kafin ya mike cikin mita ya dubi mahaifiyar tasa yana sakato kwanannan daskararren tasonan hancin sa,

“Gaskia gajiyalle nagaji. Ke kullum aike aike, Ni Ina zansan inda shedaniyar nan take..?”

“Haba Mudi na! Yi hak’uri kaji temaka ka nemota saboda kai ma na aiketa tasiyo.”

Mudi yana cuno baki gaba haka yafice bayan ya jefi mahaifiyar tasa gajiyalle da harara. Can kasan bishiyar dirimin layin su ya hangota da cincirindon yara akanta, Kowa ya tsaya yana kallon su. Ga ledar kokonta a gefe ta fashe kokan ya tsiyaye, Ta cakumo wuyan yaron wanda da alama shine ya zubar da kokon. Rantsuwa ta shiga kwarara wa tana kifa masa mari. Jikin yaron gaba d’aya rawa yake yi kuma da alama a girme ya girme mata.

“Kutumelesin kan babban bala’in dirimin durbun, Walle ko dan haladu (Baban sa)ne zai zo wajen nan sai na lallasa ka. Kokon har na wazobiya ace ka barar min? Bazan yadda ba ko wajen mai gari za’aje.”

Na sake duban kokon daya malalar ina tuno yadda gajiyalle zata caskalani, Zuciyata ta kara zafi na daga hannu na sake dirka masa rankwashi a kwanyar kansa ji kake,
‘Qwas..’

“Ke! Ke! Ke! Toh kizo inji gajiyalle banza bankadaddiya.”

Daga jin yadda aka kirawoni bankadaddiya nasan Mudi ne, ‘Dan gajiyalle matar babana. Na dubi Mudansiru dake hawaye sha’be shabe yana shafa kuncin sa dana lallafta masa mari. Ai kuwa na kame awajen naki zuwa wajen Mudi, Cikin haka sai ga dan haladu mai rake mahaifin mudansiru, Yana tafe yana kankare raken sa, Mudansiru na ganin sa ya sake barkewa da kuka yana nuno ni, Ni kuwa na shiga harara ina watsa hannu sama domin ba yadda zan yi ba.

“Kai Meya faru? Waya dake ka?”

Dan haladu ya tambaya yana mai janyo mudansiru jikin sa, Na tabe baki ina mika hannu na saitin sa tamkar ance na mika,

“Koko na na wazobiya ya barar min nace ya biya ni yaki biya.”

Na karasa fada ina gatsine. Dan haladu yaja dogon tsaki yana mai dankarawa mudansiru Harara,

“Shine ka bari mace ta maka duka? Allah ya sawwake. Ke kuma Ungo talatin domin bakici hamsin ba tunda kin lafce shi.”

“Meyaci murtalar (nera ashirin) din?”

“Laftar sa da ki kai. Rike kafin na maida kudi na.”

Na karbi kudin ina karewa murtalar din kallo na girgiza kai,

“Kai bazata karbu ba yasin ta yage da yawa.”

Wafcewa dan haladu yai ya cillo min wata na karb’e ina cuno baki gaba. Dan haladu ya tisa k’eyar mudansiru gaba yana sake jibgar sa akan bari da yai na tule shi batare daya rama ba, Sauran yara dake wajen suka sa shewa suna tafa hannaye, Suka shiga yi min kirari na wanda kaf kauyen durbun kowa yasan da shi,

“Woo Dijangala oganniya , Qadangaren bakin tulu, Ta gajiyalle mai yar hakiya.”

Tabbas ni oga ce shysa sauran yara ke kira na oganniya. Domin duk wani fada lungu da sako nike cinye shi sannan wani lokacin har siyan fada nake na tarewa marasa k’arfi. Mudi ya cakumo hannu na ya kwace talatin din sannan ya tisa keya ta har gida. Tun a farkon layin mu na yai nasa wuri ni kuma na kama hanyar shiga gida, Ina kambama mamakin Mudi da halin satar sa, Kusan kullum hakan yakeyi Idan gajiyalle ta aike ni. Ina zuwa gajiyalle tundaga soro tana tsaye da muciya a hannun ta tana gani na ta janyo ni ta hau bugu tamkar tasamu jaka. Tana yi ina kirga duwarwatsun hannu na, Domin Inde duka ne na saba ya zama jiki sam banajin zafin sa ko kadan.

“Shegiya almura da idanu zuru-zuru, Yar iskar yarinya, Mumugunciya yau kuma wani fadan kika rakito. Ina kudin dan uban ki?

“Mudi ya...”

Ruwan ciki na ta haye ta hau duka na tana yakushi na kamar mage.

“Guzumar uba! Narantse da uban da ya haifeni zan cire miki hakora, Yau ma Sharrin zaki masa? Kinje kin kashe kudin Shine zaki sake karairakin da kike? Ban haifi barowa ba, Kece barauniya da kika tsotsa a mama. Matsa kafin na shureki ki mutu. Bankadaddiyar banza bankadaddiyar wofi.”

Matsawa nai gefe ina goge hawayen bakin cikin da Mudi da gajiyalle ke kunsa min kullum, Ina ji ina gani ta fita ta sayo kosai da zafin sa sai kamshi yake yi ga kunun gidan yar asabe daya sha kayan kamshi, Mudi ya dawo suka shiga ci suna korawa da kunun hankalin su kwance. Ni kuwa cikina sai kukan yunwa yake yi. Baya na juya musu Ina tunanin yadda zanyi na samu abunda zan sanya a baki na, Domin nasan yau gaba d’aya gajiyalle bazata bani abinci ba.

Tulin wanke wanken dake jira na na kalla, Mi’kewa nai dakyar Ina bubbuga konkosona na karasa wajen na duka na fara dauraye su ina tara kanzo a gefe. Cikin haka Laraba mai kaya ta shigo gidan tana doka sallama, Gaisawa sukai dasu nima na gaishe ta ta amsa tana bantarar goro,

“Gajiyalle! Gajiyalle ta ubale, daga ke ba kari sai dabbobin ki da kajin ki da Mudin ki..”

Gajiyalle ta dashare hakora tana mutstsuka kananun kwayar idanun ta mai dauke da hakiya. Jinta take a sama a duk lokacin da aka yi mata wannan kirarin.

Ruwan dauraya ya kare sai na ebo acan gangaren bakin gari. Mikewa nai na dauki bokiti ina sosa kai na dake min kaikayi rabona da wankeshi tun sallar bara sai tsami yake yi yana tashin doyi. To yaxanyi? Babu sabulun dazan wanke dashi, Wanka ma haka nake yi ba sabulu, Shiyasa na kan dau tsawon lokaci shima kafin nayi. Ficewa nai kogin na gangare ebo ruwa, Kafata ko takauni babu domin babu halin samu...

Kafin dai naje rafi na dawo nayi fa’da da yara ba adadi, Wani daga rabiya abu ya dawo kai na, Wani kuma ni na sai fadan. A haka dai na ebo ruwan ina ‘digirgire gab da gangaren unguwar kuka na sake hango cincirundan yara ana dambatuwa. A sukwane na ajiye bokitin kai na, Na dira a tsakiyar filin, Ganin yadda ake tular Nafisa yar Badamasi kansilar garin mu, Kuma ba kowa bane ke dukan ta fyace kabiru dan gidan Nanun me kyamis. Wai Kabiru Nafisa ke bari yana jibgarta. Kabiru fa? Kabiru dai abu kamar ka hure shi ya fad’i saboda rashin auki. Kankace kanzil na janyo shi na lallafta masa mari a duka kuncinan sa, Ba tare da neman ba’asin asalin fad’an ba.

Yara dake gefe suka hau tafin,

“Woo ke Dijangala oganniya, Ta mai gari..”

Na sheke da dariya ina bin Kabiru dake hawaye da kallo, Nafisa ta matso kusa dani tana min godiya, Na sosa duddugaggen gashi kai na daya lalace saboda rashin gyara. Kafin nace,

“Sai ni Dije-Dijangala-Ta mai gari.. Oganniya yar baffan ta..”

Sauran yara suka hau shewa suna tafa min. Kabiru ya kwashi takalman sa ya zura a guje. Nafisa ta rik’o hannu na tana dashare hak’ora. Na cuno mitsitsin baki na gaba ina gatsina shi, Kafin na daga hannun dama na sama, Na kwararo rantsuwa na buga a zani na,

“Dame zaki biya rabiyar fadan ki? Kinga dai siya nayi, Idan baki yadda ba na kira Kabiru ku karasa daga inda kuka tsaya,”

Na karasa fada ina bubbuga kafa ta hade da jijjiga kwankwaso na. Nafisa tayi rau-rau da idanu tana murza hannun ta alamun dai batada abunda zata bani, Naja shewa ina shata layi a tsakanin mu da ita,

“Kan babban balai, Alo tsiya alo danja, Shege ka fasa dan halak sai yanka... Kina nufin ba zaki biya ba?”

“Kiyi hak’uri Dijangala, Yanzun bani da abunda zan baki...”

Kukan kura nai na cakumo wuyan rigar ta ta yan gayu, Dai dai lokacin da Mudikallen Gajiyalle ya karaso wajen yana mai dakamin tsawa,

“Ke dalla can zo ki wuce mu tafi gida uwar ƴan masifa kawai.”

Yayi magana yana banbare hannun da na ri’ke kwalar Nafisa.

“Idan na bar wajan nan ayi gunduwa-gunduwa dani, yo yama za'a yi na siyi fadanta, Tak’i biya ace na hak’ura? Hum uhm!”

“Marar kunya kawai, ni kike gayawa wannan maganar? Zaki tafi gida ko sai na koya miki hankali yanzu a wajan nan.”

Na shiga huci kamar wacce zaki ya biyo daga jeji na sakarwa Nafisa wuya, Ina faman murgud’a baki nace.

“Wallahi bashi ne ki kaci sai kin biya ni.”

Na figi bokiti na nufi gida ina masifa kai kace wani gagarumin abu aka yi min . Da zakara na fara cin karo a zaure yana kwance, Zuciyata sai zugi take, Nasa kafa na shure shi, ya tashi firrrr yana kuka ya shige cikin gidan. naja tsaki Ina galla masa harara tamkar da mutum nake,

“Da karka tashi, wallahi da sai na karya maka kafa d'aya. Gaji..! Gaji..!! Gaji wai kina ina!!!?”

Gajiyalle ta fito daga cikin daki hannunta ri’ke da mafici wanda alamu suka nuna fifita take yi saboda zafi.

“Ya aka yi kike ta faman rafka min kira tamkar wata tsohuwar makauniya?”

Na sanya bayan hannun na dinga murza ido kamar wacce na yiwa sarki karya. Na sake zukar iska cikin hanci na tare da murguda baki ina kifta ido nace.

“Gajiyalle rabiyar fada nayi tsakanin Nafisan kansila da Kabiru Dan gidan mai kyamis. Nace Nafisan ta kawo ladan tariyan fadan taki. Kuma wallahi yunwa nake ji, ciki na zafi kawai yake yi kamar ana hura garwashi.”

Gajiyalle ta kalli Dije sama da kasa cikin takaici, zuciyarta na tafasa kamar taje ta shake ta haka taji. Juyawa tayi ta koma cikin dakin tana mai jan tagwayen tsaki,
Chapter 1 · 0% Book details