← Book details Sakayyah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 97 OF 114

Sashe 97

Sakayyah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Khausar kuwa jin Asma'u tayi Picking call ɗin yasa cikin sauri tace.
“Asma'u”.
Cikin wata dashash-shiyar murya mai cike da rauni Asma'u tace.
“Na'am Khausar”.
Cikin alamun damuwa Khausar tace.
“Asma'u wai me nake ji?”.
Cikin muryan kuka Asma'u tace.
“Khausar an sace Yah Jameel yau kwana biyu kenan kusan na uku ba Yaya Jameel ba labarinsa”.
Atsorace Khausar ta dafe hannunta aƙirji kana tace.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n ansace Yah Jameel Kuma?”.
Kai Asma'u ta gyaɗa hawaye na bin kuncinta tace.
“Eh”,
Cikin sanyin murya tace.
“Ubangiji Allah ya bayyana shi aduk inda yake Allah ya fito mana dashi”.
Ameen Asma'u ta amsa tare da katse kiran.

Kallon Mommy Khausar cikin tashin hankali tace.
“Mommy wallahi da gaske an sace sa”.
Girgiza kai Mommy tayi tare da cewa.
“Ya Salam wallahi bamu sani ba barin idan Abbanku ya shigo zan tambaye sa muje muyi wa Umminsa jaje Ubangiji Allah ya bayyana shi Allah ya tsaresa aduk inda yake”.
Khausar kuwa kasa tsaida hawayen ta tayi cikin Muryan kuka tace.
“Ameen Mommy Ameen ya hayyu ya ƙayyum Allah ya bayyana Malam Jameel har kwana biyu kuma!?”.

Ta gumi Hajiya Bunayya tayi tare da marairaice fuska kana tace.
“Hakane kam wannan duniyar ta zama abin tsoro idan kana fama da talauci ka banu idan kayi wadata ɓarayi da ƴan Kidnapping su hanaka kwanciyar hankali da nutsuwa Allah dai ya kyauta”.
Ta faɗa tare da miƙewa ta fice ranta fess.
Baki ɗaya Wunin wannan ranan haka Mommy da Khausar suka yita cikin jimami da fargaba musamman Khausar ta gagara tsaida hawayen ta.

Moddibo kuwa yana fita daga sashen Innayi mota ya shiga tare da nufar gidan Abba yana isa ana kiran maghariba tare da Abba suka shiga Masallaci suka gabatar da sallah.
Acan ɓangaren Mommy kuwa bayan an idar da sallar Isha'i ta sanarwa da Lamiɗo suna san zuwa yiwa Ummi jaje nan yace ba damuwa ta kira Khausar da Hajiya Bunayya su fito bayan sun fito da kansa yayi Driving ɗinsu zuwa gidan Ummi.
Bayan sun isa.
Mommy ce agaba sai Khausar sai kuma Hajiya Bunayya bakinsa ɗauke da Sallama suka shiga dai-dai lokacin kuma maƙotansu suka fito.

Zaune suka samu Ummi kan 2sitter tana riƙe da Kur'ani Idanunta sun kumbura sun ƙanƙance yayin da Asma'u ke zaune gefenta hannunta riƙe da Carbi.

Cikin sauri Khausar ta ƙarasa kusa da Asma'u tare da riƙe hannun ta kana tace.
“Asma'u da gaske wai dagaske ansace Yah Jameel!?”.
Cikin zubda hawaye Asma'u ta gyaɗa mata kai kana tace.
“Khausar da gaske ansace Yah Jameel tun randa kikazo ya maida kin nan, har yanzu babu labarin sa yanzu kusan dare na uku kenan za ashiga”.
Khausar ma cikin zubda hawaye ta damƙe hannun Asma'u tare da cewa.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n”.
Kallon Ummi Hajiya Bunayya tayi tare da cewa.
“Ayyah Ummin Jameel Ashe abinda ya faru kenan toh Ubangiji Allah ya tsare Allah ya bayyana shi”.
Kai Ummi ta gyaɗa tare da faɗin.
“Ameen ya Allah Nagode”.
Mommy kuwa kafaɗar ta ta dafa kana tace.
“Ba komai Ummin Jameel kiyi haƙuri ki daina kukan nan ki riƙa yi masa addu'a Insha Allah Ubangijin zai bayyana shi”.
Cikin sauri Ummi ta share hawayenta kana tace.
“Nagode Mommyn Khausar Nagode³”.
Cike da tausayawa Mommy ke sake ƙarfafa mata guiwa.
Ahankali Khausar ta juya tare da kallon Ummi cikin Muryan kuka tace.
“Ummi Allah ya bayyanar da Yah Jameel insha Allah ba zasu samu nasarar cutar da shiba zamu tayi masa addu'a Allah ya karesa”.
Miƙewa Hajiya Bunayya tayi kana tace.
“Bari mutafi Alhj na jiran mu awaje yace a gaidaki".
Kai Ummi ta gyaɗa tare da cewa.
“Nogeda Allah ya saka”.
Sannan suka fita a coumpund suka haɗu da wasu matan sun shigo yiwa Ummi jaje bayan sun koma gida.

Baki ɗaya Khausar ta kasa nutsuwa kafin ta kwanta taje tayi alwala kana ta ɗauki Kur'ani tana ta karatu tare da tawassali dashi da niyyan Ubangiji ya bayyana M Jameel aduk inda yake.

Misalin ƙarfe goma na dare kamar lokacin da aka dauke M Jameel Moddibo dake gefen Abba ya miƙe da niyyar tafiya Akuma dai-dai lokacin wayar Abba dake gabansa ta hau ruri.
Atare Abba da Moddibo suka kalli wayar cikin sauri Abba yayi Picking call ɗin tare da kaiwa Kunnensa.
Daga ɗaya ɓangaren akace Alhj Bashiru mahaifin Jameel ko!?”.
Cikin sauri Abba ya gyaɗa kai tare da cewa.
“Eh nine nayi ta kiran layinku baya shiga”.
Cikin fusatacciyar murya Mutumin yace.
“Dama ce maka mukayi idan ka kira zai shiga?”.
Girgiza kai Abba yayi tare da faɗin.
“A'a to menene sharaɗin ku na biyu kaga ban faɗawa kowa ba!”.
Cikin bauɗaɗɗiyar murya Mutumin yace.
“Kuɗin fansa zaka biya shine sharaɗin mu na biyu”.
Kai Abba ya gyaɗa tare da cewa.
“To nawa kuke buƙata?”.
Kai tsaye mutumin yace.
“Milion ɗari biyu”.
Atsorace Abba ya dafe hannunsa aƙirji kana ya zare ido cikin tsanananin firgici yace.
“Milion ɗari biyu!?”.
Atare Hajiya Bunayya da Moddibo da maganar ya dakesu suka haɗa baki atare wajen cewa.
“Milion ɗari biyu?”.
Cike da gadara Mutumin yace.
“Toh idan ba zaka bada ba sai ka shirya karɓan gawar ɗan ka!”.
Cikin sauri Abba ya Girgiza kai tare da cewa.
“Kuyi hakuri dan Allah dan darajar Annabi kada ku kashe wayar”.
Cikin Yanayin ɓacin rai Mutumin yace.
“To ai mun riga mun faɗa muku abinda ake buƙata idan ka shirya gobe zamu sake kiran ka muji ko ka shirya”.
Yana gama fadar haka ya katse kiran...!

By
*GARKUWAR MARUBUTA*

[30/07, 1:40 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: *Littafin SAKAYYAH dai na kuɗi ne ba free book bane 1k ne kacal ki biya ki karanta cikin Aminci kada ki karanta na sata na Allah ya isa. 0661110179 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276 sai in saki a Group ɗina*

Cappande. Acikin tafin hannunsa ya ɗebo sulallan Gwal ɗin da wasu yan guntu-guntun sanduna tare da birbiɗin yashin kana ya shiga jujjuyasu, ahankali ya maida kallonsa kan Innayi data gyaɗa masa kai alamar ya fito dasu hannunsa ya zura acikin tukunyar yashiga kalato salullan wanda na ainihin Gwalne aƙalla sun kai guda ashirin, karkaɗe yashin yayi tare da fitowa dasu kana ya ɗaura su akan rigarsa tare da gyara zaman sa abakin ramin ya tsura mata Ido Innayi ma ido ta zuba masa ganin yanda ya zauna yasa tashiga maida yashin ta rufe ramin kana ta sanya duwatsun ta rufe tare da tura fantekar kan ramin kallon Moddibo dake binta da kallo tayi kana tace.
“Ɗaura min randan nan akai”.
Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe still Idanunsa na Kanta cikin sanyin murya yace.
“Innayi wannan kamar Gwal?”.
Kai ta gyaɗa masa kana tace.
“Eh Gwal ne”
Still ba tare daya motsa ba ya sake kallon Gwal ɗin kana yace.
“Ina kika same su Innayi?”.
Girgiza masa kai tayi kana tace.
“Wannan ba lokacin tambayar ina nasamu gwala-gwalai bane. Moddibo lokacine daya kamata ace ka lissafa su muga adadin su kana musan nawa za'a samu mu haɗa mu karɓo Jameelu yanzu tashi mubar wajen nan mushiga ɗaki kaga dare ya tsala”.

Kai ya gyaɗa mata tare da cewa.
“Toh”,Kana yabi bayanta tare da tsira mata idanu cike da ɗumbin mamaki tare da tarin tuhuma ahankali ya sake kallon sulallan Gwal ɗin dake haɗe da waɗanan sanduna guntaye aciki asaman laɓɓansa yayi sallama tare da shiga ɗaki.
Wutan ɗakin Innayi ta kunna Atake haske ya zagaye ɗakin bayan Moddibo ta ratsa tare da rufe kofar ɗakin kana ta dawo kusa dashi ta tsaya tare da sanya hannunta ta tsistsince ƴan guntulayen sandar ta shiga haɗawa kasancewar akwai wajen haɗawa ajiki Moddibo kuwa Idanu ya zuba mata cike da mamaki.
tana cigaba da haɗawa ga mamakinsa sai yaga ya zama sanda irin wanda manyan Limamai ke riƙe wa suna tafiya dashi sanda ce mai masifar kyau da tsari wacce da ka gani kasan mai tsadace.

Kallonsa Innayi tayi tare da cewa.
“Wannan sanda ce samansa inda ake riƙewa ne kaɗai keda Gwal sai kuma ƙasan sa inda ake dogara wa amma wannan bazan baka shiba saboda ba zaiyi daraja sosai ba. Saboda ahaɗe yake da sanda kana sandar kuma bazan siyar ba, sulallan dai zaka haɗa ka duba sai dai sunzo mana alokacin da bashine ba saboda sulallan baki ɗaya sun ƙare”.
Ido kawai Moddibo ya zuba mata still da shock atare dashi.
Innayi ta cigaba da cewa.
“Baki ɗaya nauyin karatunka.
Cin mu, shan mu, suturar mu, tun kana ƙarami da duk wani abinda ya kama su nake ɗauka in siyarwa Alhaji Hashim mai sayan gwala-gwalai shiyasan farashin sulallan duk yanda suke zan faɗa masa adadin da suke yazo ya siya muyi lissafi muga nawa za'a samu”.
Kai Moddibo ya gyaɗa tare da cewa.
“Toh shikenan”.Yayi mgnar tare da lumshe idanunsa, baki ɗaya damuwarsa asamu kuɗin bawai tunaninsa ya tambayi ina tasamu gwala-gwalan nan ba sannan bashida kuzarin da zai iya tambayar ta, sandar na menene, kana bashi da ƙarfin zuciyar jin mai yasa baza asayar da sandar ba, ayanzu burinsa bai wuce asamu ahaɗa kuɗaɗen akarɓo J ba.
Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da kallon Innayi kana yace.
“Toh zan tafi dasu ɗakina”.
Kai ta gyaɗa masa kana ya miƙe ya fita yana jin confidence da farin ciki yasan Gwal nada daraja duk da cewa ƴan ƙananun sulallane amma yasan da izinin Ubangiji zasuyi daraja.

Acan gidan Abba kuwa bayan tafiyar Moddibo Hajiya Karima ta kalli Abba daya zurfafa acikin tunani kana ta ɗan ya mutse Fuska tace.
“Alhji wai yanzu baza ka sake ƙara neman ragi ba? yanzu sai ka ɗauki Million ɗari da hamsin ka basu mai kake tunanin zai faru gaba idan sunji daɗi za'a sake ɗaukan ƴaƴanka ne fa!”.
Anutse Abba ya ɗago kansa tare da kallonta kana cikin sanyin Murya yace.
“Karima to me kike tunani?”.
Ba yabo ba fallasa tace.
“Ka nemi ragi”.
furzar da iska mai zafi yayi still Idanunsa na kanta kana yace.
“Karima kamar baki ji me yace ba, cewa fa yayi muddin aka nemi ragi akan rayuwar Jameel”.
Chapter 97 · 0% Book details