← Book details Sakayyah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 36 OF 114

Sashe 36

Sakayyah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Samira Sani kuwa tana shiga ajinsu ta lumshe Idanunta tare da kallon gefen ko wannen kujera dake ɗauke da flowes ta saki murmushi mai cike da jin daɗi,
tasan wannan aikin Moddibo ne domin kaf cikin Malaman shike son flowers.
Hajia Ruƙayya ce ta dubi Samira data shigo kana tace.
“Ni kam ya banga Khausar ta shigo ba har yanzu kuma ɗazu na hangota kafin na haura”.
Juye Ido Samira tayi tare da faɗin.
“Tana can tayiwa Moddibo rashin kunya yana cin Ubanta, shegiyar yarinya fitsararriya ‘yar marasa tarbiyya!".

Asma'u ce ta juya ta kalleta rai a haɗe tace.
“Haba Samira meyesa zaki zagi iyayenta ai bai kamata ki zagi iyayenta komai yaya iyaye nada daraja”.
Harara Samira ta wurga was Asma'u kana ta buɗe baki da niyyar magana ta fasa sakamakon shigowar Moddibo.

Ganin shigowar Moddibo yasa ta tsuke bakinta tare da neman waje ta zauna cike.
Cike da ladabi suka gaishesa cikin harshen larabci tare da faɗin.
”صبحل خير ىاعثتذ“
Ya Amsa da.
“صبحل نور كىفل قراء“.
Suka amsa da.
”الحمد الله“
Kasancewar Tafseer zasuyi dake yanzu lokacin Islamiyya ne yasa yace.
“Kuyi muraja”.
Cikin bawa ko wanne harafi hukuncinsa suka shiga karanta suratul Muhammad har zuwa karshe.
Bayan sun gama kawo haddan ya jinjina kai tare da faɗin.
“Sai gobe Insha Allah zamu fara tafsirin sa”.

Aɓangaren M Jameel kuwa tare suka jera da Amina suka nufi ajinsu yayin da azuciyar Amina yayi baƙiƙƙirin data tuna yanda M Jameel ke karyar da murya akan Khausar har suka isa ajin tunanin da take aranta kenan yanayin yanda tsarin ajinsu Khausar yake haka ko wanne aji yake cike da ƙwarewa M Jameel ya shiga yi musu ƙarin Mi'atu Hadith daga na Arba'in bayan sun karanta masa.
Ko wanne aji da Malami aciki suna darasi.

Ita kuwa Khausar ita kaɗai ce tsaye aharabar Makarantar cikin gajiyawa ta ɗaga boket ɗin ruwan ta koma rana wai ko zata samu yafi bushewa da wuri, tsoma ɗan kwalin tayi aciki kana ta matse sannan ta fara kaɗewa.
Nannauyan ajiyar zuciya ta saki tun akaɗewa na uku taji hannunta ya sage aranta tace.
“Insha Allah Ina komawa gida zan nemi ɗankwali mai shara-shara mara nauyi wanda kodan irin rana ta yau ta faru zaimin sauƙi.
Cike da gajiya ta miƙe ta riƙe ƙugunta da hannu ɗaya ta lumshe idanunta sosai ta gaji.

Shi kuwa Moddibo daga can sama acikin ajinsu Khausar yake kallonta tana kaɗe-kaɗen ganin ta tsaye ta riƙe ƙugu gaban ƙirjinta duk ya jiƙe da fuskanta, ganin ta tsayanne yasa ya buɗe glass ɗin window dake saitin ta tare da ziro hannunsa ya ƙyasta yatsunsa da ƙarfi wanda hakab yaja hankalin Khausar da saurin ta ɗaga kanta.
Ganin abinda yayi yasa da sauri ta cigaba da kaɗewa tana mai rintse Idanunta.

Har Moddibo ya gama teaching ɗinsa ya fita Khausar nakan punishment Koda ya saƙƙo ya ganta Harara ya watsa mata kana a kufule yace.
“Ba zaki shiga ajiba yau har sai kin gama abinda nasaki”.
Fuska ta Shagwaɓe tare da langwaɓar da kai tace.
“Ayyah Malam dan Allah kayafemin duk ɗan Adam ajizine!”.
Harara ya watsa mata ya wuce batare daya bata amsa ba,
bayansa tabi da kallo tana tura ƙaramin bakinta, to har wani malami ya sake shiga yayi darasi Khausar bata gama ba sai sha biyu dai-dai lokacin tashin matan Aure sannan Yara da ‘Yan mata suyi suci abinci su koma ajin boko.

Hajiya Ruƙayya ce da Aunty Khadija ne suka fito tare da ƙarasawa kusa da Khausar dai-dai lokacin da Khausar ke faɗin.
“Wayyo hannuna”.
Ta faɗa tana matsa yatsunta dake raɗaɗi.

Dafata Hajiya Ruƙayya tayi kana tace.
“Ayyah sannu Khausar kece bakyaji me kika yiwa Moddibo!?”.
Langwaɓar da kai Khausar tayi tare da marairaice murya tace.
“Allah babu abinda na masa kawai ina tahowa ne mukayi karo dashi har System ɗinsa ya faɗi kuma ma naji malam Jameel yace System ɗin beyi komai ba amma sai da ya sani wannan kaɗe-kaɗen sabida in baici zalina ba baya jin daɗi rayuwarsa ta duniya”.
Ta ida maganar da faɗin.
“Affan zo”,tare da miƙa masa hannu.
Murmushi Aunty Khadija tana mai jujjuya kai.
Ita kuwa Hajia Rukayya
Miƙa mata yaron dake ta faman ƙyalƙyala mata Dariya Aunty Ruƙayya tayi Sai kuma tayi saurin janye hannunta tana cewa.
“Wayyo Aunty Ruƙayya hannu na ya gaji yaukam bazan iya riƙe sa ba”.
Ta ƙare mgnar tana ƙara matsowa kusa da Aunty Ruƙayya kan kumatunsa ta sumbata tana faɗin.
“Affan gaye".
Shi kuwa yaron sai dariya yake ƙyalƙyala mata tare da miƙa mata hannu alamar yana so ta ɗauke sa dan sosai yaron ya saba da ita saboda Aunty Ruƙayya na zumunci da Mommy Khausar sannan Khausar na shiga lokaci zuwa lokaci.

Samira Sani da Abeeda Sule ne suka ƙaraso wajen Kallon Abeeda Sule Samira tayi da faɗin.
“Ai Moddibo shike maganin tantirai marasa mutunci ’ya'yan Fitsararru awannan makarantar yana min dai-dai!”.

Sake hannun Affan Khausar tayi ta juya ta kalli Samira da kyau tace.
“Waye ‘Yar marasa mutuncin?
Akwai ‘Yar marasa mutunci daya wucike ne ‘Yar magulmata Munafuka kawai! Inbanda munafurci da gulma da biye-biyen bokaye Me kuka iya!?”.
Afusace tace.
“Ke Khausar zanci Ubanki fa!".
Wara ido Khausar tayi kana tace.
“Ubana kuma, uhmm saide Kici naki uban domin ni kam nawa Ubana tuni Ubangiji ya daɗe da yimasa sutura sai dai kije kici naki ‘Yar matsiyata?”.
Ta ida mgnar cikin tsiwa,.

Abeeda Sule ne tace.
“Ke akwai ma ƴar matsiyata irinki, kina tsammanin bamu san cewa munsan ke Agwola bace acikin gidan sarki da kike nunawa kamar gidan ku ne?”.

Dariya Khausar tayi kana tace.
“Dan Allah rufe mana baki ‘Yar Alhaji sule baka layya kibari tukunna in Babanki ya fara layya saiki faɗa wa mutane Magana?”.

Zare ido Abeeda tayi tare da hayayya ƙowa tace.
“ ‘Yar iska ni zaki cewa Ubana baya layya”.
Taɓe baki Khausar tayi tare da faɗin.
“Ke rufe min baki ai bani na faɗa ba Inkiyarsa ce hakan, ko ba sunan sa bane? Alhaji Sule baka layya!! ko kuma ni nasa masa ko kuma dan tsoronki sai inki kiransa da sunan da aka sa mishi”.

Hajiya Ruƙayya ce tace.
“Khausar rabu dasu”.
Gyaɗa kai tayi.
Ita kuwa Samira cikin takaici tace.
“ ‘Yar banza kawai agola”.
Dariyar rainin hankalin Khausar tayi sannan tace.
“Eh koma menene inma ni Agolace inada daraja sannan ina da tushe dama ni ban ɓoyewa cewa Agola bace Ni saboda idan kinga sunan su Amina da sunana kin san ba yar gidan bane,
Ni sunana Khausar Usman Abubukar Lelewal sukuwa kinga ba haka sunan su yake ba daga nan ma mutum yasan Ni Agola ce ko dama anɓoye miki ne?”.

Hannunta Hajiya Ruƙayya taja suka bar wajen zuwa gefe tace.
“Khausar kifita har ƙansu kiyi abinda ke gabanki kinga duk yau baki samu karatu ba”.
Kai Khausar ta gyaɗa mata sannan tayi mata Sallama ta tafi.
Asma'u ce ta ƙaraso wajen Idanunta akan Samira da Abeeda dake zagin Khausar cikin yanayin sanyin muryanta tace.
“Khausar kifita sabgar wa'annan yaran dan Allah keda su ba ɗaya bane kada ki ringa biye musu muta nen da ƙwaƙwalensu basa ja, kinga fa yanzu da ya kamata suna SS 3 nefa daƙiƙancinsa kesa kullum basa gaba sunan a jaɓe har muka isosu”.
Yamutse fuska Khausar tayi kana tana matsa yatsun hannunta tace.
“Kinsan Allah Asma'u Indai basu fita sabgata ba zan basu mamaki zan nuna musu Khausar Usman Abubakar Lelewal ba kanwar lasa bace”.

Hannunta Asma'u ta riƙe tace.
“Ni dai dan Allah ki fita sangarsu ai ko kare bai haushi shi kaɗai tukunna wai me kika yiwa Moddibo ya saki Punishment?”.

Rau-rau da ido Khausar tayi sai kuma ta ya mutse fuska tare da jan tsaki kana tace.
“Mutum yana nan kamar wani sabon boss sam fuskarsa babu fara'a yana nan sai baƙin mugunta.
Kuma wallahi Wuta bal-bal ban yafe masa ba, ai bani kaɗai nayi kuskuren ba shima yayi yana tafiya kamar makaho, kuma yaseen saƙo na baki ki faɗa masa ehe”.
Ta ida mgnar cike da tsiwa da murguɗa baki
Asma'u kuwa dariyar dake cinta ta danne kana tace.
“Aikuwa gashi nan abayanki yana ma jinki ba sai na faɗa masa ba”.
Arazane Khausar ta saki ihu tare da rintse Idanunta cikin tsananin tsoro da rawan jiki ta juya tana mai faɗin.
“Dan Allah! Dan Allah!! Dan Allah!!! kayi haƙuri Allah bada kai nake ba kuskuren harshene ni da kainama nakeyi”,
Ta ida maganar tana buɗe Idanunta jin be tanka taba ga mamakinta bata gansa ba.
Kallon Asma'u tayi wacce zuwa lokacin ta saki dariyar ta tace.
“Fattanah sarkin tsiwa dama gwada ki nayi inga da gaske saƙon kika bani”.

Harara Khausar ta zabga wa Asma'u amma batace Komai ba.
Murmushi Asma'u tayi tare da jan hannunta zuwa resting chair dake cikin harabar makarantar suka zauna Asma'u ta fito da kula da ɗauke da pride rice da yaji kayan hadi da namar kaza suka ci.
Bayan sun gama cin wannan Khausar ta buɗe bata kukan.
Peper checking ne guzurin zabbin data dawo dasu.
Sunaci suna ɗan hirarsu dai har suka gama, suka mike tare da zagaya classes din makarantar suna kallon yanda aka tsara makarantar kamar ba shiba.
12:10 suka koma aji.
Bayan komawar su Malam Isa dake ɗaukar su Economist ya shiga ya koyar musu sosai Khausar da Asma'u ke fahimtar karatun 1:15 dai-dai suka fita sallah.

Bayan sun fita Al'wala sukaje wajen da aka tanada dan alwala sukayi gefen maza da ban na mata da ban Amma masallacin guda daya ne saidai anraba daga tsakiya anyi katanga mata zasu shiga ta gefen dama maza tagefen hagu.
Bayan sun idar da Sallah ƙarfe 1:30 suka koma aji wasu Malaman suka sake shiga.
Sosai Malaman suka dage wajen koyar dasu domin anƙara musu Salarie sannan ankawo sabbin Malamai hakan yasa babu period din dake wucewa ba tare da anshiga ba 5:00 dai-dai suka tashi motar su Khausar tazo ta ɗauke su.
Chapter 36 · 0% Book details