Sashe 43
Sakayyah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Acan gida kuwa tun bayan tafiyar su Khausar Makaranta cikin Mommy ya tsananta da ciwo da ƙyar ta yunƙura ta miƙe tana mai rintse Idanunta jini taga yana bin ƙafafunta da sauri ta dafe cikinta da ƙyar ta iya furta.
“Ya Allah wannan ciwon cikin kuma na menene?”.
Da ƙyar taja ƙafanta zuwa jikin beside drawer ta ɗaga wayarta tare da kiran number Hajiya Bunayya, kafin ya katse Hajiya Bunayya tayi picking tare da Sallama.
Mommy kuwa cikin azaban ciwon da cikinta ke mata ta rintse Idanunta kana tace.
“Yaya”.
Da sauri Hajiya Bunayya ta katseta da faɗin.
“Ƙanwata lafiya naji muryanki haka?”.
cike da yarda ta rintse Idanunta cikin yanayin azaban ciwon da cikinta keyi tace.
“Wallahi Yaya cikina ciwo yake tun daren jiya, haka na kwana banyi bacci ba yanzu kuma gashi jini ya ɓalle min!
Dan Allah ki faɗawa Alhj mutafi asibiti”.
Hajiya Bunayya kuwa da damuwa amuryanta tace.
“Subhanallahi! bari na faɗa masa yanzu ma kuwa”.
Sannan ta katse wayar ta nufi ɗakin Lamiɗo ranta fari Sol burinta ya cika abakin ƙofa suka haɗu yana shirin fita.
A take ta wani marairaice fuska kana cikin yanayin damuwa tace.
“Yanzu Mommyn Khausar ta kirani.
Wai jiya da ciwon ciki ta kwana yanzu kuma jini ya ɓalle mata”.
Ai bai ma gama sauraron abinda zata faɗa ba ya ratsa ta ya wuce sashen Mommy cike da damuwa.
Hajiya Bunayya kuwa da harara tabi bayansa kafin taja siririn tsaki ta mara masa baya.
Tana shiga Bedroom ɗin ta samu Lamiɗo tsugunne akan Mommy da sauri ta tsugunna daga gefensa ta riƙo hannun Mommy.
Cike da tausayawa kamar za tayi kuka tace.
“Sannu Aysha ciwon ciki amma baki yi magana ba, gashi har ya tsananta jini na zuba”.
Ta ida maganar zufa na karyo mata wanda in kagani zakayi zaton na tsananin damuwa ce, nan kuwa na tsananin farin cikin burinta ya cika ne.
Lamiɗo kuwa miƙewa yayi tare da naɗe hannun rigarsa zai ɗauke ta Ganin haka ne yasa Hajiya Bunayya tayi saurin miƙewa tare da tallafo Mommy jikinta suka fita,
agidan baya suka zauna Lamiɗo kuma ya shiga gefen mai zaman banza Driver yaja suka tafi Hajiya Bunayya sai faman sannu take yiwa Mommy.
Suna isa asibitin aka karɓe su kai tsaye emergency aka nufa da ita ganin cikin ya riga ya zube yasa likitoci suka nufi wani ɗaki da ita tare da yi mata wankin ciki kana suka yi mata allurai nanda nan bacci wahala ya ɗauke ta Lamiɗo kuwa kasa Matsawa daga kusa da ita yayi ya cike da kulawa ya zauna a bakin gadon tare da riƙe tafin hannunta cike da tausayinta.
Hajiya Bunayya data shaƙa ta cika kuwa.
Wani lalataccen harara ta watsawa ƙeyansa cikin ranta tace, tabbas sai tayi wani abu akan wannan rawan jikin da yake mata.
A zahiri kuwa dafa kafaɗar sa tayi, ahankali ya ɗago kansa ya kalleta da idanunsa dake cike da damuwa amma baice komai ba.
Cike da kirsa ta ƙirƙiri murmushin da bai kai zuciba kana tace.
“Dan Allah ka rage damuwar nan, babu yanda zamuyi da ƙaddara haka Ubangiji ya tsara wannan ɗin ma ba rabo bane, ayanzu addu'ar lafiya take da buƙata awajenmu”.
A hankali ya sauƙe nannuyar Ajiyar zuciya tare da mayar da Kallonsa ga Mommy dake bacci tamkar babu abinda ke damunta.
Lumshe idanunsa yayi yace.
“Ina matuƙar tausayawa Aysha tun bayan haihuwar Haiydar take fama da wannan matsalar sannan ko wanne cikin sai ya wahalar da ita kafin ya fita”.
Da sauri Hajiya Bunayya ta katsesa da faɗin.
“Ya zamuyi da rubutacciyar ƙaddara, ai kaga da Ubangiji yaga dama ai cikin Raudat da Ramadan ya zauna”.
Kai ya jinjina amma baice komai ba.
Ita kuwa cikin ɓoye farin cikinta ta sauƙe ajiyar zuciya da faɗin.
“Zan koma gida kafin ‘yan makaranta su dawo, naga lokaci yaja amma Insha Allah anjima zan dawo”.
Kai ya gyaɗa ba tare da yace komai ba still Idanunsa na kan Mommy.
Hajiya Bunayya kuwa ficewa tayi ranta fari fess kana tasa Driver ya maida ta.
Acan Makarantar su Khausar kuwa koda suka gama Exam ba abasu damar tafiya ba bayan sunyi sallar la'asar suka shiga haddar Alkur'ani sai ƙarfe biyar aka tashe su, kana suka shigo mota suka nufi gida, motar na parking Raudat ta fice da gudu ta nufi sashen su
Tana shiga falo ta fara kiran.
“Mommy! Mommy!! na mun dawo”.
Jin shiru yasa ta nufi Bedroom ɗinta da gudu ta buɗe ta shiga tana kiran.
“Mommy!, Mommy!!, Ina kika shiga”.
Still Bata ganta ba da gudu ta juya ta fito falon dai-dai lokacin Khausar kuma ta shigo ƙara sawa kusa da Khausar tayi ta riƙe hannunta kana tace.
“Addah Khausy Ina Mommy?”.
Kallonta Khausar tayi kafin tace.
“Bata ɗaki ne?”.
Kai Raudat ta gyaɗa mata alamar Eh,
Sake hannunta Khausar tayi kana ta nufi kichen ta buɗe wayam tagani alamar bata nan komawa tayi ta shiga Bedroom din ta ɓude still ba tanan jikin toilet ta nufa ta manna kunnenta ajiki tare da faɗin.
“Mommy Mommy kina ciki kuwa?”.
Jin shiru yasa ta tura ƙofar toilet din still bata nan fitowa tsakiyar falon Khausar tayi tare dasa hannun damanta ta riƙe ƙugunta tana tunanin ina Mommy ta shiga haka, bayan tasan bata fiye fitar yamma ba kuma koda zata fita tun safe kafin su tafi makaranta zata faɗa musu bare kuma yau da suka barta bata jin daɗi.
Da sauri ta kalli Raudat sai kuma tace.
“Jirani anan ina zuwa”.
ta faɗa tare da ficewa kai tsaye sashen Hajiya Bunayya ta nufa bakinta ɗauke da sallama tana faɗin.
“Ummah”.
Shigar ta yayi dai-dai da lokacin da Hajiya Bunayya ke riƙe da waya tana cewa.
“Kedai Hajiya Lami bari buƙata ɗaya ta biya saura ɗaya, tana can kwance a asibiti cikin ya zube yabi makwarari, saura ɗayan daman jira nake inga ya zata kaya ne ki shirya jibi zamu koma”.
Komai Hajiya Lami ta faɗa ohon musu, ita dai Hajiya Bunayya cikin jin dadi ta kece da wata mahaukaciyar dariya mai nuni da tsantsar farin ciki.
Lokaci ɗaya kuma dariyar nata ya tsaya ganin Khausar tsaye, sai kuma ta katse kiran tare da kallon Khausar.
Kafin tace wani abu Khausar tayi saurin cewa.
“Ummah ina Mommy mu?”.
Hajiya Bunayya ta wani langwaɓar da kai kana tace.
“Ayyah Khausar am Mommy ku tana asibiti bata da lafiya wallahi cikinta ya zube”.
Da sauri Khausar da kanta ke ƙasa ta ɗago ta kalli Hajiya Bunayya tana sake maimaita kalmar cikinta ya zube akasan ranta lokacin ɗaya hawaye masu zafin gaske suka cika kwarmin Idanunta.
Sai kuma tayi saurin maida hawayen ta kafin tace.
“Shikenan ɓuƙatar magauta tabiya hankali ya kwanta. Allah ya raya mata wa anda ta haifa. Ubangiji ya tsaresu daga sharrin mai sharrin”.
Ta ida maganar tana ƙoƙarin fita.
Da sauri Hajiya Bunayya tace.
“Ke Khausar zo nan Me kike nufi?”.
Anutse Khausar ta juya tare da sauƙe manyan Idanunta da suka sauya launi zuwa ja ta zubawa Hajiya Bunayya kana tace.
“A'a Ummah babu abinda nake nufi, kawai dai addu'a ce nayi”.
Cikin tsuke fuska Hajiya Bunayya ta watsa mata Harara da faɗin.
“Sannan su waye ne Magautan?”.
Ware hannu Khausar tayi tare da faɗin.
“Nikam ban sansu ba, amma dai nasan Allah Mabuwayi gagara Misali ya sansu kuma zaiyi maganin su, domin ai bahaushe yace rana dubu ta ɓarawo rana ɗaya ta mai kaya, suji tsoron ranan da Ubangiji zai musu kamun talala!”.
Cike da Mamaki Hajiya Bunayya tace.
“Wai Khausar me kike magana kamar habaici kike min ko kuma hannunka mai sanda!?.”
Ware ido Khausar tayi tace.
“Haba Ummah in Miki habaici kuma ayanda kike ƙaunar Mommyn mu kinfi ƙarfin habaici ko hannunka mai sanda kin wuce haka sai dai mgnar ce tazo kamar zaurance”.
Ɓoyeyyen Ajiyar zuciya Hajiya Bunayya ta saki domin tayi zaton yarinyar ta gano lagonta ne.
Khausar kuwa murmushi tayi tare da faɗin.
“Bari na tafi asibitin kar dare yayi”.
Da sauri Hajiya Bunayya ta gyara zamanta Idanunta akan Khausar tace.
“Toh kibari in ƙara sa abinci mana sai ki tafi dashi”.
Kai Khausar ta gyaɗa da faɗin.
“Toh amma bari na shiga gidan Aunty Ruƙayya kafin ki ƙarasa”.
Kai Hajia Bunayya ta gyaɗa tare da faɗin.
“Toh ki gaisheta”.
Kai kawai Khausar ta gyaɗa Sannan ta wuce sashen su.
Tana shiga Bedroom direct toilet ta wuce ta cire Uniform ɗin ta sannan ta watsa ruwa bayan ta fito ta dauki dogon rigar material pinch colour ta sanya, kana ta nufi kichen Agurguje ta dafawa su Haiydar jollof ɗin shin kafa da yaji bushesh-shen kifi da kayan ƙamshi nan da nan kichen ɗin ya ɗauki ƙamshi Warmers ta ɗauka ta juye sannan ta tafasa musu tea kana ta ɗura musushi, sannan ta fita falon dai-dai lokacin da Haiydar ya shigo.
Kallonsa Khausar tayi tare da kiran sunansa tace.
“Haiydar”.
Ya amsa da.
“Na'am”.
Cikin sanyi tayi ƙasa da muryanta tare da faɗin.
“Dan Allah Haiydar ka kwana anan kai da Ramadan, Raudat kuma zamu tafi da ita asibiti sai mu kwana da Mommy”.
Kai ya gyaɗa mata sai kuma yace.
“Nima ai inaso naje na dubata”.
Jinjina kai Khausar tayi tace.
“Ba damuwa kazo mutafi dukan mu amma yanzu zan fara shiga gidan Aunty Ruƙayya in sanar mata, idan yaso kai da Ramadan ku taho tare da Ummah,
In yaso sai ku dawo tare amma kubar min Raudat dan zamu kwana tare”.
“Toh shikenan Allah ya bata lafiya”.
“Ameen”,
Tace kana ta juya ta tafi har ta kusa fita ta sake juyawa ta kalli Haiydar dake tsaye Ahankali tace.
“Dan Allah Haiydar ka kula, bakomai za'a baka kaci ba, akwai abinci na dafa muku sannan duk wani abu da zaku buƙata akwai”.
Da sauri ya dafe kansa tare da faɗin.
“Ke dai jeki da rashin yardan ki kedai haka Allah ya halicce ki baki da yarda”.
Cikin sanyi ta girgiza kai kana tace.
“Shikenan ni dai ban san sai yaushe zaku yarda dani ba”.
Ta ida maganar tare da ficewa”.
Kai tsaye gidan Aunty Ruƙayya ta nufa.
Tare da Sallama tashiga Babban falon da yaji kayan alfarma kujerun set biyu aciki Black and Ash sai kuma babban tv plasma dake Manne abango daga ƙasansa kuma horm teater ne ƙasan falon kuma shimfiɗe yake da chanis capet.
“Ya Allah wannan ciwon cikin kuma na menene?”.
Da ƙyar taja ƙafanta zuwa jikin beside drawer ta ɗaga wayarta tare da kiran number Hajiya Bunayya, kafin ya katse Hajiya Bunayya tayi picking tare da Sallama.
Mommy kuwa cikin azaban ciwon da cikinta ke mata ta rintse Idanunta kana tace.
“Yaya”.
Da sauri Hajiya Bunayya ta katseta da faɗin.
“Ƙanwata lafiya naji muryanki haka?”.
cike da yarda ta rintse Idanunta cikin yanayin azaban ciwon da cikinta keyi tace.
“Wallahi Yaya cikina ciwo yake tun daren jiya, haka na kwana banyi bacci ba yanzu kuma gashi jini ya ɓalle min!
Dan Allah ki faɗawa Alhj mutafi asibiti”.
Hajiya Bunayya kuwa da damuwa amuryanta tace.
“Subhanallahi! bari na faɗa masa yanzu ma kuwa”.
Sannan ta katse wayar ta nufi ɗakin Lamiɗo ranta fari Sol burinta ya cika abakin ƙofa suka haɗu yana shirin fita.
A take ta wani marairaice fuska kana cikin yanayin damuwa tace.
“Yanzu Mommyn Khausar ta kirani.
Wai jiya da ciwon ciki ta kwana yanzu kuma jini ya ɓalle mata”.
Ai bai ma gama sauraron abinda zata faɗa ba ya ratsa ta ya wuce sashen Mommy cike da damuwa.
Hajiya Bunayya kuwa da harara tabi bayansa kafin taja siririn tsaki ta mara masa baya.
Tana shiga Bedroom ɗin ta samu Lamiɗo tsugunne akan Mommy da sauri ta tsugunna daga gefensa ta riƙo hannun Mommy.
Cike da tausayawa kamar za tayi kuka tace.
“Sannu Aysha ciwon ciki amma baki yi magana ba, gashi har ya tsananta jini na zuba”.
Ta ida maganar zufa na karyo mata wanda in kagani zakayi zaton na tsananin damuwa ce, nan kuwa na tsananin farin cikin burinta ya cika ne.
Lamiɗo kuwa miƙewa yayi tare da naɗe hannun rigarsa zai ɗauke ta Ganin haka ne yasa Hajiya Bunayya tayi saurin miƙewa tare da tallafo Mommy jikinta suka fita,
agidan baya suka zauna Lamiɗo kuma ya shiga gefen mai zaman banza Driver yaja suka tafi Hajiya Bunayya sai faman sannu take yiwa Mommy.
Suna isa asibitin aka karɓe su kai tsaye emergency aka nufa da ita ganin cikin ya riga ya zube yasa likitoci suka nufi wani ɗaki da ita tare da yi mata wankin ciki kana suka yi mata allurai nanda nan bacci wahala ya ɗauke ta Lamiɗo kuwa kasa Matsawa daga kusa da ita yayi ya cike da kulawa ya zauna a bakin gadon tare da riƙe tafin hannunta cike da tausayinta.
Hajiya Bunayya data shaƙa ta cika kuwa.
Wani lalataccen harara ta watsawa ƙeyansa cikin ranta tace, tabbas sai tayi wani abu akan wannan rawan jikin da yake mata.
A zahiri kuwa dafa kafaɗar sa tayi, ahankali ya ɗago kansa ya kalleta da idanunsa dake cike da damuwa amma baice komai ba.
Cike da kirsa ta ƙirƙiri murmushin da bai kai zuciba kana tace.
“Dan Allah ka rage damuwar nan, babu yanda zamuyi da ƙaddara haka Ubangiji ya tsara wannan ɗin ma ba rabo bane, ayanzu addu'ar lafiya take da buƙata awajenmu”.
A hankali ya sauƙe nannuyar Ajiyar zuciya tare da mayar da Kallonsa ga Mommy dake bacci tamkar babu abinda ke damunta.
Lumshe idanunsa yayi yace.
“Ina matuƙar tausayawa Aysha tun bayan haihuwar Haiydar take fama da wannan matsalar sannan ko wanne cikin sai ya wahalar da ita kafin ya fita”.
Da sauri Hajiya Bunayya ta katsesa da faɗin.
“Ya zamuyi da rubutacciyar ƙaddara, ai kaga da Ubangiji yaga dama ai cikin Raudat da Ramadan ya zauna”.
Kai ya jinjina amma baice komai ba.
Ita kuwa cikin ɓoye farin cikinta ta sauƙe ajiyar zuciya da faɗin.
“Zan koma gida kafin ‘yan makaranta su dawo, naga lokaci yaja amma Insha Allah anjima zan dawo”.
Kai ya gyaɗa ba tare da yace komai ba still Idanunsa na kan Mommy.
Hajiya Bunayya kuwa ficewa tayi ranta fari fess kana tasa Driver ya maida ta.
Acan Makarantar su Khausar kuwa koda suka gama Exam ba abasu damar tafiya ba bayan sunyi sallar la'asar suka shiga haddar Alkur'ani sai ƙarfe biyar aka tashe su, kana suka shigo mota suka nufi gida, motar na parking Raudat ta fice da gudu ta nufi sashen su
Tana shiga falo ta fara kiran.
“Mommy! Mommy!! na mun dawo”.
Jin shiru yasa ta nufi Bedroom ɗinta da gudu ta buɗe ta shiga tana kiran.
“Mommy!, Mommy!!, Ina kika shiga”.
Still Bata ganta ba da gudu ta juya ta fito falon dai-dai lokacin Khausar kuma ta shigo ƙara sawa kusa da Khausar tayi ta riƙe hannunta kana tace.
“Addah Khausy Ina Mommy?”.
Kallonta Khausar tayi kafin tace.
“Bata ɗaki ne?”.
Kai Raudat ta gyaɗa mata alamar Eh,
Sake hannunta Khausar tayi kana ta nufi kichen ta buɗe wayam tagani alamar bata nan komawa tayi ta shiga Bedroom din ta ɓude still ba tanan jikin toilet ta nufa ta manna kunnenta ajiki tare da faɗin.
“Mommy Mommy kina ciki kuwa?”.
Jin shiru yasa ta tura ƙofar toilet din still bata nan fitowa tsakiyar falon Khausar tayi tare dasa hannun damanta ta riƙe ƙugunta tana tunanin ina Mommy ta shiga haka, bayan tasan bata fiye fitar yamma ba kuma koda zata fita tun safe kafin su tafi makaranta zata faɗa musu bare kuma yau da suka barta bata jin daɗi.
Da sauri ta kalli Raudat sai kuma tace.
“Jirani anan ina zuwa”.
ta faɗa tare da ficewa kai tsaye sashen Hajiya Bunayya ta nufa bakinta ɗauke da sallama tana faɗin.
“Ummah”.
Shigar ta yayi dai-dai da lokacin da Hajiya Bunayya ke riƙe da waya tana cewa.
“Kedai Hajiya Lami bari buƙata ɗaya ta biya saura ɗaya, tana can kwance a asibiti cikin ya zube yabi makwarari, saura ɗayan daman jira nake inga ya zata kaya ne ki shirya jibi zamu koma”.
Komai Hajiya Lami ta faɗa ohon musu, ita dai Hajiya Bunayya cikin jin dadi ta kece da wata mahaukaciyar dariya mai nuni da tsantsar farin ciki.
Lokaci ɗaya kuma dariyar nata ya tsaya ganin Khausar tsaye, sai kuma ta katse kiran tare da kallon Khausar.
Kafin tace wani abu Khausar tayi saurin cewa.
“Ummah ina Mommy mu?”.
Hajiya Bunayya ta wani langwaɓar da kai kana tace.
“Ayyah Khausar am Mommy ku tana asibiti bata da lafiya wallahi cikinta ya zube”.
Da sauri Khausar da kanta ke ƙasa ta ɗago ta kalli Hajiya Bunayya tana sake maimaita kalmar cikinta ya zube akasan ranta lokacin ɗaya hawaye masu zafin gaske suka cika kwarmin Idanunta.
Sai kuma tayi saurin maida hawayen ta kafin tace.
“Shikenan ɓuƙatar magauta tabiya hankali ya kwanta. Allah ya raya mata wa anda ta haifa. Ubangiji ya tsaresu daga sharrin mai sharrin”.
Ta ida maganar tana ƙoƙarin fita.
Da sauri Hajiya Bunayya tace.
“Ke Khausar zo nan Me kike nufi?”.
Anutse Khausar ta juya tare da sauƙe manyan Idanunta da suka sauya launi zuwa ja ta zubawa Hajiya Bunayya kana tace.
“A'a Ummah babu abinda nake nufi, kawai dai addu'a ce nayi”.
Cikin tsuke fuska Hajiya Bunayya ta watsa mata Harara da faɗin.
“Sannan su waye ne Magautan?”.
Ware hannu Khausar tayi tare da faɗin.
“Nikam ban sansu ba, amma dai nasan Allah Mabuwayi gagara Misali ya sansu kuma zaiyi maganin su, domin ai bahaushe yace rana dubu ta ɓarawo rana ɗaya ta mai kaya, suji tsoron ranan da Ubangiji zai musu kamun talala!”.
Cike da Mamaki Hajiya Bunayya tace.
“Wai Khausar me kike magana kamar habaici kike min ko kuma hannunka mai sanda!?.”
Ware ido Khausar tayi tace.
“Haba Ummah in Miki habaici kuma ayanda kike ƙaunar Mommyn mu kinfi ƙarfin habaici ko hannunka mai sanda kin wuce haka sai dai mgnar ce tazo kamar zaurance”.
Ɓoyeyyen Ajiyar zuciya Hajiya Bunayya ta saki domin tayi zaton yarinyar ta gano lagonta ne.
Khausar kuwa murmushi tayi tare da faɗin.
“Bari na tafi asibitin kar dare yayi”.
Da sauri Hajiya Bunayya ta gyara zamanta Idanunta akan Khausar tace.
“Toh kibari in ƙara sa abinci mana sai ki tafi dashi”.
Kai Khausar ta gyaɗa da faɗin.
“Toh amma bari na shiga gidan Aunty Ruƙayya kafin ki ƙarasa”.
Kai Hajia Bunayya ta gyaɗa tare da faɗin.
“Toh ki gaisheta”.
Kai kawai Khausar ta gyaɗa Sannan ta wuce sashen su.
Tana shiga Bedroom direct toilet ta wuce ta cire Uniform ɗin ta sannan ta watsa ruwa bayan ta fito ta dauki dogon rigar material pinch colour ta sanya, kana ta nufi kichen Agurguje ta dafawa su Haiydar jollof ɗin shin kafa da yaji bushesh-shen kifi da kayan ƙamshi nan da nan kichen ɗin ya ɗauki ƙamshi Warmers ta ɗauka ta juye sannan ta tafasa musu tea kana ta ɗura musushi, sannan ta fita falon dai-dai lokacin da Haiydar ya shigo.
Kallonsa Khausar tayi tare da kiran sunansa tace.
“Haiydar”.
Ya amsa da.
“Na'am”.
Cikin sanyi tayi ƙasa da muryanta tare da faɗin.
“Dan Allah Haiydar ka kwana anan kai da Ramadan, Raudat kuma zamu tafi da ita asibiti sai mu kwana da Mommy”.
Kai ya gyaɗa mata sai kuma yace.
“Nima ai inaso naje na dubata”.
Jinjina kai Khausar tayi tace.
“Ba damuwa kazo mutafi dukan mu amma yanzu zan fara shiga gidan Aunty Ruƙayya in sanar mata, idan yaso kai da Ramadan ku taho tare da Ummah,
In yaso sai ku dawo tare amma kubar min Raudat dan zamu kwana tare”.
“Toh shikenan Allah ya bata lafiya”.
“Ameen”,
Tace kana ta juya ta tafi har ta kusa fita ta sake juyawa ta kalli Haiydar dake tsaye Ahankali tace.
“Dan Allah Haiydar ka kula, bakomai za'a baka kaci ba, akwai abinci na dafa muku sannan duk wani abu da zaku buƙata akwai”.
Da sauri ya dafe kansa tare da faɗin.
“Ke dai jeki da rashin yardan ki kedai haka Allah ya halicce ki baki da yarda”.
Cikin sanyi ta girgiza kai kana tace.
“Shikenan ni dai ban san sai yaushe zaku yarda dani ba”.
Ta ida maganar tare da ficewa”.
Kai tsaye gidan Aunty Ruƙayya ta nufa.
Tare da Sallama tashiga Babban falon da yaji kayan alfarma kujerun set biyu aciki Black and Ash sai kuma babban tv plasma dake Manne abango daga ƙasansa kuma horm teater ne ƙasan falon kuma shimfiɗe yake da chanis capet.