← Book details Sakayyah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 76 OF 114

Sashe 76

Sakayyah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ga masu buƙata ga number' wayata wanda nake whatsApp dashi 09097853276 kimin mgn ta whatsApp in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta, muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so.
0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk ƙasar da kike kayana zaije gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida.

GARKUWAR MA'AURATA

*By*
*GARKUWAN MARUBUTA*
[24/07, 6:14 AM] Halimatu A/rahman Sadeeya: Isreg'o. Cikin tsananin tsoro da mamaki Baba mai gadi ya juya gabas da yamma,r kudu da arewa acikin coumpund ɗin gidan amma babu mutum babu dalilin mutum, cikin tsananin kaɗuwa da ganin wannan abin al'ajabin yace.
“Innalillahi wa'inna Ilahi rajiu'n. Cikin abinda bai wuce second ɗaya ba ace babu rago babu dalilinsa, kuma abu ayanke bawai da ransa ba bare ace ya gudu”.
Cikin kaɗuwa ya nufi cikin gidan tare da cewa.
“Ya Ilahi mai ya faru”.
Duk ya burkice ganin abin yake tamkar mafarki dai-dai lokacin da mai gidan ƙanin Lamiɗo yake fitowa.
Aruɗe Baba mai gadi yace.
“Alhaji ragunan biyu suna ɗaure amma yanzu naga ba ɗaya”.
Kallon Mamaki Alhj Musa ya masa tare da cewa.
“A'a ragunan biyu yanzu kuma babu ɗaya ƙafa ragon yake dashi Malam Idi?.
Aruɗe Malam Idi yace.
“Wallahi tallalahi Alhj da gaske yanzu-yanzu ragonan yana nan amma yanzu ya ɓace babu shi babu dalilinsa”.
Tsayuwa Alhj Musa ya gyara tare da cewa.
“Toh ragon ƙafa zaiyi ina zai shiga?”,.
Malam Idi daya gama shiga tashin hankali yace.
“Wallahi da gaske Alhj”.
ya faɗa tare da juyawa ya fice daga gate ɗin ganin su Khausar basu yi nisa ba yasa ya saki Ajiyar zuciya tare da cewa.
“Khausar!, Khausar!! Kuzo”.
A tsorace Khausar da Asma'u suka jiyo atare kana suka haɗa baki wajen faɗin.
“Ya dai Baba mai gadi”.
Hannu ya ɗaga musu tare da cewa.
“Kuzo dai”.
Cikin rawan jiki da tsoro Khausar tace.
“Lafiya?”.
Cikin ƙasa da murya Asma'u tace.
“Mun shiga uku kad dai ya gane?”.
Da ƙarfi Khausar ta haɗiye wani abu mai ɗaci tare da cewa.
“A'a Insha Allahu ma bai gane ba”.
Suna isa bakin gate ɗin yace.
“Khausar kushigo”.
Ƙara sa shiga sukayi zuciyar su na bugawa da mugun sauri.
Kallonsu Baba mai Gadi yayi tare da kallon Alhj Musa kana yace.
“Dan Allah dan Annabi ba ragunan biyu suna nan ba, har kuka tsaya kusa dasu suna ɗaure ba?”.
Atsorace Khausar ta gyaɗa masa kai kana Muryanta na rawa tace.
“Eh”.
Da sauri Baba mai gadi ya sake kallon wajen tare da cewa.
“Kawai ina zaune fa kamar abin wasa kamar amafarki kamar a Tv naga rago ɗaya ya ɓace”.
Khausar da jikinta ya fara rawane tace.
“Ya ɓace kuma?”
Cikin tashin hankali Asma'u da Idanunta sukayi zuru-zuru ta dafe ƙirjinta tare da faɗin.
“Ya ɓace kuma dai?”.
Jinjina kai Baban mai gadi yayi tare da cewa.
“Wallahi kuwa kun fita kenan ina juyawa naga ragon nan ya ɓace Khausar abin nan abin mamaki fa ina kuma kun gansu?”.
Shi dai Alhj Musa na tsaye ya harɗe hannunsa aƙirji yana sauraransu cike da al'ajabi.
Cikin tsananin tsoro mamaki da al'ajabi da kaɗuwa gami da kiɗima Khausar ta kalli Alhj Musa kana tace.
“Wallahi kuwa Baba ƙarami muma munga ragunan nikam mafa akusa dasu na tsaya. Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n yau mun shiga uku Meye faru ya akayi haka?”.
Jin hayaniya yasa mata dake cikin gida suka fara fitowa suna tambayar abinda yafaru duk wanda yaji rago ya ɓace sai yashiga cikin mamaki da al'ajabi.
Baba mai Gadi da abin ya tsaya masa arai ya kalli mutanen dake wajen tare da cewa.
“Wallahi ganin Idona ragon nan ya ɓace ɓat kamar a Film kuma babu kowa a farfajiyar gidan Khausar suna fita abin ya faru ina juyawa naga sun ɓace ɓat!”.
Atsorace Khausar ta jinjina kai tare da cewa.
“Wallahi kuwa Muma yanzu muka gansu mun samu ragu nan nan aɗaure”.
Ana haka Mommy tashigo nan ta samu labarin rago ya ɓace nan suka shiga jajantawa.

Khausar kuwa hannun Asma'u taja suka fice bayan sun fita Asma'u ta juya ta kalli Khausar tare da cewa.
“Khausar”.
Juyawa Khausar tayi tare da haɗiye wani abu mai Masifar ɗaci tace.
“Asma'u”.
Asma'u taja dogon numfashi kana tace.
“Khausar da kece zaki ɓace fa. Innalillahi wa'inna Ilahi rajiu'n”.
Khausar kuwa da jikinta yake rawan jitayi Idanunta sun ciko da hawaye cike da alhini tace.
“Asma'u mun shiga uku”.
Cike da rawan jiki suka ƙarasa gida kai tsaye ɗakin Khausar suka nufa tare da zama a ƙasa Capet ɗin duk sunyi zuru-zuru dasu kallo ɗaya zaka musu kasan cewa suna cikin ɗimuwa da tashin hankali mara misaltuwa.
Cikin rawan murya Khausar ta kalli Asma'u tare da cewa.
“To yanzu kam Uncle Naseer me yake nufi dani? Dama tsafi zaiyi dani, kenan Uncle Naseer ma tsafi ne Asma'u? ba kingani ba dama ni sam ban yarda da shiba, tsoronsu nake dama Gimbiya Dadu ya take bare kuma ƙanwarta mun shiga uku dama tsafi zaiyi dani Asma'u shikenan da kashe ni suke sonyi?”.
Cikin raunin murya Asma'u tace.
“Khausar wannan abin ya gigita ni na rasa ta yanda zan fassara shi”.
Ta gumi sukayi yayin da zuciyarsu ta cigaba da bugawa tsoro da tashin hankali ya bayyana atare dasu lokacin ɗaya zazzaɓi ya fara dirarwa Khsusar.

Ba jimawa Mommy ta dawo kai tsaye ɗakin Khausar ta shiga tana cewa.
“Ohhh Allah mai iko an duba fa ƙasa da sama babu ragon nan babu dalilinsa an duba ko ina babu shi ya ɓace!”.
Murya na rawa Asma'u tace.
“Mommy muma fa mun gansu”.
Mommy kuwa ahankali ta maida kallonta kan Khausar da jikinta ke rawa duk ta ruɗe cike da kulawa tace.
“Khausar ya dai?”.
Kuka Khausar ta fashe dashi tare da yarfe hannu kana tace.
“Mommy zan faɗa miki Mommy zan faɗi gaskiya”.
Kallon Mamaki Mommy tayi mata kana tace.
“Meya faru Khausar?”.
Cikin kuka sosai Khausar tace.
“Allah Mommy Zan faɗi”.
Zama Mommy tayi gefensu kana tace.
“Wai meke faruwa ne Asma'u”.
Cikin ƙoƙarin tsaida hawayen Khausar ta riƙe hannun Mommy acikin nata, kana ta zayyane mata duk yanda sukayi da Naseer da kuma shawarar da Asma'u ta bata sannan ta ɗaura da cewa.
“Mommy kuma nice ɗazun na dandala ƙyallen akan wuyan ragon, har muka ji tsoro kar Baba mai gadi ya ganmu kuma Allah wanda na shafawa ƙyellen ne ya ɓace”.
Aruɗe Mommy ta saki salati tare da sanar da ubangiji.
_“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n. Hasbunallahu wani'imal wakil. La'ilah ha Illah anta subhanaka Inni kuntu Minal Zhalimin. Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan minha_. Ohh Khausar am nashiga uku wannan rayuwa har ina Khausar kin tabbatar?”.
Kai ta gyaɗa tare da faɗin.
“Wallahi tallahi Mommy da gaske ne”.
Ta faɗa tare da cusa hannunta ƙarƙashin gado ta ciro mata ƙyallen data ajiye da niyyar idan Naseer yazo zata bashi”.
Cikin raunin murya tace.
“Mommy kingani Mommy kin gani ko wallahi shine ƙyallen”.
Jinjina kai Mommy tayi tare da kallon ƙyallen da ƙamshinsa ke bugun kanta kana tace.
“Nashiga Uku ni Aysha wannan masifa har ina?”.
Asma'u kuwa ta gumi tayi ganin abin take tamkar almara.

Khausar na share hawaye tace.
“Mommy ina dai yanzu kin gani kinga zahiri Mommy inaga yanzu kam zaki iya yarda su Mayu neko?”.
Girgiza kai Mommy tayi cike da jimami da kuma al'ajabi ta kalli Khausar tare da cewa.
“Toh su sukayi ko shi Allah am nashiga uku ba'a shaidar halin ɗan mutum”.
Girgiza kai Asma'u tayi kana tace.
“Nikam wallahi Uncle Naseer ya bani Mamaki duk da rawan kansa ban taɓa zaton zai aikata irin wannan abin ba”.
Ta gumi Khausar tayi duk abin duniya ya isheta Hausawa sunyi gaskiya da suka ce Mutum mugun Icce.
Ganin yanda suka ruɗe da al'amari yasa Mommy dai-dai ta nutsuwarta tare da cewa.
“Kar ku damu ku cigaba da addu'a domin addu'a takobin mumunice, sannan kada ku faɗa wa kowa wannan maganar ya zama sirri atsakanin mu”.
Sai kuma ta maida kallonta kan Asma'u kana tace.
“Asma'u Allah ya miki al'barka, kin cika ƙawar kirki duk inda ake neman ƙawar arziki kin kai.
Allah Ubangiji ya Al'barkanci rayuwar ku ya kuma kare ku aduk inda kuke”.
Haɗa baki sukayi wajen faɗin.
“Ameen”.
Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe kana tace.
“Wannan magana ya zama sirri atsakanin mu, kada ku fadawa kowa daga. Ni sai ku sai kuma Ubangijin daya halluccemu shi kuma Naseer zamu ga manufarsa.
Za muga iya gudun ruwansa sannan daga yau Khausar koda ya kira ki baza ki sake zuwa inda yake ba ko dai kina son shi!?”.

Zaro ido Khausar tayi cikin sauri ta shiga yarfe hannun tare da Girgiza kai kana tace.
“Allah Mommy bana sonshi, na tsane shi bani bashi har abada, me zanyi da matsafi ni dai bana sonshi Wallahi bana sonshi”.
Kai Mommy ta gyaɗa tare da kallon su kana tace.
“Toh shikenan ki kwantar da hankalin Allah ya tsare ku ya muku zaɓi da maza na gari, wannan ma ai addu'a ce tasa asirinsa ya tonu Allah ya ƙara tsaremu baki ɗaya ku kara riƙo da addu'a in sha Allah duk sharrin mai sherri sai dai yaga gadon bayanmu”.
Atare suka amsa da.
“Ameen”.
Haka dai akayi suna aka watse kowa na al'ajabi da ta'ajjadin ɓacewar ragon suna.

Acan gidansu Moddibo kuwa M Jameel zaune tare da Innayi Moddibo kuwa na tare da Malam Arɗo bai dawo ba.
Chapter 76 · 0% Book details