Sashe 30
Sakayyah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Motar tayo kansu gadan-gadan.
Aruɗe M Jameel yace.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n!Hasbunallahu wani'imal wakin!! A'a su waye wannan suna da hankali kuwa!?”.
Cike da al'ajabi Moddibo ya zuba musu ido tare da ƙoƙarin yiwa motar key sai kuma ya gaza yin komai ya zubawa motar ido ganin gada-gadan fa ta nufi kansu haiƙan ƙadaran.
Sai da motar tazo gab dasu sai kuma ta kauce ta hau titi ta wuce.
Wani irin nannauyan ajinyan zuciya mai masifan ƙarfin M Jameel ya dire tare da meda kansa ya jingina da kujerar.
Shi kuwa Moddibo Idonu ya tsirawa motar cike da mamaki sai kuma ya motsa laɓɓansa a saman lips ɗinshi ya furta.
“Wannan wani irin tuƙi ne?.
Tuƙin ganganci ne ko kuwa dai da nufi ne?”.
Dalilin da yasa ya tsaya ma atunanin sa ko ɗaya daga cikin ‘Ya‘yan Malam Arɗo ne sai kuma yaga saɓanin haka.
Key yayiwa motar tare da kallon M Jameel dake lumshe da ido a hankali yace.
“J nayi zaton ɗaya daga cikin ‘Ya‘yan Malam Arɗo ne ya biyo mu shiyasa na tsaya, amma inaga basu bane wata ƙil ɗan koyon tuƙi ne”.
Ya ida Maganar batare daya ɗauki abin da muhimmanci ba.
Kai M Jameel ya gyaɗa da faɗin.
“Allah ya kyauta amma na tsorata da ganin yanda sukayo kanmu kamar da gayya suka yi sun tsinka min zuciya saura kaɗan fa su hau kanmu”.
Girgiza Kai Moddibo yayi kana yace.
“Da alama dai 'yan koyo ne!”.
Kai M Jameel ya gyaɗa tare da gyara zamansa, kana suka cigaba da tafiya.
Kai tsaye masallaci suka nufa kasancewar lokacin sallar Azahar yayi, bayan sunyi parking ne suka fito suka nufi cikin masallacin, aƙofar masallacin suka tsaya kusan tare sukay addu'ar shiga masallacin.
_“Auzubillahil Azim,Wabiwajhihil Kareem,Wasulɗanihil Ƙadiym,Minal Bismillahi Wassatu Wassalamu Ala Rasulullah.Allahummaftahliy Abwabal Rahmatik”_.
kana suka shiga.
Bayan sun idar sun fito daga masallacin M Jameel ya juya ya kalli Moddibo yace.
“Muje gida muci abinci”.
Da gefen ido
Moddibo ya kalleshi tare damotsa lips enshi zaiyi magana.
M Jameel yayi saurin ɓata fuska tare da cewa.
“Ba zakaje ba ko?”.
Murmushi Moddibo yayi tare da juyawa akalar motar zuwa gidansu M Jameel.
Yanzu ƙira'ar Sheykh Jabeer suke saurara har suka isa.
Bayan sunyi parking suka shiga Babban falon gida Adining suka zauna sukaci abincin shikam Moddibo kaɗan yaci ya bari.
Miƙewa sukayi suka fita Fitowarsu daga falon yayi dai-dai da ƙarasowar Hajiya Karima wajen M Jameel yace.
“Aunty Karima ina yini”.
Ba tare data amsa ba ta watsawa Moddibo kallon tsana tace.
“Maƙale anzo kenan?”.
Cikin ɗan sakin fuska yace.
“Ehh”.
Cike da mamakin halayensa da ƙarfin halinsa tace.
“To wai kai dan Allah ka rabu da bawan Allah nan da dukiyar mahaifinsa mana ko zai samu yayi abin kansa!”.
Cikin takaici M Jameel yace.
“Dan Allah Aunty ki ƙyale Moddibo da irin wa'annan kalaman mana, na sha faɗa miki shi ba irin mutunen da kike zato bane, ta ya zan fahimtar da ke?”.
Baki ta taɓe tare da juyawa tabar wajen kamar zata tashi sama.
Shi kuwa Moddibo lumshe idanunsa yayi tare da cije laɓaɓɓansa na ƙasa tare da kiran sunan Allah aransa.
Araunane M Jameel yace.
“Dan Allah Moddibo kayi haƙuri da abinda Aunty Karima keyi maka”.
Cikin kula Moddibo ya dubesa cikin yanayin nutsuwarsa da kuma ƙasaitarsa yace.
“J.kada ka damu inda sabo ai yaci ace na saba da halin Aunty abinda tun tasowar mu a haka nake da ita abinda tun bamu wuce shekaru shida-shida a duniya ba take min, har yanzu da muka bawa talatin baya, ai ya zama man shafawa kawai dai abu biyu ke sawa ban taɓa yi mata wonkin babban borgoba”.
Ya ƙare mgn tare da nufar ɗakin M Jameel.
Cikin jinjina kai M Jameel ya bi bayansa yana mai al'ajabi abinda Modiyke ɓoyewa tsawon shekaru da yake cewa dalilin dake hanasa taka mata birki, yayi ya gaya masa kuma sam yaƙi.
A ha dai suka isa, suna shiga ɗakin Moddibo ya kwanta bisa kujera tare da lumshe idanunsa alamun bacci zaiyi.
Acan gidansu Lamiɗo kuwa Mommy ce zaune yayin da Asma'u ke zaune daga ƙasa gefen ƙafafunta ta ɗago kanta tace.
Mommy asatin nan zamu koma makaranta gashi har yanzu Khausar bata dawo ba”.
“Wallahi kuwa gashi duk kwana biyun nan ba muyi waya ba, dan munfi sati da yin mgn”.
“Ayyah Allah Andi Meyesa”.
Cewar Asma'u
Kai Mommy ta jinjina tare da cewa.
“Kuma Idan ka kiransu ba zai shiga ba sai dai idan su suka kira ka”.
Gyara zama Asma'u tayi tare da cewa.
“Gaskiya Mommy Idan ta kira kice ta dawo tasan ana komawa za'a fara karatu gadan-gadan”.
Mommy tace.
“Inasha Allah zan faɗa mata”.
Daga nan sai suka ɗan ci gaba da hida, daga bisani sukayi
Sallama sannan ta tafi.
Acan Rugar Jauro Yaya kuwa yau sati da rasuwar Baffa Umaru baki ɗaya basu da cikakkiyar walwala duk da cewa sun dawo da sabgoginsu kamar da sai dai ciwon na nan aransu.
Khausar kuwa sosai tayi sanyi tun da akayi rasuwar bata cikin hayyacinta shiyasa bata samu ta kira Mommy ta ba.
Kasancewar jiya akayi adduo'ar bakwai Baffanta da yaransa duk sun koma bayan sunyi exchange na number ita dai ta Mommy ta basu. tare da yiwa Khausar al'ƙawarin kai mata ziyara wataran...
Anutse Khausar ta juya ta kalli Yaya Abba cikin sanyin murya tace.
“Ayyah yaya Abba dan Allah ka bani wayarka zan kira Mommy na”.
Kallonta Yaya Abba yayi cike da tausayi duk tayi wata iri yace.
“Toh shikenan amma ki bari sai gobe ki kirasu dan yau network bashi da kyau koda kin hau kan Bishiyar ma ba zaki ji magana ba”.
Kai ta gyaɗa masa kana tace.
“Toh Allah ya kaimu”.
“Amin”.
Ya amsa tare da miƙewa ya fita.
*GEMBILA*
Washe gari da safe tunda gari ya waye Malam Arɗo ke ta kiran wayar Moddibo awaya amma ba'a ɗagawa.
Shi kuwa Moddibo Anutse ya farka daga baccin daya koma tare da furta.
_“Alhamdulillahil Lazi ahyana bada amatana wa'ilaihil nushur”_
Wayarsa dake gefe ya janyo ganin Miss call ɗin malam Arɗo bar katai da yayi ne ya sashi ajiye wayar.
Kana ya miƙe ya shiga toilet.
Tare da addu'a a baki nai
Wanka yayi wanda ya ɗauke sa kimanin minti talatin kana ya fito yana mai faɗin.
_“Gufranaka”_
Suman kansa yake tsanewa da baby pink towel mai taushi.
Yayinda yake sanye da jibgegiyar bathrobe pink color mai masifar taushi wacce ya saƙale igiyoyinta a ƙugunsa.
A hankali ya zauna agaban dressing mirrow tare da,
Jona handdryer kana ya kunna tare da gyara zamansa da kyau bisa kujerar, dressing mirror ɗin tare da fara busar da sumar kansa mai ɗan karen sulɓi.
56 seconds yayi zuwa 1 minute yayi yana jujjuya kan handdryer ɗin tare da sa hannunsa ɗaya dake riƙe da madaidaicin Kum.
A hankali ya ajiye dryer din tare, da buɗe wani gora mai haɗe da man gashi na musamman, wanda Ummi ce ke haɗa musu, ɗan tsiyaya yayi kana ya murza tafin hannunsa tare da shafa.
Wani irin sheƙi da ƙyalli mai ɗaukan ido suman nasa ya farayi tare da fidda wani ni'imtaccen ƙamshi.
wani ƙum mai laushi wanda yafi na farin ya ɗauka tare da bin gashin nasa ya mishi tafiyar tsutsa,
Wow masha Allah, kamar saƙan taburma haka gashin ya kwanta da salo mai burgewa.
Goge tafin hannunsa yayi da towel ɗin dake bisa ƙafaɗarsa, kanaya
lakato lotion ɗin sa mai daɗin ƙamshi ya shafa jikinsa baki ɗaya.
idonsa ya lumshe tare da kauda kansa lokacin da yake shafawa cinyoyinsa mayin,
fuskarsa ya ɗan shafawa, mai ɗin tare da sa yatsarsa babba ya kwantar da gashin giransa na gefen dama, kana yasa babbar yatsar na hagu ya kwantar da na gefen hagun. sannan ya ɗan tsiyayi man kanshin ya shafawa tattausan sajensa dake kwance lip-lip ya shafa, wani irin sheƙi sajen keyi yana fitar da sanyayyan ƙamshi.
Anutse ya Miƙe ya buɗe durowarsa ya ɗauki jallabiyarsa mai masifar tsada da taushi Kalar Army green, kana ya zaro tattausan boxer and singlet farare ƙal-ƙal,
ɗan sunkuyawa yayi ya sanya boxer ɗin ba tare da kalli surarsa ba.
Kana ya miƙa tare da dai-dai ta zaman robor a gugunsa,
Bathrobe din ya kwance, kana ya saƙalashi bisa wata yar Kekkyawar masaƙali dake gefen drowersa, singlet ɗin ya saka, kana ya zira tattausar jallabiyar dake zuba sheƙi da ƙyalli wacce kai da ka gani kasan taja kuɗi.
baƙin hirami ya jawo, sanya kana ya naɗe kansa da hirami tare da sako jelar ɗaurin ta gefensa na hagu tsayawa yayi agaban Dressing mirrow tare da ɗaukar kwalbar turaren mai masifar ƙamshi ya feshe ilahirin jikinsa dashi wayarsa ya ɗauka tare da sanya wa a aljihun gaban rigarsa kana ya fice.
A motarsa ya shiga bayan ya buɗe gate sannan ya fice kana ya sake fitowa ya rufe gate ɗin.
Aƙofar gate ɗin gidan Malam Arɗo yayi Hong mai gadi ya buɗe masa yashiga Babban gida ne sosai sai dai kallo ɗaya zaka yiwa gidan kasan mamallakin gidan mutum nai mugun maƙo da kirta babu wani fentin arziƙi ajikin ginin gidan haka zalika ginin ɗakunan single rooms ne cikin haraban gidan kuwa koda flow babu daga can kusan ƙaramin ƙofar da zai sadaka da cikin gidan rijiya ce babba anyi masa murfin ƙarfe fitowa Malam Arɗo yayi yana murmushi.
Ɗan guntun Murmushin gefen baki Moddibo ya mayar masa tare da cewa.
“Ina kwana Malam ɗazu ka kira ina bacci”.
Ya ida maganar yana shiga ɗakin ɗaya daga cikin matan Malam Arɗo mai suna Hajiya Zainabu domin Malam Arɗo ya ɗauki Moddibo tamkar jika.
Wara ido Moddibo yayi yana kallon Hajiya Zainabu yace.
“Hajiya ina kujerun ɗakin?
Indai ba kujera Ni gaskiya bazan zauna ba”.
Sai kuma ya juya tare da kallon Malam Arɗo yace.
“Malam dan Allah asamu kujeru saboda idan sukayi baƙi su samu inda zasu zauna”.
Hararansa Malam Arɗo yayi tare da cewa.
“Ba kai bane kake lissafin duk abinda zai cin yemin aljihu kasan yanda gyaran makarantar nan ya cinye min kuɗi kuwa?.
Yanzu ma abu biyune yasa na kira ka na farko motata ta ɓaci zaka kaini Rugar Jauro yaya sannan kuma muyi magana akan ƙara kudin school fees ɗin yara dan gaskiya saina fanshe kuɗin dana kashe a school fees ɗin forko Aradun Allah.
Aruɗe M Jameel yace.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n!Hasbunallahu wani'imal wakin!! A'a su waye wannan suna da hankali kuwa!?”.
Cike da al'ajabi Moddibo ya zuba musu ido tare da ƙoƙarin yiwa motar key sai kuma ya gaza yin komai ya zubawa motar ido ganin gada-gadan fa ta nufi kansu haiƙan ƙadaran.
Sai da motar tazo gab dasu sai kuma ta kauce ta hau titi ta wuce.
Wani irin nannauyan ajinyan zuciya mai masifan ƙarfin M Jameel ya dire tare da meda kansa ya jingina da kujerar.
Shi kuwa Moddibo Idonu ya tsirawa motar cike da mamaki sai kuma ya motsa laɓɓansa a saman lips ɗinshi ya furta.
“Wannan wani irin tuƙi ne?.
Tuƙin ganganci ne ko kuwa dai da nufi ne?”.
Dalilin da yasa ya tsaya ma atunanin sa ko ɗaya daga cikin ‘Ya‘yan Malam Arɗo ne sai kuma yaga saɓanin haka.
Key yayiwa motar tare da kallon M Jameel dake lumshe da ido a hankali yace.
“J nayi zaton ɗaya daga cikin ‘Ya‘yan Malam Arɗo ne ya biyo mu shiyasa na tsaya, amma inaga basu bane wata ƙil ɗan koyon tuƙi ne”.
Ya ida Maganar batare daya ɗauki abin da muhimmanci ba.
Kai M Jameel ya gyaɗa da faɗin.
“Allah ya kyauta amma na tsorata da ganin yanda sukayo kanmu kamar da gayya suka yi sun tsinka min zuciya saura kaɗan fa su hau kanmu”.
Girgiza Kai Moddibo yayi kana yace.
“Da alama dai 'yan koyo ne!”.
Kai M Jameel ya gyaɗa tare da gyara zamansa, kana suka cigaba da tafiya.
Kai tsaye masallaci suka nufa kasancewar lokacin sallar Azahar yayi, bayan sunyi parking ne suka fito suka nufi cikin masallacin, aƙofar masallacin suka tsaya kusan tare sukay addu'ar shiga masallacin.
_“Auzubillahil Azim,Wabiwajhihil Kareem,Wasulɗanihil Ƙadiym,Minal Bismillahi Wassatu Wassalamu Ala Rasulullah.Allahummaftahliy Abwabal Rahmatik”_.
kana suka shiga.
Bayan sun idar sun fito daga masallacin M Jameel ya juya ya kalli Moddibo yace.
“Muje gida muci abinci”.
Da gefen ido
Moddibo ya kalleshi tare damotsa lips enshi zaiyi magana.
M Jameel yayi saurin ɓata fuska tare da cewa.
“Ba zakaje ba ko?”.
Murmushi Moddibo yayi tare da juyawa akalar motar zuwa gidansu M Jameel.
Yanzu ƙira'ar Sheykh Jabeer suke saurara har suka isa.
Bayan sunyi parking suka shiga Babban falon gida Adining suka zauna sukaci abincin shikam Moddibo kaɗan yaci ya bari.
Miƙewa sukayi suka fita Fitowarsu daga falon yayi dai-dai da ƙarasowar Hajiya Karima wajen M Jameel yace.
“Aunty Karima ina yini”.
Ba tare data amsa ba ta watsawa Moddibo kallon tsana tace.
“Maƙale anzo kenan?”.
Cikin ɗan sakin fuska yace.
“Ehh”.
Cike da mamakin halayensa da ƙarfin halinsa tace.
“To wai kai dan Allah ka rabu da bawan Allah nan da dukiyar mahaifinsa mana ko zai samu yayi abin kansa!”.
Cikin takaici M Jameel yace.
“Dan Allah Aunty ki ƙyale Moddibo da irin wa'annan kalaman mana, na sha faɗa miki shi ba irin mutunen da kike zato bane, ta ya zan fahimtar da ke?”.
Baki ta taɓe tare da juyawa tabar wajen kamar zata tashi sama.
Shi kuwa Moddibo lumshe idanunsa yayi tare da cije laɓaɓɓansa na ƙasa tare da kiran sunan Allah aransa.
Araunane M Jameel yace.
“Dan Allah Moddibo kayi haƙuri da abinda Aunty Karima keyi maka”.
Cikin kula Moddibo ya dubesa cikin yanayin nutsuwarsa da kuma ƙasaitarsa yace.
“J.kada ka damu inda sabo ai yaci ace na saba da halin Aunty abinda tun tasowar mu a haka nake da ita abinda tun bamu wuce shekaru shida-shida a duniya ba take min, har yanzu da muka bawa talatin baya, ai ya zama man shafawa kawai dai abu biyu ke sawa ban taɓa yi mata wonkin babban borgoba”.
Ya ƙare mgn tare da nufar ɗakin M Jameel.
Cikin jinjina kai M Jameel ya bi bayansa yana mai al'ajabi abinda Modiyke ɓoyewa tsawon shekaru da yake cewa dalilin dake hanasa taka mata birki, yayi ya gaya masa kuma sam yaƙi.
A ha dai suka isa, suna shiga ɗakin Moddibo ya kwanta bisa kujera tare da lumshe idanunsa alamun bacci zaiyi.
Acan gidansu Lamiɗo kuwa Mommy ce zaune yayin da Asma'u ke zaune daga ƙasa gefen ƙafafunta ta ɗago kanta tace.
Mommy asatin nan zamu koma makaranta gashi har yanzu Khausar bata dawo ba”.
“Wallahi kuwa gashi duk kwana biyun nan ba muyi waya ba, dan munfi sati da yin mgn”.
“Ayyah Allah Andi Meyesa”.
Cewar Asma'u
Kai Mommy ta jinjina tare da cewa.
“Kuma Idan ka kiransu ba zai shiga ba sai dai idan su suka kira ka”.
Gyara zama Asma'u tayi tare da cewa.
“Gaskiya Mommy Idan ta kira kice ta dawo tasan ana komawa za'a fara karatu gadan-gadan”.
Mommy tace.
“Inasha Allah zan faɗa mata”.
Daga nan sai suka ɗan ci gaba da hida, daga bisani sukayi
Sallama sannan ta tafi.
Acan Rugar Jauro Yaya kuwa yau sati da rasuwar Baffa Umaru baki ɗaya basu da cikakkiyar walwala duk da cewa sun dawo da sabgoginsu kamar da sai dai ciwon na nan aransu.
Khausar kuwa sosai tayi sanyi tun da akayi rasuwar bata cikin hayyacinta shiyasa bata samu ta kira Mommy ta ba.
Kasancewar jiya akayi adduo'ar bakwai Baffanta da yaransa duk sun koma bayan sunyi exchange na number ita dai ta Mommy ta basu. tare da yiwa Khausar al'ƙawarin kai mata ziyara wataran...
Anutse Khausar ta juya ta kalli Yaya Abba cikin sanyin murya tace.
“Ayyah yaya Abba dan Allah ka bani wayarka zan kira Mommy na”.
Kallonta Yaya Abba yayi cike da tausayi duk tayi wata iri yace.
“Toh shikenan amma ki bari sai gobe ki kirasu dan yau network bashi da kyau koda kin hau kan Bishiyar ma ba zaki ji magana ba”.
Kai ta gyaɗa masa kana tace.
“Toh Allah ya kaimu”.
“Amin”.
Ya amsa tare da miƙewa ya fita.
*GEMBILA*
Washe gari da safe tunda gari ya waye Malam Arɗo ke ta kiran wayar Moddibo awaya amma ba'a ɗagawa.
Shi kuwa Moddibo Anutse ya farka daga baccin daya koma tare da furta.
_“Alhamdulillahil Lazi ahyana bada amatana wa'ilaihil nushur”_
Wayarsa dake gefe ya janyo ganin Miss call ɗin malam Arɗo bar katai da yayi ne ya sashi ajiye wayar.
Kana ya miƙe ya shiga toilet.
Tare da addu'a a baki nai
Wanka yayi wanda ya ɗauke sa kimanin minti talatin kana ya fito yana mai faɗin.
_“Gufranaka”_
Suman kansa yake tsanewa da baby pink towel mai taushi.
Yayinda yake sanye da jibgegiyar bathrobe pink color mai masifar taushi wacce ya saƙale igiyoyinta a ƙugunsa.
A hankali ya zauna agaban dressing mirrow tare da,
Jona handdryer kana ya kunna tare da gyara zamansa da kyau bisa kujerar, dressing mirror ɗin tare da fara busar da sumar kansa mai ɗan karen sulɓi.
56 seconds yayi zuwa 1 minute yayi yana jujjuya kan handdryer ɗin tare da sa hannunsa ɗaya dake riƙe da madaidaicin Kum.
A hankali ya ajiye dryer din tare, da buɗe wani gora mai haɗe da man gashi na musamman, wanda Ummi ce ke haɗa musu, ɗan tsiyaya yayi kana ya murza tafin hannunsa tare da shafa.
Wani irin sheƙi da ƙyalli mai ɗaukan ido suman nasa ya farayi tare da fidda wani ni'imtaccen ƙamshi.
wani ƙum mai laushi wanda yafi na farin ya ɗauka tare da bin gashin nasa ya mishi tafiyar tsutsa,
Wow masha Allah, kamar saƙan taburma haka gashin ya kwanta da salo mai burgewa.
Goge tafin hannunsa yayi da towel ɗin dake bisa ƙafaɗarsa, kanaya
lakato lotion ɗin sa mai daɗin ƙamshi ya shafa jikinsa baki ɗaya.
idonsa ya lumshe tare da kauda kansa lokacin da yake shafawa cinyoyinsa mayin,
fuskarsa ya ɗan shafawa, mai ɗin tare da sa yatsarsa babba ya kwantar da gashin giransa na gefen dama, kana yasa babbar yatsar na hagu ya kwantar da na gefen hagun. sannan ya ɗan tsiyayi man kanshin ya shafawa tattausan sajensa dake kwance lip-lip ya shafa, wani irin sheƙi sajen keyi yana fitar da sanyayyan ƙamshi.
Anutse ya Miƙe ya buɗe durowarsa ya ɗauki jallabiyarsa mai masifar tsada da taushi Kalar Army green, kana ya zaro tattausan boxer and singlet farare ƙal-ƙal,
ɗan sunkuyawa yayi ya sanya boxer ɗin ba tare da kalli surarsa ba.
Kana ya miƙa tare da dai-dai ta zaman robor a gugunsa,
Bathrobe din ya kwance, kana ya saƙalashi bisa wata yar Kekkyawar masaƙali dake gefen drowersa, singlet ɗin ya saka, kana ya zira tattausar jallabiyar dake zuba sheƙi da ƙyalli wacce kai da ka gani kasan taja kuɗi.
baƙin hirami ya jawo, sanya kana ya naɗe kansa da hirami tare da sako jelar ɗaurin ta gefensa na hagu tsayawa yayi agaban Dressing mirrow tare da ɗaukar kwalbar turaren mai masifar ƙamshi ya feshe ilahirin jikinsa dashi wayarsa ya ɗauka tare da sanya wa a aljihun gaban rigarsa kana ya fice.
A motarsa ya shiga bayan ya buɗe gate sannan ya fice kana ya sake fitowa ya rufe gate ɗin.
Aƙofar gate ɗin gidan Malam Arɗo yayi Hong mai gadi ya buɗe masa yashiga Babban gida ne sosai sai dai kallo ɗaya zaka yiwa gidan kasan mamallakin gidan mutum nai mugun maƙo da kirta babu wani fentin arziƙi ajikin ginin gidan haka zalika ginin ɗakunan single rooms ne cikin haraban gidan kuwa koda flow babu daga can kusan ƙaramin ƙofar da zai sadaka da cikin gidan rijiya ce babba anyi masa murfin ƙarfe fitowa Malam Arɗo yayi yana murmushi.
Ɗan guntun Murmushin gefen baki Moddibo ya mayar masa tare da cewa.
“Ina kwana Malam ɗazu ka kira ina bacci”.
Ya ida maganar yana shiga ɗakin ɗaya daga cikin matan Malam Arɗo mai suna Hajiya Zainabu domin Malam Arɗo ya ɗauki Moddibo tamkar jika.
Wara ido Moddibo yayi yana kallon Hajiya Zainabu yace.
“Hajiya ina kujerun ɗakin?
Indai ba kujera Ni gaskiya bazan zauna ba”.
Sai kuma ya juya tare da kallon Malam Arɗo yace.
“Malam dan Allah asamu kujeru saboda idan sukayi baƙi su samu inda zasu zauna”.
Hararansa Malam Arɗo yayi tare da cewa.
“Ba kai bane kake lissafin duk abinda zai cin yemin aljihu kasan yanda gyaran makarantar nan ya cinye min kuɗi kuwa?.
Yanzu ma abu biyune yasa na kira ka na farko motata ta ɓaci zaka kaini Rugar Jauro yaya sannan kuma muyi magana akan ƙara kudin school fees ɗin yara dan gaskiya saina fanshe kuɗin dana kashe a school fees ɗin forko Aradun Allah.