Sashe 3
Sakayyah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ganin Innayi na kwance bisa sallaya babu ko pillown ga kuma karkarwa da jikinta keyi.
A hankali ya rusuna tare da takwara ƙafarsa ta dama ya zauna kanta ta hagu kuma ya tsaidata, cikin kulawa da tarin so tausayi, ya motsa lips ɗinshi a hankali yace.
“Yah Salam.
Innayi! Innayi!! Innayi!!!”. Ya kirata sau uku, ganin bata amsa bane, yasashi manna tafin hannunsa kan goshinta, wanda hakan ne yasata buɗe kwayar idanunta da sukayi ja.
Sai kuma ta medasu ta rufesu, sai ga wasu hawayen masu zafi sun kwaranyo mata.
Jiki na rawa tasa hannunta, ta kamo hannunsa, murya a raunace tace.
“Aliyu”. Da sauri ya zuba mata idanun tare da tsareta dasu, domin zai iya cewa, wannan shine karo na biyu a rayuwarsa da yaji ta kirasa da asalin sunansa na yanka.
A hankali yace.
“Na'am Innayi meke damunki? Meyasa baki kirani kin gaya min baki da lfy ba? Tashi mu tafi asibiti”.
Ya ƙare mgnar yana mai tallabota ya zaunar da ita.
Wani dogon numfashi Innayin taja cikin rawan murya tace.
“Aliyu ka zauna, kaji abinda zan gaya maka”.
cikin yanayin kulawa a sanyaye yace.
“A'a muje asibiti tukuna, sai mun dawo”.
Cikin ɗan ɗaga murya tace.
“Aliyu ka bari kaji abinda baka saniba.
Bana son in mutu in barka a nahiyar maraici, bana son in mutu da abinda ni kaɗaice na sani kuma nakeda dama da ikon sanar da kai, idan na mutu a haka ban sanar da kai abinda ke bibiye da muba, nayi maka cuta mafi muni a rayuwarka.
Aliyu ka bari in sanar da kai abinda Allah ya nuna min a daren jiya”.
A hankali ya fesar da nannauyan numfashi, sai kuma ya juyo ya kalli ƙofar ɗakin, jiyo Muryar Amininsa mafi ɗan uwa, wato M Jamil yanayin sallama, a hankali yace.
“Wa alaikassalam J”.
Ya ƙira Aminin nasa da sunan da duk duniya shi kadai ke kiransa da hakan,
Ido ya zubawa M Jamil ɗin a hankali tare dayi masa alamun ya shigo da kwayar idanunsa,
Cikin yanayin sauƙin kai sakin fuska faram-faram Jamil ya sako kansa cikin ɗakin yana mai cewa.
“Iya innare yau me kika dafa mana ne, dan tun jiya da na dawo ƙasar nan banci komai ba, nace sai abincinki zanci ko na Ummina”.
Sai kuma yayi shiru tare da matsowa kusa da ita...
Cikin Masarautar Gembilan kuwa.
Wata Kekkyawar matace yar duma-duma mai kyan shiga da haiba, ke zaune bisa kujera, yayinda System ke gabanta bisa ɗan madaidaicin stool yayinda fuskarta ke manne da wani ɗan farin glass siriri.
Da alamu typing takeyi.
Kai ta ɗan jinjina tare da juyowa ta kalli dinning area inda hayaniyar yaranta ke tashi.
Kai ta ɗan jinjina tare da kallon wata yar narkekkiyar matashiya da bazata wuce 14 year's ba.
Ido ta zuba mata ganin ta nufota da sauri.
Hannunta ɗaya.
Riƙe da school bag da takalmin sinika da kuma ɗan madaidacin hijabin Uniform ɗin ta.
Da sauri ta rusuna gaban Matar tare da juya mata baya tana cewa.
“Ayya Momy tubke min kaina, nayi-nayi yaƙi sai na ƙulleshi sai ya sule”.
Kwaffa tayi tare da cewa.
“To wai ke kam Khausar yaushe ne zaki iya, tubke gashin kanki”.
Ta ƙare mgnar tana tattaro suman Khausar din yana mai zamewa,
Sai kuma ta ɗago kanta ta kalli Ɗan matashin yaron da yanzu ya fito cikin Uniform ɗinsa. Wanda yake iri ɗaya dana jikin wacce aka kira da Khausar.
Da alamun ya gama shirinsa tsab.
Cikin tsuke fuska ya watsawa Khausar din harara tare da cewa.
“Gsky ni zan tafi Ramadan Raudat zomu tafi, kullum ita ke jaza mana yin letting muje aita zanemu kamar bayi.
Ni wlh da zan samu a rabamun hanya da ita inaso, muna shiga school kamar wasu shaidanu zakaji an fara cewa.
FATTANAH kuka biyewa ko, duk sai an gama shiga aji kafin ku iso.”
Cikin yanayin tsiwa da son girma ta miƙe tsaye tana ɗaure ɗan kwalinta harara ta watsa mishi tare da cewa.
“Wallahi ka shiga hankalinka dani Haydar in baka dena cemin FATTANAH ba zan fasa maka baki”.
Dogon tsaki yaja tare da juyawa ya nufi ƙofar falon, yana gyara zaman net ɗin sa. Tare da cewa.
“Sai ki gayawa wanda yasa miki sunan, ko kuma ki nitsu ki dena rashin kunya da rawan kai”.
Cikin ɗan ɗaga murya Momyn nasu tace.
“Gsky Babana bana son wannan sunan da aka liƙawa Mamana sam bafana son sunan”.
Da sauri yace.
“Toh Momy ai ita ta jawa kanta fitinenneyar ce ta gasken gaske, in dai kinji faɗa to da ita a ciki, in kuma babu ita to zakiji ance ai gulma akayi ta maidawa maishi, wai ita ba'a gulma da ita, itafa tana iya zuwa zuwa ta samu ana faɗa ta shiga tayi kane-kane sai an gama tace wai me dalilin faɗan”.
Ya ƙare mgnar yana fita.
Ita kuwa Khausar zama tayi gefen Momynsu tana sa takalmanta da ɗan sassarfa domin yau din ranace ta musamman a wurinta tana cike da ɗokin zuwa makaranta kasancewar yau suka dawo hutu, kuma hutune na canjaza aji da JSS zata tafi SS 1 wanda takega matakin samun encinta ne kenan zata taka, tunda yanzu zata koma aji da matan aure, a islamiyar safe, sai kuma na bokone tacan anan ne babu enci sai randa ta gama sa takalmin ta saka, tana sakin yelwataccen murmushi.
Yayinda Ramadan da Raudat suke tsaye gefenta.
Hannu tasa ta kama hannun Raudat tare da cewa.
“Mu tafi”.
Da sauri ta juyo ta kalli Momyn nasu tare da kwaɓe fuska jin tana cewa.
“Ku biya sashin Gimbiya Dadu ku gaidata, bata da lfy”.
Cikin kwaɓe fuska tace.
“Momy zamuyi letti muje wannan mai sunan baban naki ya samu damar sawa a azabtar dani”.
Ta ƙare mgnar cikin son zillewa zuwa sashin Gimbiya Duda, ita kuwa Momy tsuke fuska tayi tare da cewa.
“Ku biya ku gaisheta da jiki nace ko”.
Cikin bin umarnin mahaifiyar tata badon tasowa tace.
“Toh Momy”.
Daga nan ta kada kan ƙannen nata Duk suka fito.
Sai kuma tayi sauri ta juyo tare da cewa.
“Momy mun tafi”.
Murmushi tayi sanin manufar ta yasa cikin lumshe idanu tace.
“Allah ya kaiku lfy ya baku Sa'a Allah yasa ki shiga SS 1 da ƙafar dama, Allah ya shirya min ku”.
Cike da jin daɗi tace.
“Amin Ya Allah”.
Kana suka fita.
Suna fitowa suka samu duk sauran yaran gidanma sun fito.
Kamar haɗin baki kab ɗin su sashin Gimbiya Dadu suka nufa.
Kai tsaye suka wuce har bedroom ɗin ta domin bata falon.
Su Asiya ce, a gaba ita da sauran ƙannenta, sai kuma su Khausar din.
Zaune suka sameta bisa tsakiyar gadon mulkinta, mai martaba Lamido Gembilan yana zaune ƙasa bisa carpet, yana haɗa mata tea,
Cikin tarin biyayya, da sauri suka rusuna baki ɗayansu, kusa haɗa baki sukayi wurin cewa.
(“Allah saine Abba, noi nɓanɗu Dadu?) Allah ya faranta maka Abba ya jikin Dadu?”.
Cikin son ahlin nasa ya jinjina masu kai tare da cewa.
(“Yettore Allah nwodi dama) an godewa Allah da sauƙi”.
“Allah ntokkin dama”.
Suka faɗa a tare, cikin tankwashe sawunsa yace.
“Allah jabu”.
Amin suka faɗi baki ɗayansu,
Yayinda Khausar kuma taketa jan hijabinta, tana mai sunkuyar da kanta ƙasa,
Allah ya sani bata ƙaunar abinda zai kawo ta gaban Gimbiya Dadu,
Domin jikinta da nitsuwarta duk rasasu takeyi, sabida wani irin mayataccen kallo mai bada tsoro da tsohuwar ke Binta dashi.
Kamar koda yaushe kuma hakane, duk da bata da lafiya, amman wani irin masifeffen kallo ta tsare Khausar ɗin dashi har bata jin gaisuwar da jikokin nata keyi mata,
Cikin taɓe baki Asiya tace.
“Dadu wannan wanne irin kallo ne? muna gaidaki kinyi shiru?”.
Jin hakanne yasa Khausar ɗan ɗago kanta,
Ai kuwa ido cikin ido sukayi da Dadu.
Da sauri ta motsa lips ɗin ta a hankali tare da cewa.
“Innalillahi wa innailaihi raji'un”.
Sabida wani irin tashi da tsikar jikinta ya farayi, yam-yam.
Ita kuwa Dadu har lau bata cire idanunta a kantaba,
Haydar ne ya ɗan miƙa tsaye tare da kamo hannun Ramadan da Raudat yace.
“Dadu Allah ya sauwaƙa, zamu tafi school kada muyi letti Raudat muje”.
Abin mamaki har lau Dadu batama san anayi mata mgna ba, bare ta amsa musu, gaba ɗaya nitsuwarta da kallonta yana kan Khausar....!
Lamido kuwa ido ya zubawa maifiyar tasa, cike da mamakin lamarinta, ya zama ana kallon kalo, ita tana kallon Khausar data kasa koda ƙwaƙƙwaran motsi shi kuwa yana kallonta.
Asiya kuwa itama miƙeqa tayi tare da kaɗa kan ƙannenta tayi gaba Amina ce ƙanwar Asiya mai binta ta ɗan miƙa tare da cewa,
“Uhum”. ta fice
Ya zama daga Dadu sai Lamido sai Khausar.
Cikin wani irin yanayi da Khausar din keji ta kuma kallon Dadu, wacce zuwa yanzu ta saki laɓen bakinta na ƙasa, wani irin yawu mai cike da mayataccen kwaɗayi ne ya tsinko mata, har yana ɗan sauƙowa kan lips ɗin ta.
Cikin sauri Khausar ta miƙe jin Lamido yana cewa.
“Mamana tashi ku tafi”.
Ai kafin ma ya rufe bakinsa, tuni ta fita tana mai cewa.
“Toh Abba”.
Ita kuwa Dadu wani nannauyan numfashin ta sauƙe tare da juyowa takalli ɗan nata, dake miƙa mata cup ɗin tea.
Cikin diriricewa tace.
“A'a bana buƙatar abin zaƙi, a kawo min abu mai yaji-yaji”.
Cike da biyayya yace.
“Toh”.
Kana ya miƙe ya fita.
A hankali ya rusuna tare da takwara ƙafarsa ta dama ya zauna kanta ta hagu kuma ya tsaidata, cikin kulawa da tarin so tausayi, ya motsa lips ɗinshi a hankali yace.
“Yah Salam.
Innayi! Innayi!! Innayi!!!”. Ya kirata sau uku, ganin bata amsa bane, yasashi manna tafin hannunsa kan goshinta, wanda hakan ne yasata buɗe kwayar idanunta da sukayi ja.
Sai kuma ta medasu ta rufesu, sai ga wasu hawayen masu zafi sun kwaranyo mata.
Jiki na rawa tasa hannunta, ta kamo hannunsa, murya a raunace tace.
“Aliyu”. Da sauri ya zuba mata idanun tare da tsareta dasu, domin zai iya cewa, wannan shine karo na biyu a rayuwarsa da yaji ta kirasa da asalin sunansa na yanka.
A hankali yace.
“Na'am Innayi meke damunki? Meyasa baki kirani kin gaya min baki da lfy ba? Tashi mu tafi asibiti”.
Ya ƙare mgnar yana mai tallabota ya zaunar da ita.
Wani dogon numfashi Innayin taja cikin rawan murya tace.
“Aliyu ka zauna, kaji abinda zan gaya maka”.
cikin yanayin kulawa a sanyaye yace.
“A'a muje asibiti tukuna, sai mun dawo”.
Cikin ɗan ɗaga murya tace.
“Aliyu ka bari kaji abinda baka saniba.
Bana son in mutu in barka a nahiyar maraici, bana son in mutu da abinda ni kaɗaice na sani kuma nakeda dama da ikon sanar da kai, idan na mutu a haka ban sanar da kai abinda ke bibiye da muba, nayi maka cuta mafi muni a rayuwarka.
Aliyu ka bari in sanar da kai abinda Allah ya nuna min a daren jiya”.
A hankali ya fesar da nannauyan numfashi, sai kuma ya juyo ya kalli ƙofar ɗakin, jiyo Muryar Amininsa mafi ɗan uwa, wato M Jamil yanayin sallama, a hankali yace.
“Wa alaikassalam J”.
Ya ƙira Aminin nasa da sunan da duk duniya shi kadai ke kiransa da hakan,
Ido ya zubawa M Jamil ɗin a hankali tare dayi masa alamun ya shigo da kwayar idanunsa,
Cikin yanayin sauƙin kai sakin fuska faram-faram Jamil ya sako kansa cikin ɗakin yana mai cewa.
“Iya innare yau me kika dafa mana ne, dan tun jiya da na dawo ƙasar nan banci komai ba, nace sai abincinki zanci ko na Ummina”.
Sai kuma yayi shiru tare da matsowa kusa da ita...
Cikin Masarautar Gembilan kuwa.
Wata Kekkyawar matace yar duma-duma mai kyan shiga da haiba, ke zaune bisa kujera, yayinda System ke gabanta bisa ɗan madaidaicin stool yayinda fuskarta ke manne da wani ɗan farin glass siriri.
Da alamu typing takeyi.
Kai ta ɗan jinjina tare da juyowa ta kalli dinning area inda hayaniyar yaranta ke tashi.
Kai ta ɗan jinjina tare da kallon wata yar narkekkiyar matashiya da bazata wuce 14 year's ba.
Ido ta zuba mata ganin ta nufota da sauri.
Hannunta ɗaya.
Riƙe da school bag da takalmin sinika da kuma ɗan madaidacin hijabin Uniform ɗin ta.
Da sauri ta rusuna gaban Matar tare da juya mata baya tana cewa.
“Ayya Momy tubke min kaina, nayi-nayi yaƙi sai na ƙulleshi sai ya sule”.
Kwaffa tayi tare da cewa.
“To wai ke kam Khausar yaushe ne zaki iya, tubke gashin kanki”.
Ta ƙare mgnar tana tattaro suman Khausar din yana mai zamewa,
Sai kuma ta ɗago kanta ta kalli Ɗan matashin yaron da yanzu ya fito cikin Uniform ɗinsa. Wanda yake iri ɗaya dana jikin wacce aka kira da Khausar.
Da alamun ya gama shirinsa tsab.
Cikin tsuke fuska ya watsawa Khausar din harara tare da cewa.
“Gsky ni zan tafi Ramadan Raudat zomu tafi, kullum ita ke jaza mana yin letting muje aita zanemu kamar bayi.
Ni wlh da zan samu a rabamun hanya da ita inaso, muna shiga school kamar wasu shaidanu zakaji an fara cewa.
FATTANAH kuka biyewa ko, duk sai an gama shiga aji kafin ku iso.”
Cikin yanayin tsiwa da son girma ta miƙe tsaye tana ɗaure ɗan kwalinta harara ta watsa mishi tare da cewa.
“Wallahi ka shiga hankalinka dani Haydar in baka dena cemin FATTANAH ba zan fasa maka baki”.
Dogon tsaki yaja tare da juyawa ya nufi ƙofar falon, yana gyara zaman net ɗin sa. Tare da cewa.
“Sai ki gayawa wanda yasa miki sunan, ko kuma ki nitsu ki dena rashin kunya da rawan kai”.
Cikin ɗan ɗaga murya Momyn nasu tace.
“Gsky Babana bana son wannan sunan da aka liƙawa Mamana sam bafana son sunan”.
Da sauri yace.
“Toh Momy ai ita ta jawa kanta fitinenneyar ce ta gasken gaske, in dai kinji faɗa to da ita a ciki, in kuma babu ita to zakiji ance ai gulma akayi ta maidawa maishi, wai ita ba'a gulma da ita, itafa tana iya zuwa zuwa ta samu ana faɗa ta shiga tayi kane-kane sai an gama tace wai me dalilin faɗan”.
Ya ƙare mgnar yana fita.
Ita kuwa Khausar zama tayi gefen Momynsu tana sa takalmanta da ɗan sassarfa domin yau din ranace ta musamman a wurinta tana cike da ɗokin zuwa makaranta kasancewar yau suka dawo hutu, kuma hutune na canjaza aji da JSS zata tafi SS 1 wanda takega matakin samun encinta ne kenan zata taka, tunda yanzu zata koma aji da matan aure, a islamiyar safe, sai kuma na bokone tacan anan ne babu enci sai randa ta gama sa takalmin ta saka, tana sakin yelwataccen murmushi.
Yayinda Ramadan da Raudat suke tsaye gefenta.
Hannu tasa ta kama hannun Raudat tare da cewa.
“Mu tafi”.
Da sauri ta juyo ta kalli Momyn nasu tare da kwaɓe fuska jin tana cewa.
“Ku biya sashin Gimbiya Dadu ku gaidata, bata da lfy”.
Cikin kwaɓe fuska tace.
“Momy zamuyi letti muje wannan mai sunan baban naki ya samu damar sawa a azabtar dani”.
Ta ƙare mgnar cikin son zillewa zuwa sashin Gimbiya Duda, ita kuwa Momy tsuke fuska tayi tare da cewa.
“Ku biya ku gaisheta da jiki nace ko”.
Cikin bin umarnin mahaifiyar tata badon tasowa tace.
“Toh Momy”.
Daga nan ta kada kan ƙannen nata Duk suka fito.
Sai kuma tayi sauri ta juyo tare da cewa.
“Momy mun tafi”.
Murmushi tayi sanin manufar ta yasa cikin lumshe idanu tace.
“Allah ya kaiku lfy ya baku Sa'a Allah yasa ki shiga SS 1 da ƙafar dama, Allah ya shirya min ku”.
Cike da jin daɗi tace.
“Amin Ya Allah”.
Kana suka fita.
Suna fitowa suka samu duk sauran yaran gidanma sun fito.
Kamar haɗin baki kab ɗin su sashin Gimbiya Dadu suka nufa.
Kai tsaye suka wuce har bedroom ɗin ta domin bata falon.
Su Asiya ce, a gaba ita da sauran ƙannenta, sai kuma su Khausar din.
Zaune suka sameta bisa tsakiyar gadon mulkinta, mai martaba Lamido Gembilan yana zaune ƙasa bisa carpet, yana haɗa mata tea,
Cikin tarin biyayya, da sauri suka rusuna baki ɗayansu, kusa haɗa baki sukayi wurin cewa.
(“Allah saine Abba, noi nɓanɗu Dadu?) Allah ya faranta maka Abba ya jikin Dadu?”.
Cikin son ahlin nasa ya jinjina masu kai tare da cewa.
(“Yettore Allah nwodi dama) an godewa Allah da sauƙi”.
“Allah ntokkin dama”.
Suka faɗa a tare, cikin tankwashe sawunsa yace.
“Allah jabu”.
Amin suka faɗi baki ɗayansu,
Yayinda Khausar kuma taketa jan hijabinta, tana mai sunkuyar da kanta ƙasa,
Allah ya sani bata ƙaunar abinda zai kawo ta gaban Gimbiya Dadu,
Domin jikinta da nitsuwarta duk rasasu takeyi, sabida wani irin mayataccen kallo mai bada tsoro da tsohuwar ke Binta dashi.
Kamar koda yaushe kuma hakane, duk da bata da lafiya, amman wani irin masifeffen kallo ta tsare Khausar ɗin dashi har bata jin gaisuwar da jikokin nata keyi mata,
Cikin taɓe baki Asiya tace.
“Dadu wannan wanne irin kallo ne? muna gaidaki kinyi shiru?”.
Jin hakanne yasa Khausar ɗan ɗago kanta,
Ai kuwa ido cikin ido sukayi da Dadu.
Da sauri ta motsa lips ɗin ta a hankali tare da cewa.
“Innalillahi wa innailaihi raji'un”.
Sabida wani irin tashi da tsikar jikinta ya farayi, yam-yam.
Ita kuwa Dadu har lau bata cire idanunta a kantaba,
Haydar ne ya ɗan miƙa tsaye tare da kamo hannun Ramadan da Raudat yace.
“Dadu Allah ya sauwaƙa, zamu tafi school kada muyi letti Raudat muje”.
Abin mamaki har lau Dadu batama san anayi mata mgna ba, bare ta amsa musu, gaba ɗaya nitsuwarta da kallonta yana kan Khausar....!
Lamido kuwa ido ya zubawa maifiyar tasa, cike da mamakin lamarinta, ya zama ana kallon kalo, ita tana kallon Khausar data kasa koda ƙwaƙƙwaran motsi shi kuwa yana kallonta.
Asiya kuwa itama miƙeqa tayi tare da kaɗa kan ƙannenta tayi gaba Amina ce ƙanwar Asiya mai binta ta ɗan miƙa tare da cewa,
“Uhum”. ta fice
Ya zama daga Dadu sai Lamido sai Khausar.
Cikin wani irin yanayi da Khausar din keji ta kuma kallon Dadu, wacce zuwa yanzu ta saki laɓen bakinta na ƙasa, wani irin yawu mai cike da mayataccen kwaɗayi ne ya tsinko mata, har yana ɗan sauƙowa kan lips ɗin ta.
Cikin sauri Khausar ta miƙe jin Lamido yana cewa.
“Mamana tashi ku tafi”.
Ai kafin ma ya rufe bakinsa, tuni ta fita tana mai cewa.
“Toh Abba”.
Ita kuwa Dadu wani nannauyan numfashin ta sauƙe tare da juyowa takalli ɗan nata, dake miƙa mata cup ɗin tea.
Cikin diriricewa tace.
“A'a bana buƙatar abin zaƙi, a kawo min abu mai yaji-yaji”.
Cike da biyayya yace.
“Toh”.
Kana ya miƙe ya fita.