Sashe 66
Sakayyah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kallon Habu tayi kana tace.
“Haba kaja motar mu tafi”.
Da mamaki Habu drive ya kalleta kana yace.
“Haba Amina taya zamu tafi mu barta anan dubi hadarin daya taso sannan babu kowa a haraban makarantar ya za'ayi mutafi ne”.
Harara ta galla masa kana tace.
“Mu tafi kuma wallahi idan ka ƙi na rantse da Allah saina sa Ummah tasa akoreka”.
Ahankali Haiydar ya juya ya kalli Amina wanda tun da suka fara magana bai sa baki ba yace.
“Haba Addah Amina Meyesa haka Fisabilillah ai koma menene bai kamata ki hanata shiga mota ba dubi hadari fa kuma kin san yadda take tsoron yanayin ruwan sama”.
Harara ta watsa masa kana tace.
“Rufe min baki an hanata ɗin rufe min baki ɗan Iskan yaro zaka nuna min ƴan Ubanci kenan ruwan ya cinyata, ta mutuma kawai kowa ya huta”.
Da ɓacin rai Afuskarsa ya kalleta kana yace.
“Ni dai bazan nuna miki ƴan Ubanci ba, saboda bamu tashi da shiba, kuma wallahi idan na koma gida na faɗawa Ummah ma ke kanki kinsan sai tayi miki faɗa”.
Dogon tsaki taja tare da cewa.
“Kayi sauri kada ƙuda ya rigaka”.
Jin haka yasa Haiydar yin shiru sai kuma ya kalli Amina tare da cewa. “Matsa min In ɗauki jakata bazan iya tafiya in barta anan ba”.
Girgiza kai Khausar tayi kana tace.
“A'a Haidar kada ka ɗauka ka shiga dasu Ramadan ku tafi nima yanzu zan biyo bayanku”.
Amina kuwa kallon Habu Driver tayi kana tace.
“Mu tafi”.
Jin haka yasa Khausar jan marfin motar tare da rufewa kana tace.
“Pless dan Allah Haiydar zauna ku tafi, in Sha Allah babu abinda zai sameni”.
Dole ya zauba ba don ya soba,
Shi kuwa Habu ba yanda ya iya haka yaja motar ya tafi.
*Yar uwa littafin SAKAYYAH na kuɗine daga wannan page ɗin na gama Free page, in dai kin ganshi a waje to na satane, a Groups ɗina na sakayya ne ɗai ya halatta, 1k ne biya ki karanta cikin Salamah 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA ban yafe ba a karanta min littafi ba'a biya ba in kin tura kuɗin ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276*
Khausar kuwa shiru tayi tare da bin motar da kallo har ya fice aharabar makarantar, ahankali ta juya ta kalli cikin makantar babu ɗalibi ko ɗaya duk sun watse haka zalika ma Malamai duk sun watse shiru tayi sai kuma ta ɗaga kanta sama ganin yanda hadari ya taso ga iska dake kaɗawa da ƙarfi.
Tamkar kazar da ƙwai ya fashewa aciki haka ta fara jan ƙafanta har ta fice acikin Makarantar tsayawa tayi abakin titin koda zata samu Napep amma takai minti biyar babu abin hawan da yazo ya gifta sakamakon hadari daya taso sosai a garin yasa dukkan ababe hawa tsagaita zirga-zirga tana nan tsaye har aka fara ɗan yayyafi hakan yasa ta fara tafiya ahankali a gefen titin.
Ba tayi nisa da makarantar ba taji an buɗe gate ɗin makarantar da ɗan sauri ta juya, akan motar Moddibo Idanunta suka sauƙa da sauri ta kawar da kanta gefe kana ta cigaba da tafiya.
Acikin mota kuwa Moddibo ne da M Jameel yayin da Moddibo ke Driving M Jameel na gefen me zaman banza.
Kallo ɗaya Moddibo yayiwa bayanta ya ganeta, baki ya taɓe Aransa yace yau kuma wannan wani sabon rashin kunya tayi musu suka sauƙeta, sai kuma ya ɗage kafarɗarsa alamun ita ta jiyo.
M Jameel kuwa sam bai ganeta ba saida suka gifta wajenta sannan yaga fuskarta.
Da mamaki ya furta.
“A'a Lelewal”.
Cikin sauri ya ɗaura hannunsa kan Moddibo tare da cewa.
“A.J tsaya Please dubi duk ɗalibai sun watse amma sai ita kaɗai mai ya tsayar da ita anan kuma ga hadari baƙiƙƙirin dubi fa yanda garin yayi duhu ko Babba hadarin na bashi tsoro yakeyi!”.
Juyawa Moddibo yayi tare da Kallonsa cikin yanayin nutsuwarsa yace.
“To ina ruwanka da ita!?”.
Wara Ido M Jameel yayi kana yace.
“Ban gane ina ruwana da ita ba? ɗalibarmu cefa! sannan kullum a mota ake kawo su sannan zuwa ake aɗauke su, kana mun ganta ba'a tafi da ita ba sannan ka duba ita kaɗai ce a layin nan dubi fa yanda layin babu kowa”.
Kallon gefen Ido Moddibo yayi masa kana ya taɓe baki.
Da sauri M Jameel ya cigaba da cewa.
“Haba A.J ya za'ayi kace haka?”.
Moddibo kuwa juya idanunsa yayi kana yace.
“Toh Meye haɗin mu da ita? kasan Meye Uzurin daya tsayar da ita?
Sannan kasan Meye dalilin tsayuwarta! Wata ƙil ma wani bishiyoyin anguwar takeson hawa”.
Girgiza kai M Jameel Yayi kana yace.
“Ai koma mene sai mu tsaya mu tambayeta ko?”.
Kallonsa Moddibo yayi kana yace.
“Nifa bazan tsaya ba”.
Langwaɓar da kai M Jameel yayi kana cikin sanyin murya yace.
“Dan Allah A.J da darajar Annabi Muhammad (S.A.W) mu taimaki yarinyar nan.
Yanzu idan Asma'u ce zaka iya barin ta awajen nan ne?”.
Da sauri Moddibo ya kallesa kana yace.
“Asma'u kuma mai ma zai tsayar da ita anan mai zai haɗa ta faɗa da wasu har tayi musu rashin kunya su sauƙeta amota, ai Asma'u baza ta kasance haka bama!”.
Sake Langwaɓar da kai M Jameel yayi kana yace.
“Amma kayi tunani ƴa mace ce ita ko addininmu ya koyar mana da kula dasu da kuma kula da al'amuran daya shafesu A.J bai kamata ba na roƙe ka dan Allah ba danni ba kuma badan ita ba dan Allah da kuma darajar Manzon mu kayi haƙuri ka tsaya! In ma bazaka ɗauketa ba, ni ka sauƙin bazan iya tafiya in bar Khausy cikin wannan yanayin A.J bazan iya barin ta ananba”.
Ya ƙarashe mgnar cikin wata iriyar raunatacciyar murya mai fito da sirrin dake binne cikin zuciyarsa.
Hannu Moddibo ya sanya tare da dafe goshinsa alamar ya gaji da damuwar M Jameel ahankali yasanya lallausan tafin hannunsa ya shafa sajensa ba tare da yace komai ba ya taka burki ya tsaya.
Yana mai kallon yadda M Jameel ya sauƙe numfashi.
Ganin ya tsaya ya sanya M Jameel sakin murmushi tare da buɗe motar ya fita cikin sassarfa da ɗan gudu ya nufi inda Khausar take dan sun ɗanyi mata nisa kana ga yayyafin da aka fara da ƙarfi da kuma rugugi alamar ana gaba da kecewa da ruwa mai ƙarfi.
Moddibo kuwa da kallo yabi M Jameel ta mirror motarsa.
Aransa yace Ohhh J ji yanda yake gudu kamar wani yaro ko ya gani a wannan ƴar nan har yake jinta cikin zuciyarsa.
Khausar kuwa tana ganin M Jameel ta saki nannauyan Ajiyar zuciya tare da cewa.
“Yaya Jameel”.
Cike da kulawa ya kalleta tare da cewa.
“Lelewal mai yafaru yana ganki anan ke kaɗai, bayan baki ɗaya student's sun watse”.
Ahankali ta kallesa sai kuma tayi saurin lumshe Idanunta tare da cewa.
“Wallahi Yaya Jameel Amina ce ta hanani shiga motarsu yau kam masifa take ji dashi”.
Girgiza kai yayi tare da faɗin.
“Subhanallah gaskiya bata kyauta ba, maza zo ki shigo mota mutafi”.
“Toh”,tace tare da bin bayansa cikin sassarfa yayinda ko wanne gaɓa na jikinta ke motsawa.
Ɗan guntun tsaki Modibbo yaja, tare da kauda kansa daga kan madubin, ganin yadda suka wani jero da J ɗinsa.
Suna isa wajen motar M Jameel ya buɗe mata bayan gefen da Modibbo yake tashiga, sannan shi kuma ya zagaya ya shiga a hankali Khausar ta ɗaga kanta tare da kallon gaban motar ai kuwa idanunta suka sauƙa akan Moddibo da batasan yana cikin motar Ba gashi ta zauna asaitin bayansa.
A kuma dai-dai lokaci ruwa ya kece tamkar da bakin ƙorya, key Moddibo yayi wa motar tare da figarta a dan guje suka fara tafiya.
Kallon Moddibo M Jameel yayi kana yace.
“A.J kasan zamu biya ta gida ka sauƙe ni tun safe Abba ke kirana wai Inje Yana son magana dani muje ka sauƙe ni”.
Kallon sa Moddibo yayi tare da cewa.
“Baza ka bari sai anjima ba?”.
Girgiza kai M Jameel Yayi kana yace.
“A'a muje dan Allah ka sauƙe ni saboda bansan me yake sona dashi ba yanata ne mana tun tuntuni”.
Kai Moddibo ya gyaɗa kana yace.
“Toh naji”.
Yayi mgnar tare da haharan M Jameel ɗin,
Sannan ya cigaba da Driving ɗin sa.
Shi kuwa M Jameel murmushin yayi tare da ɗan mishi alamun zunɗe.
*Littafin SAKAYYAH na kuɗine daga wannan page ɗin na gama Free page, daga gobe in dai kinga littafin SAKAYYAH a wani wuri to na satane, yar uwa ki biya 1k ne kacal ki karanta cikin Aminci ba haƙƙin kowa a kanki littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa kada ki karanta in baki biyaba 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA, sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276*
Khausar dake zaune abayan motar kuwa ƙanƙame jikinta tayi saboda yanda ɗumin motar ke ratsata sam cikin motar babu sanyi da yawa ba kamar waje da iska ke kaɗawa ba.
Sanyayyar Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da gyara Questions peper dake hannunta ta sake rungumesu aƙirji sai kuma ta gyara zaman wuyan hijabinta wanda har tattausan gashin gaban goshinta mai sansti ya bayyana.
Baki ɗaya cikin motar a wadace yake da wani irin ni'imtaccen sanyayyan ƙamshi mai daɗin shaƙa yakeyi, Ahankali Khausar ta maida kallon kan bayan Moddibo da take fuskanta sanye yake cikin ɗanyen Boyel fari ƙal yasha guga sosai yayin da kansa ke sanye da hula zanna bukar wadataccen sumar ƙeyansa ya kwanto lib-lib gwanin kyau sai sheƙi da ƙyalli yake zubawa.
Ƙeyar tasa ta zubawa ido sai kuma ta gallawa ƙeyar tasa harara tare da murguɗa masa baki.
“Haba kaja motar mu tafi”.
Da mamaki Habu drive ya kalleta kana yace.
“Haba Amina taya zamu tafi mu barta anan dubi hadarin daya taso sannan babu kowa a haraban makarantar ya za'ayi mutafi ne”.
Harara ta galla masa kana tace.
“Mu tafi kuma wallahi idan ka ƙi na rantse da Allah saina sa Ummah tasa akoreka”.
Ahankali Haiydar ya juya ya kalli Amina wanda tun da suka fara magana bai sa baki ba yace.
“Haba Addah Amina Meyesa haka Fisabilillah ai koma menene bai kamata ki hanata shiga mota ba dubi hadari fa kuma kin san yadda take tsoron yanayin ruwan sama”.
Harara ta watsa masa kana tace.
“Rufe min baki an hanata ɗin rufe min baki ɗan Iskan yaro zaka nuna min ƴan Ubanci kenan ruwan ya cinyata, ta mutuma kawai kowa ya huta”.
Da ɓacin rai Afuskarsa ya kalleta kana yace.
“Ni dai bazan nuna miki ƴan Ubanci ba, saboda bamu tashi da shiba, kuma wallahi idan na koma gida na faɗawa Ummah ma ke kanki kinsan sai tayi miki faɗa”.
Dogon tsaki taja tare da cewa.
“Kayi sauri kada ƙuda ya rigaka”.
Jin haka yasa Haiydar yin shiru sai kuma ya kalli Amina tare da cewa. “Matsa min In ɗauki jakata bazan iya tafiya in barta anan ba”.
Girgiza kai Khausar tayi kana tace.
“A'a Haidar kada ka ɗauka ka shiga dasu Ramadan ku tafi nima yanzu zan biyo bayanku”.
Amina kuwa kallon Habu Driver tayi kana tace.
“Mu tafi”.
Jin haka yasa Khausar jan marfin motar tare da rufewa kana tace.
“Pless dan Allah Haiydar zauna ku tafi, in Sha Allah babu abinda zai sameni”.
Dole ya zauba ba don ya soba,
Shi kuwa Habu ba yanda ya iya haka yaja motar ya tafi.
*Yar uwa littafin SAKAYYAH na kuɗine daga wannan page ɗin na gama Free page, in dai kin ganshi a waje to na satane, a Groups ɗina na sakayya ne ɗai ya halatta, 1k ne biya ki karanta cikin Salamah 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA ban yafe ba a karanta min littafi ba'a biya ba in kin tura kuɗin ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276*
Khausar kuwa shiru tayi tare da bin motar da kallo har ya fice aharabar makarantar, ahankali ta juya ta kalli cikin makantar babu ɗalibi ko ɗaya duk sun watse haka zalika ma Malamai duk sun watse shiru tayi sai kuma ta ɗaga kanta sama ganin yanda hadari ya taso ga iska dake kaɗawa da ƙarfi.
Tamkar kazar da ƙwai ya fashewa aciki haka ta fara jan ƙafanta har ta fice acikin Makarantar tsayawa tayi abakin titin koda zata samu Napep amma takai minti biyar babu abin hawan da yazo ya gifta sakamakon hadari daya taso sosai a garin yasa dukkan ababe hawa tsagaita zirga-zirga tana nan tsaye har aka fara ɗan yayyafi hakan yasa ta fara tafiya ahankali a gefen titin.
Ba tayi nisa da makarantar ba taji an buɗe gate ɗin makarantar da ɗan sauri ta juya, akan motar Moddibo Idanunta suka sauƙa da sauri ta kawar da kanta gefe kana ta cigaba da tafiya.
Acikin mota kuwa Moddibo ne da M Jameel yayin da Moddibo ke Driving M Jameel na gefen me zaman banza.
Kallo ɗaya Moddibo yayiwa bayanta ya ganeta, baki ya taɓe Aransa yace yau kuma wannan wani sabon rashin kunya tayi musu suka sauƙeta, sai kuma ya ɗage kafarɗarsa alamun ita ta jiyo.
M Jameel kuwa sam bai ganeta ba saida suka gifta wajenta sannan yaga fuskarta.
Da mamaki ya furta.
“A'a Lelewal”.
Cikin sauri ya ɗaura hannunsa kan Moddibo tare da cewa.
“A.J tsaya Please dubi duk ɗalibai sun watse amma sai ita kaɗai mai ya tsayar da ita anan kuma ga hadari baƙiƙƙirin dubi fa yanda garin yayi duhu ko Babba hadarin na bashi tsoro yakeyi!”.
Juyawa Moddibo yayi tare da Kallonsa cikin yanayin nutsuwarsa yace.
“To ina ruwanka da ita!?”.
Wara Ido M Jameel yayi kana yace.
“Ban gane ina ruwana da ita ba? ɗalibarmu cefa! sannan kullum a mota ake kawo su sannan zuwa ake aɗauke su, kana mun ganta ba'a tafi da ita ba sannan ka duba ita kaɗai ce a layin nan dubi fa yanda layin babu kowa”.
Kallon gefen Ido Moddibo yayi masa kana ya taɓe baki.
Da sauri M Jameel ya cigaba da cewa.
“Haba A.J ya za'ayi kace haka?”.
Moddibo kuwa juya idanunsa yayi kana yace.
“Toh Meye haɗin mu da ita? kasan Meye Uzurin daya tsayar da ita?
Sannan kasan Meye dalilin tsayuwarta! Wata ƙil ma wani bishiyoyin anguwar takeson hawa”.
Girgiza kai M Jameel Yayi kana yace.
“Ai koma mene sai mu tsaya mu tambayeta ko?”.
Kallonsa Moddibo yayi kana yace.
“Nifa bazan tsaya ba”.
Langwaɓar da kai M Jameel yayi kana cikin sanyin murya yace.
“Dan Allah A.J da darajar Annabi Muhammad (S.A.W) mu taimaki yarinyar nan.
Yanzu idan Asma'u ce zaka iya barin ta awajen nan ne?”.
Da sauri Moddibo ya kallesa kana yace.
“Asma'u kuma mai ma zai tsayar da ita anan mai zai haɗa ta faɗa da wasu har tayi musu rashin kunya su sauƙeta amota, ai Asma'u baza ta kasance haka bama!”.
Sake Langwaɓar da kai M Jameel yayi kana yace.
“Amma kayi tunani ƴa mace ce ita ko addininmu ya koyar mana da kula dasu da kuma kula da al'amuran daya shafesu A.J bai kamata ba na roƙe ka dan Allah ba danni ba kuma badan ita ba dan Allah da kuma darajar Manzon mu kayi haƙuri ka tsaya! In ma bazaka ɗauketa ba, ni ka sauƙin bazan iya tafiya in bar Khausy cikin wannan yanayin A.J bazan iya barin ta ananba”.
Ya ƙarashe mgnar cikin wata iriyar raunatacciyar murya mai fito da sirrin dake binne cikin zuciyarsa.
Hannu Moddibo ya sanya tare da dafe goshinsa alamar ya gaji da damuwar M Jameel ahankali yasanya lallausan tafin hannunsa ya shafa sajensa ba tare da yace komai ba ya taka burki ya tsaya.
Yana mai kallon yadda M Jameel ya sauƙe numfashi.
Ganin ya tsaya ya sanya M Jameel sakin murmushi tare da buɗe motar ya fita cikin sassarfa da ɗan gudu ya nufi inda Khausar take dan sun ɗanyi mata nisa kana ga yayyafin da aka fara da ƙarfi da kuma rugugi alamar ana gaba da kecewa da ruwa mai ƙarfi.
Moddibo kuwa da kallo yabi M Jameel ta mirror motarsa.
Aransa yace Ohhh J ji yanda yake gudu kamar wani yaro ko ya gani a wannan ƴar nan har yake jinta cikin zuciyarsa.
Khausar kuwa tana ganin M Jameel ta saki nannauyan Ajiyar zuciya tare da cewa.
“Yaya Jameel”.
Cike da kulawa ya kalleta tare da cewa.
“Lelewal mai yafaru yana ganki anan ke kaɗai, bayan baki ɗaya student's sun watse”.
Ahankali ta kallesa sai kuma tayi saurin lumshe Idanunta tare da cewa.
“Wallahi Yaya Jameel Amina ce ta hanani shiga motarsu yau kam masifa take ji dashi”.
Girgiza kai yayi tare da faɗin.
“Subhanallah gaskiya bata kyauta ba, maza zo ki shigo mota mutafi”.
“Toh”,tace tare da bin bayansa cikin sassarfa yayinda ko wanne gaɓa na jikinta ke motsawa.
Ɗan guntun tsaki Modibbo yaja, tare da kauda kansa daga kan madubin, ganin yadda suka wani jero da J ɗinsa.
Suna isa wajen motar M Jameel ya buɗe mata bayan gefen da Modibbo yake tashiga, sannan shi kuma ya zagaya ya shiga a hankali Khausar ta ɗaga kanta tare da kallon gaban motar ai kuwa idanunta suka sauƙa akan Moddibo da batasan yana cikin motar Ba gashi ta zauna asaitin bayansa.
A kuma dai-dai lokaci ruwa ya kece tamkar da bakin ƙorya, key Moddibo yayi wa motar tare da figarta a dan guje suka fara tafiya.
Kallon Moddibo M Jameel yayi kana yace.
“A.J kasan zamu biya ta gida ka sauƙe ni tun safe Abba ke kirana wai Inje Yana son magana dani muje ka sauƙe ni”.
Kallon sa Moddibo yayi tare da cewa.
“Baza ka bari sai anjima ba?”.
Girgiza kai M Jameel Yayi kana yace.
“A'a muje dan Allah ka sauƙe ni saboda bansan me yake sona dashi ba yanata ne mana tun tuntuni”.
Kai Moddibo ya gyaɗa kana yace.
“Toh naji”.
Yayi mgnar tare da haharan M Jameel ɗin,
Sannan ya cigaba da Driving ɗin sa.
Shi kuwa M Jameel murmushin yayi tare da ɗan mishi alamun zunɗe.
*Littafin SAKAYYAH na kuɗine daga wannan page ɗin na gama Free page, daga gobe in dai kinga littafin SAKAYYAH a wani wuri to na satane, yar uwa ki biya 1k ne kacal ki karanta cikin Aminci ba haƙƙin kowa a kanki littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa kada ki karanta in baki biyaba 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA, sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276*
Khausar dake zaune abayan motar kuwa ƙanƙame jikinta tayi saboda yanda ɗumin motar ke ratsata sam cikin motar babu sanyi da yawa ba kamar waje da iska ke kaɗawa ba.
Sanyayyar Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da gyara Questions peper dake hannunta ta sake rungumesu aƙirji sai kuma ta gyara zaman wuyan hijabinta wanda har tattausan gashin gaban goshinta mai sansti ya bayyana.
Baki ɗaya cikin motar a wadace yake da wani irin ni'imtaccen sanyayyan ƙamshi mai daɗin shaƙa yakeyi, Ahankali Khausar ta maida kallon kan bayan Moddibo da take fuskanta sanye yake cikin ɗanyen Boyel fari ƙal yasha guga sosai yayin da kansa ke sanye da hula zanna bukar wadataccen sumar ƙeyansa ya kwanto lib-lib gwanin kyau sai sheƙi da ƙyalli yake zubawa.
Ƙeyar tasa ta zubawa ido sai kuma ta gallawa ƙeyar tasa harara tare da murguɗa masa baki.