← Book details Sakayyah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 87 OF 114

Sashe 87

Sakayyah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Anutse Khausar ta ɗago manyan Idanunta dake cike da mamaki ta tsaida su akan sa.
Ganin kallon data ke jifansa dashi yasa ya dake tare da langwaɓar da kai kana ya marairaice murya tare da cewa.
“Wallahi na rantse miki da Allah My Khausi gaskiya nake faɗa miki ki yarda dani”.
Still Ido Khausar ta zuba masa aranta tace Ohhh lalle Uncle Naseer baya tsoron Allah ya aikata abu sannan yazo yana rantsewa da girman Allah saboda baisan girman Allah ba.

Hannun Ramadan ya riƙe acikin nasa tare da sake Matsawa gabanta kana yace.
“Na rantse miki da Allah My Khausi ban aikata abinda kike zargina ba wallahi tallahi ai babu wani abu sama da Allah?”.
Wani irin kallo ta watsa masa tare da Kallonsa kana tace.
“Ni dai awajena da duk wani Muminin duniya babu wani abu sama da Allah.
Amma awajen matsafi yana da abu da yake ganin zai bashi abu sama da Allah yana da dodon tsafi! Kuma dama yawan rantsuwa a mgn ai masiface”.

Zare Ido Uncle Naseer yayi cikin yanayin ruɗewa ya kalleta tare da cewa.
“Innalillahi wa'inna Ilahi rajiu'n Khausar!, Khausar!!, Khausar!!! Nine matsafi?, Hasbunallahu wani'imal wakil, ya Salam Khausar Ashe dama kallon da kike min kenan?. Kai cona da wannan zargi da matar aurena take min”.

Lokaci ɗaya jikin Khausar yayi masifsr sanyi kallon fuskarsa tayi taga duk yanda ya wani susuce aranta tace To Uncle Naseer ko dai dan naji tsoron abin ne amma kayi haƙuri na zarge ka akan abinda baka aikata ba.
Uncle Naseer kuwa jin bata ce komai ba yasa ya sake narkar da murya tare da cewa.
“Sam ban taɓa zaton zaki yimin irin wannan mummunar fahimtar ba, My dear koda ace ina tsafi tasirin soyayyarki ba zaisa inyi tsafi dake ba shin idan nayi tsafi dake dawa zan rayu? kece rayuwata My life is nothing without you Khausi”.

Dai-dai lokacin Mommy ta fito daga Bedroom.Jin motsin fitowarta yasa Uncle Naseer ya juya tare da dai-dai-ta nutsuwarsa kana yace.
“Mommy ya mai jiki ashe abinda yafaru Allah ya sawwaƙa”.
Ba yabo ba fallasa Mommy tace.
“Ameen mun gode”.
Kana ta nufi kichen tare da cewa.
“Khausar zo muje mu ƙara sa aiki”.
Ahankali Khausar ta kalleta tare da cewa.
“Toh”.
Mommy kana ta miƙe idanu ya zuba mata har ta ɓacewa Kallonsa.
Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da miƙewa ya fita.

Acan ɓangaren Moddibo kuwa Anutse suka fito daga masallaci bayan sun idar da Sallar Isha'i suka nufi gida suna shiga coumpund ɗin M Jameel ya tsaya.
Anutse Moddibo ya juya ya kallesa tare da cewa.
“Ya dai J”.
Lumshe idanu M Jameel Yayi kana cikin sanyin Murya yace.
“A.J muje wajen Ummi mana nayi missing ɗin ta”.
Kallonsa Moddibo yayi kana yace.
“Kai J ina yau da safe ma kafin muje makaranta sai da muka biya?”.
Kai M Jameel ya gyaɗa kana yace.
“A.J Ina son ganinta ne wallahi A.J inajin zanyin Aure kwanan nan”.
Cike da Mamaki Moddibo ya juya ya kallesa kana yace.
“Aure J?”.
Kai M Jameel ya gyaɗa kana yace.
“Eh zanyi Aure”.

Jinjina kai Moddibo yayi kana yace.
“Toh babban magana J wannan magana ce mai girma ai mushiga daga ciki muyi ta”.
Girgiza kai M Jameel Yayi kana yace.
“A'a mushiga mota dai muje muyi ta agidan Ummi”.
Wara Ido Moddibo yayi tare da saurin kallon M Jameel kana yace.
“J baka da kunya agaban Ummi?”.
Murmushi M Jameel Yayi tare da faɗin.
“A.J ni kake cewa bani da kunya ba gwara niba cewa nayi inason Aure, kaifa jikinka ne ya nuna kana son Aure na riga dana fadawa Innayi na faɗa mata komai na kuma zaɓa maka matar da zaka aura ma”.
Cike da mamaki Moddibo ya juya ya kallesa tare da sakar masa da murmushi kana ya shafa sajensa tare da cewa.
“Iyeee sannu Babana”.
Dariya M Jameel Yayi kana yace.
“Ayaaa kana wasa ne?, Wallahi da gaske nayi maka zaɓin mata kuma na faɗawa Innayi sannan ta aminta da hakan kana na shaida mata cewa A.J ɗina yana ɓuƙatar Aure”.

Juyawa Moddibo yayi ya kallesa tare da Matsawa kusa dashi kana ya ɗan mari fuskarsa.
M Jameel kuwa dariya ya fashe dashi wanda ya bayyanar da Fararen haƙoransa kana ya shiga tsinkar fulawar dake wajen yana sunsunawa tare da watsa su sama ga hasken farin wata da da gloves ɗin ya haska wajen.
Moddibo kuwa idanu ya zubawa M Jameel yana sakin murmushi akai-akai wani irin amintaccen kyau M Jameel ya masa fuskarsa kuwa sheƙi da ƙyalli takeyi more especially gishinsa, lumshe idanu Modibbo yayi kana Aransa yace.
“Masha Allah J kayi kyau sosai baka taɓa yin kyau irin na yau ba”.
M Jameel kuwa still dariyar ya cigaba dayi yana mai buɗe hannayensa tare da cewa.
“Allah ko A.J nayi kyau, kace inje amaryata ta ganni”.
Ahankali Moddibo ya sauke Ajiyar zuciya tare da cewa.
“Au ashe mgnar ta fito fili.”
Cikin sakin yalwataccen murmushin da yasa kyawawan haƙoransa bayyana ya gyaɗa mishi kai.
Shi kuwa Modibbo a hankali yace.
“Sosai ma kuwa J kayi kyau, fara'a nayi maka kyau idan kana dariya kana kyau sosai”.
Ahankali M Jameel ya ɗago ya kallesa still Yana cigaba da dariyar yace.
“Ai kaima in zaka yi fara'a haka yana maka kyau A.J”.
Girgiza kai Moddibo yayi har zuwa lokacin da murmushi afuskarsa yace.
“Bazan iya dariya yanda kake yi haka ba J”.
Wara Ido M Jameel Yayi kana cikin dariyar yace.
“Zaka iya A.J”.
Harɗe hannunsa yayi a ƙirjinsa tare da ɗan jingina da jikin mota, kana ya zubawa M Jameel ɗin idanu yana kallon yadda yaketa dariya har maƙolloton wuyanshi yana ɗan haurawa sama kana ya yi ƙasa, sannan haƙoransa nata sheƙi.
Innayi ce ta fito daga sashen ta tare da kallon M Jameel kana tace.
“A'a Jamilu yau mai ya maka daɗi haka?”.
Cikin dariya sosai ya kalli Moddibo kana ya nuna masa saitin Dick ɗin sa da ido.
Da sauri Moddibo ya sunkuyar da kansa tare da kallon inda M Jameel ya nuna da sauri ya lumshe Idanunsa ganin yanda Dick ɗinsa ke miƙe tun ranan da abin ya faru tsakanin sa da Khausar har yau Dick ɗin sa bai sake kwanciya ba koda na second ɗaya sam yaƙi kwanciya ya koma Normal yanda yake cikin dabara ya sanya ƙafarsa ɗaya agaba ɗaya abaya ya matse cinyarsa kana ya cije lips ɗin sa.

Wani sabon dariya M Jameel ya fashe dashi tare da riƙe cikinsa kana ya kalli Innayi tare da cewa.
“Wayyo Allah cikina hahahaha khhykhy Innayi wai dan nace masa na zaɓa masa mata shine yake cewa, nine Babansa kuma na faɗa masa akan na faɗa miki cewa wallahi Aure yakeso ya girma yanzu shine yake wata magana Innayi ki faɗa masa bana zaɓa masa mata ba?”.

Murmushi Innayi tayi kana tace.
“Sosai ma”.
Moddibo kuwa sajensa ya shafa tare da kallon su kana yace.
“Iyeee kune ma masu tsara min rayuwata toni nace muku ina bukatar aure ne?”.
Still cikin ƙyelƙyala dariya sosai M Jameel yace.
“Ai bai sai kafaɗa da bakin ka ba A.J dama ai body language ɗabi'ar kace to ganganar jikinka ta faɗa min kana son Aure”.
Moddibo kuwa cikin sauri ya juya tare da nufar mota jin M Jameel na Shirin tona masa asiri batare daya juya ba yace.
Toh kazo mu tafi Innayi bari muje gidan Ummi”.
Kai Innayi ta gyaɗa da murmushi afuskarta tace.
“Toh Allah ya tsare”.
Bayansa M Jameel yabi tare da buɗe motar yashiga har suka isa gidan da zaran M Jameel ya Kalli Moddibo zaiyi dariya shi kuwa Moddibo sai ya sakar masa da murmushi.
Suna isa Moddibo yayi Parking suka fita akan baranda suka hango Ummi hannunta riƙe da kayan shanya da alama akan igiya ta ɗebosu, ƙara sawa Moddibo yayi kana yace.
“Ummi kawo in karɓa miki”.
Miƙa masa yayi.
Cike da so M Jameel yace.
“Umminaaa”.
Kallonsa Ummi tayi tare da ƙara sa shiga falon ya suka biyo bayan ta atare.

Akan capet Ummi ta zauna tare da jingina bayanta da jikin kushin kana ta miƙe ƙafafunta ahankali Moddibo ya zauna daga gefenta tare da ajiye kayan wankin ganin kayanta ne yasa ya fara ninkewa.
M Jameel kuwa ahankali ya kwanta tare da ɗaura kansa akan cinyar Ummi kana ya ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya kana ya lumshe Idanunsa tare da cewa.
“Ummina kenan”.

Ahankali Ummi ta juya ta kalli Moddibo kana ta mayar da kallonta kan M Jameel sai kuma ta ɗaga kanta ta kalli haɗeɗɗen agogon dake manne abango kana ta sauƙe Idanunta ƙasa tare da cewa.
“Ayana yin garin nan da yake ga alamun yau akwai hadari sannan baku zo da wuri ba dubi time fa har kusan 8:30 kodai zamu kwana ne?”.

Murmushi M Jameel Yayi tare da ɗago kai ya kalleta kana ya langwaɓar da kai tare da cewa.
“Ummi dana fi kowa farin ciki ace yau gani gaki muna kwana gida ɗaya”.
Juyawa yayi ya kalli Moddibo kana yace.
“Shiyasa ma nake faɗawa A.J nifa Aure zanyi”.

Cikin sauri Ummi ta juya ta kallesa kana cike da Mamaki wannan shine karo na biyu da yake faɗa mata Kalmar yana son Aure Girgiza kai tayi kana tace,
“Jamiluuuu”,Ta faɗa kai tsaye ta rasa Meyesa acikin kwanakin take kiran sunan sa kai tsaye.

Dariya M Jameel ya fashe dashi sosai yake ƙyalƙyala dariya harda kaɗa ƙafa.
Asma'u da Bashir kuwa jiyo sautin dariyar sa yasa suka fito daga Bedroom tare da zama daga gefensu cike da girmamawa suka gaishesu atare.
Ahankali ya kalle tare da sakar musu da murmushi kana yace.
“Ƴan ƙanne na”.
Sai kuma ya juya ya kalli Ummi dake murmushi kana yace.
“Wallahi Ummi dagaske aure nake so”.
Chapter 87 · 0% Book details