Sashe 101
Sakayyah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Har naji hankali na ya dan kwanta wayar J ɗina ya shiga, kinga farko kafin mu rasa shi kiran wayarsa muka fara rasawa Ummi, yanzu kuma Insha Allah mun samu kiran wayarsa shi zamu ƙara samu next da izinin Ubangiji”.
Kai Ummi ta gyaɗa tare da cewa.
“Ameen”.
Cikin jin sanyi Asma'u tayi murmushi kana tace.
“Alhamdulillah wayar Yah Jameel ya shiga gaskiya munyi farin ciki”.
Malam Ahmad daya fito daga wanka ya fito coumpund ɗin fuskarsa ɗauke da murmushi kana yace.
“Alhamdulillah Asma'u maza kawo musu abinci suci tunda mun samu wayar Jameelu ya shiga maza kawo musu abinci”.
Moddibo kuwa kallon Malam Ahmad yayi kana yace.
“Nikam ma Malam baki ɗaya cikina ya cushe baki ɗaya farin ciki ya cika min cikana”.
Murmushi Ummi tayi kana tace.
“Nima cikina ya cika baki ɗaya farin ciki nake ji”.
Jinjina kai Malam Ahmad yayi tare da cewa.
“Dan Allah ku zauna kuci abinci wayarsa muka fara rasawa yanzu kuma wayarsa muka faru samu insha Allah shi ma zamu sameshi nan kusa ”.
Dai-dai lokacin Asma'u tazo ta ajiye musu abincin.
Tun ɓatan M Jameel sai yau Ummi da Moddibo sukaci abinci mai nauyi acikinsu duk da ba dayawa suka ciba.
Miƙewa Moddibo yayi kana yace.
“Ummi bari naje in faɗawa Innayi ta tayamu farin ciki”.
Kai Ummi ta gyaɗa tare da faɗin.
“Aikam dai gwara kaje”.
Ficewa yayi tare da tafiya Driving yake Cike da farin ciki har ya isa gida yana zuwa ya shiga sashen Innayi.
Innayi dake ki shimfiɗe ta miƙe kana tace.
“Alhamdulillah Moddibo naga kana cikin farin ciki da alama akwai labari mai daɗi?”.
Kai ya gyaɗa still Fuskarsa ɗauke da murmushi yace.
“Innayi wayar J ɗina ya shiga yau”.
Kai Innayi ta gyaɗa tare da cewa.
“Alhamdulillah gaskiya munyi farin ciki. Allah ya bayyanar mana dashi”.
Ameen ya amsa tare da wucewa sashen sa cike da farin ciki yana shiga ɗaki ya kira layin Malam Arɗo.
Malam Arɗo na dagawa yace.
“Malam Alhamdulillah yau wayar J ɗina yashiga a cigaba da taya mu da addu'a a masallacai da makarantu”.
Cike da farin ciki malam Arɗo yace.
“Masha Allah da izinin Ubangiji zai fito Insha Allah zamu cigaba da addu'a”.
Awannan daren haka Moddibo Ummi, Asma'u Bashir malam Ahmad da Innayi suka kwana cike da farin cikin shigar wayar M Jameel.
Yayin da Aɓangaren Abba ya kwana cikin taraddadi da tashin hankali koda ya farka tsakiyar dare kuka yayi ta yi yayin da Hajiya Karima ke kuka tana basa haƙuri kana tana cewa bada niyya tayi ba.
Aɓangaren gidan Lamiɗo ma haka Khausar da Mommy suka kwana azaune da Ramadan da kansa ke masifar ciwo da zaran an bashi maganin da Lamiɗo ya kawo yasha ciwon zai ɗan lafa jimawa kaɗan kuma zai sake tashi tsakiyar dare ya farka ya riƙa kuka dole Ummi ta kira Abba ya kawo masa magani cikin ikon Allah yana sha ciwon kan ya lafa.
Washe gari; Moddibo, Malam Arɗo, Ummi Innayi duk wani makusancin M Jameel na cikin farin ciki kana duk wanda ya kira wayarsa zai shiga sai dai ba aɗagawa Wunin wannan ranan haka Moddibo yayi yana kiran layin M Jameel still ba amsa.
Zuwa yamma jikin Moddibo ya fara sanyi da lamarin ganin yana kiran wayar M Jameel baya shiga lokaci ɗaya tsoro ya fara kamashi hankalinsa ya tashi Misalin ƙarfe goma na dare yana gidan Abba zaune sun kira Jameel kuma sama da sau ashirin kuma duk kiran yana shiga, sau dai ba'a ɗagawa, su kuma masatan basu kiraba.
Yayin da idanun Abba ke kumbure alamar har yanzu jinjinsa bai sauƙa sosai ba.
Cikin mutuwar jiki Moddibo ya koma gida kai tsaye sashen Innayi ya nufa bakinsa ɗauke da Sallama ya shiga.
Innayi dake zaune riƙe da carbi ta amsa masa cikin raunin Murya yace.
“Innayi”.
Kallonsa tayi cike da kulawa kana tace.
“Na'am”.
Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da fesar da numfashi kana cikin sanyin murya yace.
“ Innayi hankalina ya soma tashi wayar J yana shiga ba'a ɗauka sannan mutanen nan basu sake kira ba”.
Ajiyar zuciya Innayi ta sauƙe tare da cewa.
“Ba komai Moddibo Insha Allah ka kwantar da hankalin ka”.
Girgiza kai yayi kana yace.
“Anya kuwa Innayi?”.
Cikin bashi ƙwarin gwiwa tace.
“Ba komai Insha Allah ka cigaba dayi masa addu'a da izinin Ubangiji zai fito yanzu idan sun sake kira kuce musu an samu kuɗin Insha Allah Million biyar bazai gagara ba koda a masallatai anemi temako za'a samu su haɗu”.
Kai ya gyaɗa kana yace.
“Toh Innayi Allah yasa su kira ɗin dan yanzu kam ma cikon Million ukune”.
Cikin jin daɗi Innayi tace.
“Alhamdulillah Allah ya bamu sa'a”.
Amin yace
Sanna ya miƙe ya koma sashen sa cike da damuwa. Washe gari jin sauran kuɗin da ake buƙata, Lamido ya bawa Mommy da kanta ta kaiwa Ummi su sau dai sam basu kuma kiraba.
Haka dai rayuwa ta cigaba da tafiya yau kusan kwana ki shida kenan duk lokacin da aka kira wayar M Jameel zai shiga sai dai ba'a ɗauka.
Yayinda Ramadan kuwa ke kwana da azabebben ciwon kai idan aka bashi magani yasha ciwo ya lafa anjina kaɗan kuma ya sake dawowa.
Ga ɗaya Mommy da kwausar sun shiga damuwa, sun kai asibiti har cikin Taraba anyi hoton kan da duk wani gwaje-gwaje amman babu wani ciwo dake kansa, dan da farima likitocin sunyi zaton brain cancer ne.
baki ɗaya yaron ya fita hayyacinsa saboda tsananin ciwon kai.
Yau kimanin kwana shida kenan da aka fara samun wayar M Jameel na shiga.
Washe garin rana ta bakwai.
Da safe bayan an idar da Sallar Asbah Moddibo na fita a masallaci ya kira wayar M Jameel.
Cike da mmki tsoro ya janye wayar a kunnenshi sabida jin ance masa Switch off.
cikin mutuwar jiki ya nufi gidan Ummi yana shiga ya samu Ummi zaune akan Sallaya hannunta riƙe da Carbi.
Cike da ladabi ya gaisheta kana cikin sanyin murya yace.
“Ummi”.
Kallonsa tayi tare da cewa.
“Na'am Babana”.
Cikin raunin murya yace.
“Ummi na kira wayar J ɗina baya shiga”.
Ahankali Ummi ta jingina kanta da jikin kujeran falon kana tace.
“Nima na kira wayan Jameelu na baya shiga bansan Meyesa ba Allah yasa al'khairi ne”.
Cike da sanyi Middibo yace.
“Amin ya Allah in sha Allah ba komai Ummi”.
Cikin raunin murya Ummi ta lumshe Idanunta tare da cewa.
“Hmmm,Hmmm Ubangiji Allah yabamu ikon cinye jarrabawar da zai jarabce mu”.
Cikin sanyi Moddibo yace.
“Ameen”.
Miƙewa Moddibo yayi kana yace.
“Ummi bari naje gidan Abba naji koshi ya kira ya shiga”.
Kai Ummi ta gyaɗa Muryanta cike da rauni tace.
“Toh”.
Cikin sanyin jiki zuciya cike da karaya Moddibo ya nufi gidan Abba yana shiga coumpund ya ga Abba na ƙoƙarin shiga falo dawowansa daga masallaci kenan.
Ƙara sawa Moddibo yayi tare da miƙa masa hannu sukayi musabaha kana cikin sanyin murya Moddibo yace.
“Abba wayar J ɗina baya shiga”.
Ahankali Abba ya sunkuyar da kansa hawaye masu zafi suka shiga bin kuncinsa Shar-shar-shar kamar ƙaramin yaro baki ɗaya ya rame cikin raunin murya yace.
“Aliyu dama wayar Jameelu da kira yake shiga. Wani sanyi ne dama hankalina ya tashi tun jiya nake kiran wayar baya shiga, dama ni banyi farin ciki da shigan wayar Jameelu ba. Aliyu inaji Ajikina kamar akwai wani abu da bamu san menene ba jikina na bani ko ina Jameelu na yaje baya cikin walwala na rasa tudun dafawa”.
Cikin sauri Moddibo ya runtse Idanunsa zuciyarsa na bugawa da masifaffen ƙarfi kana cikin raunin murya yace.
“Abba insha Allah J yana cikin ƙoshin lafiya mu cigaba da masa addu'a amma nima baki ɗaya hankalina yayi masifar tashi”.
Cikin rauni da tsanananin tashin hankali suka ci-gaba da tattaunawa.
Acan gidan Lamiɗo kuwa Mommy, Khausar da Lamiɗo basu rintsaba a wannan daren.
A kan Ramadan suka kwana yanata kuka baiyi bacci ba.
Washe gari Bayan an idar da sallan Asbah Hajiya Bunayya ta shigo falon Mommy ahankali Ramadan dake kuka ya miƙa mata hannu kana cikin wata raunan'niyar murya mai cike da wahala yace.
“Ummah! Ummah! Kaina zai fashe kaina zai faɗi Wayyo Allah na Kaina! kaina”.
Baki daya jijiyoyin kansa sun tashi sunyi ruɗu ruɗu dasu yayinda idanunsa sukayi ja.
Cike da tausayawa Khausar ta ɗaura tafin hannunta na dama akan goshinsa Idanunta cike da ruwan hawaye kasa riƙe hawayen ta tayi jin yanda kan ke harbawa da masifar ƙarfi.
Kuka sosai Ramadan keyi kana cikin tsananin radaɗin ciwo ya riƙo hannun Mommy kana yace.
“Wayyo Mommy Kaina zai fashe. Mommy Kaina Wayyo zan mutu Mommy Zan mutufa”.
Wani irin miƙa Ramadan yayi tare da cewa.
“Momyyyyy zan mutuuuu”.
Cikin sauri Lamiɗo da yanzu ya shigo ya karɓesa ganin yanda idanun yaron suka juya da sauri ya fara ɗan bubbuga kumatunsa yana cewa.
“Ramadan! Ramadan!”.
Wani irin juyawa Idanun yaron yayi tare da wulƙitawa kana yaja dogon numfashi....!
*Zuwa yanzu dai mun gama ratsa tsakiyar labari babi-babi na zaren na dab da fara warware wa.*
By
*GARKUWAR MARUBUTA*
[30/07, 1:40 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: *LITTAFIN SAKAYYAH NA KUDINE KO KIN GANSHI A WASU WURAREN DA BA CIKIN GROUPS NA DANA BUƊE NA SAKAYYAH BAto na satane, 1k ne kacal kuɗin littafin SAKAYYAH yar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci da salama babu haƙƙin kowa a kanki 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276, kiyiwa Allah da Manzonsa ku dena fidda min littafina, in dai kin san kin sayane dan ki turawa wasu, dan Allah ki gaya min in mayar miki da kuɗinki🙏🏻🙏🏻Dan Allah nace ba dan niba*
Kai Ummi ta gyaɗa tare da cewa.
“Ameen”.
Cikin jin sanyi Asma'u tayi murmushi kana tace.
“Alhamdulillah wayar Yah Jameel ya shiga gaskiya munyi farin ciki”.
Malam Ahmad daya fito daga wanka ya fito coumpund ɗin fuskarsa ɗauke da murmushi kana yace.
“Alhamdulillah Asma'u maza kawo musu abinci suci tunda mun samu wayar Jameelu ya shiga maza kawo musu abinci”.
Moddibo kuwa kallon Malam Ahmad yayi kana yace.
“Nikam ma Malam baki ɗaya cikina ya cushe baki ɗaya farin ciki ya cika min cikana”.
Murmushi Ummi tayi kana tace.
“Nima cikina ya cika baki ɗaya farin ciki nake ji”.
Jinjina kai Malam Ahmad yayi tare da cewa.
“Dan Allah ku zauna kuci abinci wayarsa muka fara rasawa yanzu kuma wayarsa muka faru samu insha Allah shi ma zamu sameshi nan kusa ”.
Dai-dai lokacin Asma'u tazo ta ajiye musu abincin.
Tun ɓatan M Jameel sai yau Ummi da Moddibo sukaci abinci mai nauyi acikinsu duk da ba dayawa suka ciba.
Miƙewa Moddibo yayi kana yace.
“Ummi bari naje in faɗawa Innayi ta tayamu farin ciki”.
Kai Ummi ta gyaɗa tare da faɗin.
“Aikam dai gwara kaje”.
Ficewa yayi tare da tafiya Driving yake Cike da farin ciki har ya isa gida yana zuwa ya shiga sashen Innayi.
Innayi dake ki shimfiɗe ta miƙe kana tace.
“Alhamdulillah Moddibo naga kana cikin farin ciki da alama akwai labari mai daɗi?”.
Kai ya gyaɗa still Fuskarsa ɗauke da murmushi yace.
“Innayi wayar J ɗina ya shiga yau”.
Kai Innayi ta gyaɗa tare da cewa.
“Alhamdulillah gaskiya munyi farin ciki. Allah ya bayyanar mana dashi”.
Ameen ya amsa tare da wucewa sashen sa cike da farin ciki yana shiga ɗaki ya kira layin Malam Arɗo.
Malam Arɗo na dagawa yace.
“Malam Alhamdulillah yau wayar J ɗina yashiga a cigaba da taya mu da addu'a a masallacai da makarantu”.
Cike da farin ciki malam Arɗo yace.
“Masha Allah da izinin Ubangiji zai fito Insha Allah zamu cigaba da addu'a”.
Awannan daren haka Moddibo Ummi, Asma'u Bashir malam Ahmad da Innayi suka kwana cike da farin cikin shigar wayar M Jameel.
Yayin da Aɓangaren Abba ya kwana cikin taraddadi da tashin hankali koda ya farka tsakiyar dare kuka yayi ta yi yayin da Hajiya Karima ke kuka tana basa haƙuri kana tana cewa bada niyya tayi ba.
Aɓangaren gidan Lamiɗo ma haka Khausar da Mommy suka kwana azaune da Ramadan da kansa ke masifar ciwo da zaran an bashi maganin da Lamiɗo ya kawo yasha ciwon zai ɗan lafa jimawa kaɗan kuma zai sake tashi tsakiyar dare ya farka ya riƙa kuka dole Ummi ta kira Abba ya kawo masa magani cikin ikon Allah yana sha ciwon kan ya lafa.
Washe gari; Moddibo, Malam Arɗo, Ummi Innayi duk wani makusancin M Jameel na cikin farin ciki kana duk wanda ya kira wayarsa zai shiga sai dai ba aɗagawa Wunin wannan ranan haka Moddibo yayi yana kiran layin M Jameel still ba amsa.
Zuwa yamma jikin Moddibo ya fara sanyi da lamarin ganin yana kiran wayar M Jameel baya shiga lokaci ɗaya tsoro ya fara kamashi hankalinsa ya tashi Misalin ƙarfe goma na dare yana gidan Abba zaune sun kira Jameel kuma sama da sau ashirin kuma duk kiran yana shiga, sau dai ba'a ɗagawa, su kuma masatan basu kiraba.
Yayin da idanun Abba ke kumbure alamar har yanzu jinjinsa bai sauƙa sosai ba.
Cikin mutuwar jiki Moddibo ya koma gida kai tsaye sashen Innayi ya nufa bakinsa ɗauke da Sallama ya shiga.
Innayi dake zaune riƙe da carbi ta amsa masa cikin raunin Murya yace.
“Innayi”.
Kallonsa tayi cike da kulawa kana tace.
“Na'am”.
Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da fesar da numfashi kana cikin sanyin murya yace.
“ Innayi hankalina ya soma tashi wayar J yana shiga ba'a ɗauka sannan mutanen nan basu sake kira ba”.
Ajiyar zuciya Innayi ta sauƙe tare da cewa.
“Ba komai Moddibo Insha Allah ka kwantar da hankalin ka”.
Girgiza kai yayi kana yace.
“Anya kuwa Innayi?”.
Cikin bashi ƙwarin gwiwa tace.
“Ba komai Insha Allah ka cigaba dayi masa addu'a da izinin Ubangiji zai fito yanzu idan sun sake kira kuce musu an samu kuɗin Insha Allah Million biyar bazai gagara ba koda a masallatai anemi temako za'a samu su haɗu”.
Kai ya gyaɗa kana yace.
“Toh Innayi Allah yasa su kira ɗin dan yanzu kam ma cikon Million ukune”.
Cikin jin daɗi Innayi tace.
“Alhamdulillah Allah ya bamu sa'a”.
Amin yace
Sanna ya miƙe ya koma sashen sa cike da damuwa. Washe gari jin sauran kuɗin da ake buƙata, Lamido ya bawa Mommy da kanta ta kaiwa Ummi su sau dai sam basu kuma kiraba.
Haka dai rayuwa ta cigaba da tafiya yau kusan kwana ki shida kenan duk lokacin da aka kira wayar M Jameel zai shiga sai dai ba'a ɗauka.
Yayinda Ramadan kuwa ke kwana da azabebben ciwon kai idan aka bashi magani yasha ciwo ya lafa anjina kaɗan kuma ya sake dawowa.
Ga ɗaya Mommy da kwausar sun shiga damuwa, sun kai asibiti har cikin Taraba anyi hoton kan da duk wani gwaje-gwaje amman babu wani ciwo dake kansa, dan da farima likitocin sunyi zaton brain cancer ne.
baki ɗaya yaron ya fita hayyacinsa saboda tsananin ciwon kai.
Yau kimanin kwana shida kenan da aka fara samun wayar M Jameel na shiga.
Washe garin rana ta bakwai.
Da safe bayan an idar da Sallar Asbah Moddibo na fita a masallaci ya kira wayar M Jameel.
Cike da mmki tsoro ya janye wayar a kunnenshi sabida jin ance masa Switch off.
cikin mutuwar jiki ya nufi gidan Ummi yana shiga ya samu Ummi zaune akan Sallaya hannunta riƙe da Carbi.
Cike da ladabi ya gaisheta kana cikin sanyin murya yace.
“Ummi”.
Kallonsa tayi tare da cewa.
“Na'am Babana”.
Cikin raunin murya yace.
“Ummi na kira wayar J ɗina baya shiga”.
Ahankali Ummi ta jingina kanta da jikin kujeran falon kana tace.
“Nima na kira wayan Jameelu na baya shiga bansan Meyesa ba Allah yasa al'khairi ne”.
Cike da sanyi Middibo yace.
“Amin ya Allah in sha Allah ba komai Ummi”.
Cikin raunin murya Ummi ta lumshe Idanunta tare da cewa.
“Hmmm,Hmmm Ubangiji Allah yabamu ikon cinye jarrabawar da zai jarabce mu”.
Cikin sanyi Moddibo yace.
“Ameen”.
Miƙewa Moddibo yayi kana yace.
“Ummi bari naje gidan Abba naji koshi ya kira ya shiga”.
Kai Ummi ta gyaɗa Muryanta cike da rauni tace.
“Toh”.
Cikin sanyin jiki zuciya cike da karaya Moddibo ya nufi gidan Abba yana shiga coumpund ya ga Abba na ƙoƙarin shiga falo dawowansa daga masallaci kenan.
Ƙara sawa Moddibo yayi tare da miƙa masa hannu sukayi musabaha kana cikin sanyin murya Moddibo yace.
“Abba wayar J ɗina baya shiga”.
Ahankali Abba ya sunkuyar da kansa hawaye masu zafi suka shiga bin kuncinsa Shar-shar-shar kamar ƙaramin yaro baki ɗaya ya rame cikin raunin murya yace.
“Aliyu dama wayar Jameelu da kira yake shiga. Wani sanyi ne dama hankalina ya tashi tun jiya nake kiran wayar baya shiga, dama ni banyi farin ciki da shigan wayar Jameelu ba. Aliyu inaji Ajikina kamar akwai wani abu da bamu san menene ba jikina na bani ko ina Jameelu na yaje baya cikin walwala na rasa tudun dafawa”.
Cikin sauri Moddibo ya runtse Idanunsa zuciyarsa na bugawa da masifaffen ƙarfi kana cikin raunin murya yace.
“Abba insha Allah J yana cikin ƙoshin lafiya mu cigaba da masa addu'a amma nima baki ɗaya hankalina yayi masifar tashi”.
Cikin rauni da tsanananin tashin hankali suka ci-gaba da tattaunawa.
Acan gidan Lamiɗo kuwa Mommy, Khausar da Lamiɗo basu rintsaba a wannan daren.
A kan Ramadan suka kwana yanata kuka baiyi bacci ba.
Washe gari Bayan an idar da sallan Asbah Hajiya Bunayya ta shigo falon Mommy ahankali Ramadan dake kuka ya miƙa mata hannu kana cikin wata raunan'niyar murya mai cike da wahala yace.
“Ummah! Ummah! Kaina zai fashe kaina zai faɗi Wayyo Allah na Kaina! kaina”.
Baki daya jijiyoyin kansa sun tashi sunyi ruɗu ruɗu dasu yayinda idanunsa sukayi ja.
Cike da tausayawa Khausar ta ɗaura tafin hannunta na dama akan goshinsa Idanunta cike da ruwan hawaye kasa riƙe hawayen ta tayi jin yanda kan ke harbawa da masifar ƙarfi.
Kuka sosai Ramadan keyi kana cikin tsananin radaɗin ciwo ya riƙo hannun Mommy kana yace.
“Wayyo Mommy Kaina zai fashe. Mommy Kaina Wayyo zan mutu Mommy Zan mutufa”.
Wani irin miƙa Ramadan yayi tare da cewa.
“Momyyyyy zan mutuuuu”.
Cikin sauri Lamiɗo da yanzu ya shigo ya karɓesa ganin yanda idanun yaron suka juya da sauri ya fara ɗan bubbuga kumatunsa yana cewa.
“Ramadan! Ramadan!”.
Wani irin juyawa Idanun yaron yayi tare da wulƙitawa kana yaja dogon numfashi....!
*Zuwa yanzu dai mun gama ratsa tsakiyar labari babi-babi na zaren na dab da fara warware wa.*
By
*GARKUWAR MARUBUTA*
[30/07, 1:40 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: *LITTAFIN SAKAYYAH NA KUDINE KO KIN GANSHI A WASU WURAREN DA BA CIKIN GROUPS NA DANA BUƊE NA SAKAYYAH BAto na satane, 1k ne kacal kuɗin littafin SAKAYYAH yar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci da salama babu haƙƙin kowa a kanki 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276, kiyiwa Allah da Manzonsa ku dena fidda min littafina, in dai kin san kin sayane dan ki turawa wasu, dan Allah ki gaya min in mayar miki da kuɗinki🙏🏻🙏🏻Dan Allah nace ba dan niba*