Sashe 100
Sakayyah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin rauni da fusata Abba ya cigaba da cewa.
“Saboda bake kika haifi min Jameelu ba shine zaki salwantar da rayuwarsa, yanzu da ɗan da kika haifa a cikin kine zaki masa irin wannan abin? Karima kin cutar da rayuwata cuta mafi muni, muddin wani mummunan abu ya faru da Jameelu na bazan taɓa yafe miki ba”.
Cikin zubda hawaye Hajiya Karima tace.
“Haba Alhj wallahi ni ba haka nake nufi ba, kafahimceni tunda naga wancan karon ma da aka nemi ragin ai sun rage shiyasa nace barin ne mamaka sauƙi”.
Dai-dai lokacin Moddibo ya shigo falon idanunsa suka sauƙa akan Abba da jikinsa ke rawa idanunsa sunyi Jawur tamkar zai tsats-tsafo da hawayen jini yayin da numfashinsa ke seizing.
Cikin sauri Moddibo ya ƙara sa tare da riƙe Abba kana ya zaunar dashi akan kujera cikin sanyin murya yace.
“Abba mai ya faru?”.
Kasa cewa komai Abba yayi baki ɗaya baya cikin hayyacinsa numfashinsa sai kai koma yake cikin rauni da ficewar hayyaci yace.
“Karima kin cuceni Meyesa zaki min haka. Meyesa zaki ƙuntata min ta wannan hanyar!?”.
Cikin sauri Hajiya Turai ta shigo ganin halin da Abba ke ciki yasa kai tsaye ta wuce Bedroom ɗinsa tare da ɗauko masa magani kana ta kira Dr Muktar ya ɗagawa tace.
“Dan Allah Dr maza kazo jikin Alhj ya tashi gaba ɗaya ma numfashinsa sama yake yi”.
Da Ok Dr ya Amsa kana ta katse kiran tare da fitowa da magani ta ɓare tare da miƙa masa.
Cikin azabebben rawan da jikinsa keyi ya ture hannunta tare da cewa.
“Ba zan shaba Karima kin cuceni kin cutar da rayuwata, kin datse min farin cikina. Meyesa haka Karima duk abinda ya samu Jameelu Karima kece sanadi idan wani abu ya samu Jameelu Karima kece sanadi!”.
Ganin alamar baya cikin nutsuwarsa yasa Moddibo cewa.
“Dan Allah Abba ka kwantar da hankalin ka”.
Girgiza kai Abba keyi yana cewa.
“Karima kin cuceni kin cutar da rayuwata kin katse min farin cikina”.
Zama Moddibo yayi kana cikin sanyin murya ya shiga Furta.
_“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Hasbunallahu wani'imal wakil Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan minha La'ilaha Illah anta subhanaka Inni kuntu Minal Zhalimin la haula Wala ƙuwwata Illah billahil aliyul Azhim”_.
Ahankali Abbah yafara bin bakinsa yana karato adduo'in tun yani yi Aransa har yafara afili.
Hajiya Turai kuwa number Dr Muktar ta sake Kira yana ɗagawa tace.
“Dr kayi sauri dan Allah ina katsaya har yanzu baka zoba kuma na faɗa maka jikin Alhj ya tashi gashi mun basa magani yaƙi sha”.
Cikin sauri Dr Muktar yace.
“Gani nan na fito dama yanzu zan wuce asibiti amma yanzu na kusa gidanku ma ina ƙara so wa”.
Cike da damuwa tace.
“Toh shikenan sai kazo dan Allah kayi sauri”.
Ta ida maganar tare da katse kiran kana ta juya ta fice.
Moddibo kuwa ciki sanyi ya riƙe hannun Abba tare da cewa.
“Abba dan Allah kayi haƙuri ka cigaba da Addu'a”.
Kai Abba ya gyaɗa kana ya cigaba da maimaita adduo'in but still ɓarin da jikinsa keyi bai dai naba saima ƙaruwa da yake.
Dai-dai lokacin da Dr Muktar yayi hong mai gadi ya buɗe masa kana cikin sauri ya fito daga motar hannunsa riƙe da fest aid box Hajiya Turai dake Safa da marwa a coumpund ɗin ta masa jagora zuwa ɗakin suna shiga Dr Muktar ya zauna kan 1sitter kana ya buɗe Aidbox ɗin sa tare da gwada Bp Abba.
Cikin sauri ya kalli Abba tare da cewa.
“Subhanallah jinin Alhj ya hau sosai na faɗa muku ku daina kawo duk wani abu da kuka san zai ɓata masa rai, ko kuma tayar masa da hankali”.
Ya faɗa tare da ciro sirinji kana yace.
“Alhj bari nayi maka allura baki ɗaya damuwa yayi masa yawa”.
Ajiye sirinji Dr Muktar yayi kana ya balli magunguna ya miƙa masa tare da cewa.
“Alhj gashi kasha”.
Girgiza kai Abba yayi cike da rauni yace.
“A'a bazan shaba”.
Asanyaye Dr Muktar yace.
“Ayyah Alhj dan Allah kasha mana”.
Girgiza kai Abba yayi tare da cewa.
“A'a bazan shaba menene amfanin rayuwata matuƙar dai bazan iya temakon Jameelu na ba.
Meye riban cigaba da rayuwata matukar Jameelu na baya tare dani?”.
Cikin sauri Moddibo ya Girgiza kai tare da cewa.
“Subhanallah Abba kada kace haka kada zafin damuwa yasa mu kaucewa lissafin hankali da na Musulunci Abba kayi addu'a dan Allah ka karɓi maganin kasha Abba. shin yakakeso nayi idan har kaima ka faɗi ciwo ya kwantar da kai”.
Cikin tausayawa ya kalli Abba idanunsa cike da ruwan hawaye kana yace.
“Abba na tabbatar ko da J na nan bazai yi farin ciki da haka ba Abba dan Allah kayi haƙuri kasha maganinka, ganinka cikin dauriya shike bani ƙarfin gwiwa Abba bazan so ganin wani mugun abu yasa Meka ba. Idan har wani abu ya sameka Abba ya zanyi da rayuwata!?”.
Ya ida Maganar tare da miƙawa Abba maganin karɓa Abba yayi tare da kaiwa bakinsa ya haɗiye miƙewa Dr Muktar yayi kana yace.
“Alhj bari a maka Allura”.
Kai Abba ya gyaɗa kana Dr Muktar ya masa bayan ya masa ya juya ya fice.
Sannu Ahankali Abba ya fara maida numfashi kana ya jingina bayansa da jikin kujera ahankali numfashinsa ya fara dai-dai-ta Atake zufa ya shiga tsats-tsafo masa agabaki ɗaya ilahirin jikinsa.
Moddibo kuwa ganin haka yasa ya miƙe ahankali tare da ɗaukan remote ɗin AC ya kunna kana ya dawo ya zauna agefensa.
Matsawa kusa da Abba Hajiya Turai tayi kana ta ɗauki hankief ta shiga goge masa zufa,
cikin sanyin murya tace.
“Sannu Alhj Ubangiji ya sawwaƙa maka, ka kwantar da hankalin ka insha Allah babu abinda zai samu Jameelu sai al'khairi”.
Kallonta yayi amma baice komai ba.
Moddibo ma ahankali ya dawo kusa dashi ya zauna kana cikin sanyin murya yace.
“Abba ka kwantar da hankalin ka insha Allah babu abinda zai samu J Abba yanzu fa abinda ya kawoni da mukayi waya kace ansamu kudin kwata kwata Abba yanzu fa Million biyar ne ya rage akan kuɗin da muke nema ai abu yazo ƙarshe insha Allah babu abinda zai samu J,
Kuma ma kafin inzo nayi waya da Ummi tace akwai wasu gwala-gwalai guda biyu gobe zata kaisu Taraba, da akan yau zata kaisuma to dare yayi, ta kuma cemin in sha Allah zasu iya kai two million.
Kajifa alamomin nasara Abba meye zai tayar maka da hankali!?”.
Ahankali Abba ya ɗago jajayen Idanunsa tare da kallon Moddibo kana ya kalli Hajiya Turai sai kuma ya maida kallonsa kan Hajiya Karima dake tsaye cikin rauni ya nuna ta da yatsa kana yace.
“Karima ce nashiga wanka suka kira.
Karima ta ɗauka wai tana musu maganan ragin kuɗin nace ta nema min ragi ne?
Tabarni mana Jameelu ba ɗana bane ai zan fashi ɗana amma Meyesa Karima zata min haka!?”.
Moddibo kuwa cikin wani azabebben tsinkewar zuciya ya riƙe kansa tare da cewa.
“Innalilahi wa'inna ilahi rajiu'n.
kika nemi ragin kuɗi kuma Aunty Karima amma gaskiya baki kyauta mana ba”.
Cikin tsananin tsoro da fargabar abinda hakan zai haifar yaci gaba da cewa.
“Amma gaskiya baki kyauta manaba, ai wannan mugunta ne an saki ne ko kuma annemi wani temako awajenki fisabilillahi? wallahi kin cutar damu wannan shine cuta mafi muni da kika mana bayan kinji gargaɗin da sukayi”.
Ya ƙarashe mgnar cikin raunin murya yana jin zuciyarsa na wani irin zafi da karaya.
Cikin sauri Hajiya Turai ta kalli Hajiya Karima tare da Girgiza kai cike da takaicin halayyar ta tace.
“Idan har ba tayi haka ba ai bata cika Yadukko ba, ai dama baka sanin mai sonka da gaskiya sai kashiga wani hali, wasu kuma burinsu su samu hanyar da zasu musguna wa rayuwarka suke nema”.
Kallon Hajiya Turai Hajiya Karima tayi kana ta kalli Abba da Moddibo cikin Muryan kuka tace.
“Agaskiya ni anyi min bahaguwar fahimta nima Ina son Jameelu tamkar ɗa yake awajena fa, ke Hajiya Turai da kike wannan maganar nida ke waya fara zama da Jameelu ne?”.
Banza Hajiya Turai tayi da ita tana jin wani irin takaicin abinda ta aikata aranta.
Sannu Ahankali bacci ya fara fisgar Abba saboda magani da Alluran da aka masa nan take Bacci ya ɗauke sa kwanciya Moddibo ya gyara masa akan kujeran kana ya miƙe tare da ɗaukar key ɗin motarsa zuciyarsa cike da rauni damuwa da tashin hankali duk sun bayyana afuskarsa.
Yana fita yashiga motarsa tare da yimasa key yayin da hawaye suka cika kwarmin Idanunsa Driving yake yana sake try numbers din da suke kira kasancewar duk lokacin da suka kira saiya yi copy amma baki ɗaya Swich off.
Ahankali ya fito da Number M Jameel kana Yayi dearling cikin ikon Allah yaji wayar tashiga tana ringing lokaci ɗaya ya shiga cikin matsanancin farin ciki afili ya furta.
“Yau kuma wayar J tana shiga”.
Cikin sauri ya juya akalar motarsa zuwa gidan Ummi kana ya Parking awaje tare da buɗe gate ya shiga coumpund ɗin yana cewa.
“Ummi! Ummi!! Ummi!!!”.
Ummi dake tsaye Atsakiyar falo tayi saurin fitowa tare da cewa.
“Na'am Babana me yafaru?”.
Cike da walwala yace.
“Ummi wayar J ɗina yana shiga yau”.
Cike da farin ciki Ummi ta ware ido kana tace.
“Wayar Jameelu yana shiga?”.
Kai Moddibo ya gyaɗa still da murmushi afuskarsa ya gyaɗa mata kai kana yace.
“Wallahi yana shiga Ummi bari ma kiji”.
Ya faɗa tare da dearling number M Jameel aikuwa ya shiga ya fara ɗut-ɗut-dut cikin Sauri ya samata akunne da sauri Asma'u da Bashir dake Bedroom suka fito jiyo sautin su Ummi cikin farin ciki.
Murmushi Ummi tayi tare da cewa.
“Bari in Kira nima".
Ta ida maganar tare da dearling number kasancewar wayar na hannunta still ya shiga yana ringing.
Cikin sanyi ta juya ta kalli Moddibo tare da cewa.
“Babana to ya baya ɗauka kuma?”.
Cikin wani masifaffen tsinkewar zuciya da tsoro Moddibo ya kalleta cikin ƙoƙarin ɓoye tsoronsa yayi Murmushi tare da cewa.
“A'a Ummi Insha Allah tunda har wayarsa tana shiga zai ɗaga mu cigaba da kira da izinin Ubangiji zai ɗaga Agaskiya Ummi yau naji sanyi”.
Murmushi Ummi haram Asma'u, da Bashir.
“Saboda bake kika haifi min Jameelu ba shine zaki salwantar da rayuwarsa, yanzu da ɗan da kika haifa a cikin kine zaki masa irin wannan abin? Karima kin cutar da rayuwata cuta mafi muni, muddin wani mummunan abu ya faru da Jameelu na bazan taɓa yafe miki ba”.
Cikin zubda hawaye Hajiya Karima tace.
“Haba Alhj wallahi ni ba haka nake nufi ba, kafahimceni tunda naga wancan karon ma da aka nemi ragin ai sun rage shiyasa nace barin ne mamaka sauƙi”.
Dai-dai lokacin Moddibo ya shigo falon idanunsa suka sauƙa akan Abba da jikinsa ke rawa idanunsa sunyi Jawur tamkar zai tsats-tsafo da hawayen jini yayin da numfashinsa ke seizing.
Cikin sauri Moddibo ya ƙara sa tare da riƙe Abba kana ya zaunar dashi akan kujera cikin sanyin murya yace.
“Abba mai ya faru?”.
Kasa cewa komai Abba yayi baki ɗaya baya cikin hayyacinsa numfashinsa sai kai koma yake cikin rauni da ficewar hayyaci yace.
“Karima kin cuceni Meyesa zaki min haka. Meyesa zaki ƙuntata min ta wannan hanyar!?”.
Cikin sauri Hajiya Turai ta shigo ganin halin da Abba ke ciki yasa kai tsaye ta wuce Bedroom ɗinsa tare da ɗauko masa magani kana ta kira Dr Muktar ya ɗagawa tace.
“Dan Allah Dr maza kazo jikin Alhj ya tashi gaba ɗaya ma numfashinsa sama yake yi”.
Da Ok Dr ya Amsa kana ta katse kiran tare da fitowa da magani ta ɓare tare da miƙa masa.
Cikin azabebben rawan da jikinsa keyi ya ture hannunta tare da cewa.
“Ba zan shaba Karima kin cuceni kin cutar da rayuwata, kin datse min farin cikina. Meyesa haka Karima duk abinda ya samu Jameelu Karima kece sanadi idan wani abu ya samu Jameelu Karima kece sanadi!”.
Ganin alamar baya cikin nutsuwarsa yasa Moddibo cewa.
“Dan Allah Abba ka kwantar da hankalin ka”.
Girgiza kai Abba keyi yana cewa.
“Karima kin cuceni kin cutar da rayuwata kin katse min farin cikina”.
Zama Moddibo yayi kana cikin sanyin murya ya shiga Furta.
_“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Hasbunallahu wani'imal wakil Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan minha La'ilaha Illah anta subhanaka Inni kuntu Minal Zhalimin la haula Wala ƙuwwata Illah billahil aliyul Azhim”_.
Ahankali Abbah yafara bin bakinsa yana karato adduo'in tun yani yi Aransa har yafara afili.
Hajiya Turai kuwa number Dr Muktar ta sake Kira yana ɗagawa tace.
“Dr kayi sauri dan Allah ina katsaya har yanzu baka zoba kuma na faɗa maka jikin Alhj ya tashi gashi mun basa magani yaƙi sha”.
Cikin sauri Dr Muktar yace.
“Gani nan na fito dama yanzu zan wuce asibiti amma yanzu na kusa gidanku ma ina ƙara so wa”.
Cike da damuwa tace.
“Toh shikenan sai kazo dan Allah kayi sauri”.
Ta ida maganar tare da katse kiran kana ta juya ta fice.
Moddibo kuwa ciki sanyi ya riƙe hannun Abba tare da cewa.
“Abba dan Allah kayi haƙuri ka cigaba da Addu'a”.
Kai Abba ya gyaɗa kana ya cigaba da maimaita adduo'in but still ɓarin da jikinsa keyi bai dai naba saima ƙaruwa da yake.
Dai-dai lokacin da Dr Muktar yayi hong mai gadi ya buɗe masa kana cikin sauri ya fito daga motar hannunsa riƙe da fest aid box Hajiya Turai dake Safa da marwa a coumpund ɗin ta masa jagora zuwa ɗakin suna shiga Dr Muktar ya zauna kan 1sitter kana ya buɗe Aidbox ɗin sa tare da gwada Bp Abba.
Cikin sauri ya kalli Abba tare da cewa.
“Subhanallah jinin Alhj ya hau sosai na faɗa muku ku daina kawo duk wani abu da kuka san zai ɓata masa rai, ko kuma tayar masa da hankali”.
Ya faɗa tare da ciro sirinji kana yace.
“Alhj bari nayi maka allura baki ɗaya damuwa yayi masa yawa”.
Ajiye sirinji Dr Muktar yayi kana ya balli magunguna ya miƙa masa tare da cewa.
“Alhj gashi kasha”.
Girgiza kai Abba yayi cike da rauni yace.
“A'a bazan shaba”.
Asanyaye Dr Muktar yace.
“Ayyah Alhj dan Allah kasha mana”.
Girgiza kai Abba yayi tare da cewa.
“A'a bazan shaba menene amfanin rayuwata matuƙar dai bazan iya temakon Jameelu na ba.
Meye riban cigaba da rayuwata matukar Jameelu na baya tare dani?”.
Cikin sauri Moddibo ya Girgiza kai tare da cewa.
“Subhanallah Abba kada kace haka kada zafin damuwa yasa mu kaucewa lissafin hankali da na Musulunci Abba kayi addu'a dan Allah ka karɓi maganin kasha Abba. shin yakakeso nayi idan har kaima ka faɗi ciwo ya kwantar da kai”.
Cikin tausayawa ya kalli Abba idanunsa cike da ruwan hawaye kana yace.
“Abba na tabbatar ko da J na nan bazai yi farin ciki da haka ba Abba dan Allah kayi haƙuri kasha maganinka, ganinka cikin dauriya shike bani ƙarfin gwiwa Abba bazan so ganin wani mugun abu yasa Meka ba. Idan har wani abu ya sameka Abba ya zanyi da rayuwata!?”.
Ya ida Maganar tare da miƙawa Abba maganin karɓa Abba yayi tare da kaiwa bakinsa ya haɗiye miƙewa Dr Muktar yayi kana yace.
“Alhj bari a maka Allura”.
Kai Abba ya gyaɗa kana Dr Muktar ya masa bayan ya masa ya juya ya fice.
Sannu Ahankali Abba ya fara maida numfashi kana ya jingina bayansa da jikin kujera ahankali numfashinsa ya fara dai-dai-ta Atake zufa ya shiga tsats-tsafo masa agabaki ɗaya ilahirin jikinsa.
Moddibo kuwa ganin haka yasa ya miƙe ahankali tare da ɗaukan remote ɗin AC ya kunna kana ya dawo ya zauna agefensa.
Matsawa kusa da Abba Hajiya Turai tayi kana ta ɗauki hankief ta shiga goge masa zufa,
cikin sanyin murya tace.
“Sannu Alhj Ubangiji ya sawwaƙa maka, ka kwantar da hankalin ka insha Allah babu abinda zai samu Jameelu sai al'khairi”.
Kallonta yayi amma baice komai ba.
Moddibo ma ahankali ya dawo kusa dashi ya zauna kana cikin sanyin murya yace.
“Abba ka kwantar da hankalin ka insha Allah babu abinda zai samu J Abba yanzu fa abinda ya kawoni da mukayi waya kace ansamu kudin kwata kwata Abba yanzu fa Million biyar ne ya rage akan kuɗin da muke nema ai abu yazo ƙarshe insha Allah babu abinda zai samu J,
Kuma ma kafin inzo nayi waya da Ummi tace akwai wasu gwala-gwalai guda biyu gobe zata kaisu Taraba, da akan yau zata kaisuma to dare yayi, ta kuma cemin in sha Allah zasu iya kai two million.
Kajifa alamomin nasara Abba meye zai tayar maka da hankali!?”.
Ahankali Abba ya ɗago jajayen Idanunsa tare da kallon Moddibo kana ya kalli Hajiya Turai sai kuma ya maida kallonsa kan Hajiya Karima dake tsaye cikin rauni ya nuna ta da yatsa kana yace.
“Karima ce nashiga wanka suka kira.
Karima ta ɗauka wai tana musu maganan ragin kuɗin nace ta nema min ragi ne?
Tabarni mana Jameelu ba ɗana bane ai zan fashi ɗana amma Meyesa Karima zata min haka!?”.
Moddibo kuwa cikin wani azabebben tsinkewar zuciya ya riƙe kansa tare da cewa.
“Innalilahi wa'inna ilahi rajiu'n.
kika nemi ragin kuɗi kuma Aunty Karima amma gaskiya baki kyauta mana ba”.
Cikin tsananin tsoro da fargabar abinda hakan zai haifar yaci gaba da cewa.
“Amma gaskiya baki kyauta manaba, ai wannan mugunta ne an saki ne ko kuma annemi wani temako awajenki fisabilillahi? wallahi kin cutar damu wannan shine cuta mafi muni da kika mana bayan kinji gargaɗin da sukayi”.
Ya ƙarashe mgnar cikin raunin murya yana jin zuciyarsa na wani irin zafi da karaya.
Cikin sauri Hajiya Turai ta kalli Hajiya Karima tare da Girgiza kai cike da takaicin halayyar ta tace.
“Idan har ba tayi haka ba ai bata cika Yadukko ba, ai dama baka sanin mai sonka da gaskiya sai kashiga wani hali, wasu kuma burinsu su samu hanyar da zasu musguna wa rayuwarka suke nema”.
Kallon Hajiya Turai Hajiya Karima tayi kana ta kalli Abba da Moddibo cikin Muryan kuka tace.
“Agaskiya ni anyi min bahaguwar fahimta nima Ina son Jameelu tamkar ɗa yake awajena fa, ke Hajiya Turai da kike wannan maganar nida ke waya fara zama da Jameelu ne?”.
Banza Hajiya Turai tayi da ita tana jin wani irin takaicin abinda ta aikata aranta.
Sannu Ahankali bacci ya fara fisgar Abba saboda magani da Alluran da aka masa nan take Bacci ya ɗauke sa kwanciya Moddibo ya gyara masa akan kujeran kana ya miƙe tare da ɗaukar key ɗin motarsa zuciyarsa cike da rauni damuwa da tashin hankali duk sun bayyana afuskarsa.
Yana fita yashiga motarsa tare da yimasa key yayin da hawaye suka cika kwarmin Idanunsa Driving yake yana sake try numbers din da suke kira kasancewar duk lokacin da suka kira saiya yi copy amma baki ɗaya Swich off.
Ahankali ya fito da Number M Jameel kana Yayi dearling cikin ikon Allah yaji wayar tashiga tana ringing lokaci ɗaya ya shiga cikin matsanancin farin ciki afili ya furta.
“Yau kuma wayar J tana shiga”.
Cikin sauri ya juya akalar motarsa zuwa gidan Ummi kana ya Parking awaje tare da buɗe gate ya shiga coumpund ɗin yana cewa.
“Ummi! Ummi!! Ummi!!!”.
Ummi dake tsaye Atsakiyar falo tayi saurin fitowa tare da cewa.
“Na'am Babana me yafaru?”.
Cike da walwala yace.
“Ummi wayar J ɗina yana shiga yau”.
Cike da farin ciki Ummi ta ware ido kana tace.
“Wayar Jameelu yana shiga?”.
Kai Moddibo ya gyaɗa still da murmushi afuskarsa ya gyaɗa mata kai kana yace.
“Wallahi yana shiga Ummi bari ma kiji”.
Ya faɗa tare da dearling number M Jameel aikuwa ya shiga ya fara ɗut-ɗut-dut cikin Sauri ya samata akunne da sauri Asma'u da Bashir dake Bedroom suka fito jiyo sautin su Ummi cikin farin ciki.
Murmushi Ummi tayi tare da cewa.
“Bari in Kira nima".
Ta ida maganar tare da dearling number kasancewar wayar na hannunta still ya shiga yana ringing.
Cikin sanyi ta juya ta kalli Moddibo tare da cewa.
“Babana to ya baya ɗauka kuma?”.
Cikin wani masifaffen tsinkewar zuciya da tsoro Moddibo ya kalleta cikin ƙoƙarin ɓoye tsoronsa yayi Murmushi tare da cewa.
“A'a Ummi Insha Allah tunda har wayarsa tana shiga zai ɗaga mu cigaba da kira da izinin Ubangiji zai ɗaga Agaskiya Ummi yau naji sanyi”.
Murmushi Ummi haram Asma'u, da Bashir.