Sashe 20
Sakayyah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Murmushi Goggo Nanne tayi tace.
“Ki kwantar da hankalinki kada ki damu tashi kiyi alwala ga ruwan zafi abuta”.
Batace komai ba ta miƙe ta ɗauki butar ta zaga bayi sannan ta fito tayi alwala ɗakin Goggo Nanne suka shiga da Dije cikin ɗakin duhu.
Araunane Khausar tace.
“Daƙin duhu ni gani nake ma ko ina akwai kuliya”.
Dafa kafaɗar ta Dije tayi tace.
“ki kwantar da hankalinki nan babu kuliya”.
Ta ƙare mgnar tana kunna lantansu mai ɗan karen haske,
Kai kawai ta jinjina tare da sauƙe ajiyar zuciya ganin hasken, sannan ta tada sallah suka idar da Sallah maghariba Khausar kuwa jingina bayanta da jikin bango tayi ta fara addu'a.
Dije kuwa miƙewa tayi zata fita, Kallon ta Khausar tayi tace.
“Ina kuma zaki je?”.
Juyawa Dije tayi ta fuskance ta tace.
“Zanje in dafa mana ƙwoyin da kika ce kina so ne”.
“A'a kibari ba da fawa zamuyi ba soyawa zamuyi ina akwai attaruhu da albasa da kuma maggi?”.
Kai Dije ta gyaɗa tace.
“Eh akwai”.
“Ok to kibari sai munyi Azkhar”.
“Toh”,Dije tace.Sannan ta dawo ta zauna suka cigaba da yin Azkhar ɗin Khausar nayi da ƙarfi Dije na binta wani ta iya wani kuma bata iya ba sai Khausar ta tsaya ta gyara mata suna zaune har akira Isha'i suka Idar...
GEMBILA
Anutse Momy ta gama shirin baccinta bayan tayi addu'a sai kuma ta lumshe Idanunta ahankali ta sake buɗesu ta juya kwanciyar ta daga hagu zuwa dama sai kuma ta tashi ta zauna baki ɗaya kewan Khausar ɗin ta ke damunta acikin yini ɗaya da bata kusa da ita se taji kamar wata tayi ba tare da ita ba gashi basu da network bare ta kira taji muryanta.
Jin ƙaran Knowking ɗin ƙofa yasa Momy gyara zamanta kana ta bada izinin shiga,Anutse Haiydar ya shigo bakinsa ɗauke da Sallama kana ya zauna kusa da Momy.
Murmushi Mommy tayi tace.
“Haiydar lafiya ko kana bukatar wani abu?”.
Kai ya girgiza yace.
“Momy wallahi yau gidan nan ba daɗi da Addah Khausi bata nan”.
Murmushi Momy tayi cike da ƙaunar 'ya'yan nata da kuma yanda suke nunawa juna kulawa tace.
“Yau kuma?,Ko da yake dama haka kuke bakwa shiri sannan bakwa san rabuwa da juna”.
Fuska ya Marerece kafin yace.
“Allah yau gidan babu daɗi yau tunda gari Ya waye babu wanda yace min Haiydar kar kayi kaza, Haiydar zo in aikeka, Haiydar bakaji, Haiydar karenani, Haiydar kada fa kaci komai wurinsu Umma, Haiydar ban girme ka bane kam wai da in na saka abu bazakayi ba, Yau duk babu wanda ya faɗa min haka nayi missing ɗinta! Sosai wlh Momy Ina son Adda Khausi”.
Murmushi mai cike da shauƙi Momy tayi tare da zuba musu ido.
Raudat da shigowarta kenan ta Shagwaɓe fuska tace.
“Wallahi nima nayi kewarta Mommy yaukam tare zamu kwana ko?”.
Janyo hannunta Momy tayi tace.
“Autanah ba dole ba yau In kwana dake tunda Addah Khausar bata nan”.
Haiydar ne ya sake kallon Momy cikin yanayin kewar 'yar uwarsa yace.
“Momy dan Allah ki kira kice ta dawo munyi missing ɗin ta”.
Ramadan da Raudat suma sukayi saurin cewa.
“Please Momy ki kira”.
Kai Momy ta girgiza tace.
“Basu da network sai dai idan sunje wajen bishiyar ƙare magarka sun kira”.
Ramadan yace.
“Toh yanzu Mommy Gobe wa zai Miki shara?,da wanke-wanke da kuma gyaran falo?”.
Murmushi Momy tayi tana shafa kansa tace.
“Zanyi ƙoƙari nayi da kaina”.
Zare Ido Ramadan yayi yace.
“To wallahi Momy aɗauko Miki Addah Khausi yafi Miki gidan babu daɗi idan bata nan”.
Murmushi tayi tace.
“Toh”,Da haka hiran yazo ƙarshe Haiydar ya miƙe kana ya ɗauki Ramadan suka tafi ɗakinsu wanda zai ka fita falon Momy ƙofar nasu na jere da ƙofar falonta,
ita kuma Raudat gadon ta hau ta kwanta gefen Momyn.
Acan ɓangaren su Moddibo kuwa.
Zaune yake Atsarerren falonsa da yagaji da tsaruwa kana yana fitar da sihirtaccen ƙamshi mai masifar daɗin shaƙa.
Yayin da M Jameel ke kwance akan 3sitter da waya maƙale akunnensa, Anutse Moddibo ya juya ya zuba masa Idanunsa tare tsarasa da su, still wayan yake Amsawa ɗauke kansa yayi ya cigaba da operating system ɗin sa kana ahankali ya sake maida Kallonsa kan M Jameel still wayar ne maƙale akunnensa.
Cikin ga jiyawa da wayar da yake yi Moddibo ya zuba masa idanunsa tare da motsa laɓɓansa da suka sake yin pinch kana suka tattare saboda tsananin sanyi da akeyi yace.
“Wai kai da wa kake yin wayar?”.
Gyaɗa masa kai M Jameel yayi tare da juya hannunsa alamar ya kusa gamawa.
Ganin haka yasa Moddibo maida hankalinsa kan system ɗin sa yana cigaba da duba muhimman saƙonnin da suke shigo masa.
Wayarsa dake gefen Centre table ne yayi ƙara hannu yasa ya ɗaga nan yaga sunan Abba na yawo a screen ɗin wato Abban M Jameel.
Cikin han zari yayi picking call ɗin kana yace.
“Assalamu alaikum Abba Barka da dare”.
Daga ɓangaren Abba yace.
“Barka dai Moddibo ya gida ya kuma ɗalibai?”.
“Lafiya lau Alhamdulillah Abba”.
“Masha Allah kana tare da Hassan ɗinna ka ne?”.
Murmushi Moddibo yayi wanda ke sake fitar da ainihin kyawun fuskarsa yace.
“Eh Abba muna tare waya yake tun ɗazu nayi zaton ma da kai yake yin wayar”.
Abba yace.
“Aina kira wayarsa naji Line busy shiyasa nace bari na kira ka naga dare yayi bai dawo ba za'a rufe ƙofar gida”.
Murmushi Moddibo yayi yace.
“Ayyah Abba yau kam abarshi mu kwana tare gashi naga alamun Agajiye yake bacci ma yake ji”.
Kai Abba ya gyaɗa yace.
“Toh shikenan Moddibo ayi bacci lafiya Allah ya tashe mu lafiya amma gobe da safe kuzo ina son ganin ku”.
Kai Moddibo ya gyaɗa cike da mutuntaka yace.
“Toh insha Allah Abbah”.
Kana ya katse kiran.
kallon M Jameel yayi sai kuma ya ajiye System dake kan ƙafarsa ya miƙe ya isa inda M Jameel yake yasa hannu ya cire wayar daga kunnensa ya duba screen ɗin sai yaga number ba suna saidai aƙasan Number ansa Bahrain wato ƙasan Bahrain.
Kallon M Jameel yayi yace.
“Ooo kaida Jalaludeen ne dama?”.
Kai M Jameel ya gyaɗa yace.
“Eh shi ya hana ince da kai dashi nake waya”.
Murmushi M Jameel yayi yace.
“Yayi kyau”.
Jalaludeen abokinsa ne tare sukayi karatu a Jami'atul Madina asalin Balarabe Bahrain ne...
Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe yace.
“Abba ya kira yace baka koma ba har dare yayi sai nace zamu kwana tare yace gobe yana son ganinmu”.
Kai M Jameel ya gyaɗa da faɗin.
“Allah ya kaimu”.
“Ameen”.
Moddibo ya amsa tare da kallon M Jameel yace.
Bacci na keji zanje nayi wanka”.
Zare Ido M Jameel yayi yana kallon Moddibo yace.
“Wallahi inba cikin kashi na faɗa yanzu ba ba zanyi wanka ba yanda ake tsuga wannan sanyi agarin nan.
Kai Moddibo ya girgiza ba tare da yace komai ba ya wuce Bedroom.
wanka yayi da ruwa mai ɗumi, kana yayi shirin bacci.
Washe gari, da safe bayan sun dawo daga masallaci sashen Innayi suka nufa lokacin da suka shiga tana zaune kan darduma tana lazimi M Jameel ya zauna kusa da ita tare da riƙo tafin hannunta yace.
“Barka da safiya tsohuwa mai ran ƙarfe!”.
Murmushin fuskarta ta faɗaɗa tare da damƙe hannunsa dake cikin nata tace.
“Jameel Ubangiji Allah ya Albarkanci rayuwarku”.
Ya amsa da.
”Ameen Innayi”.
Shi kuwa Moddibo kusa da ita ya matsa ya ɗaura kansa akafaɗarta yana mai lumshe idanunsa ahankali yace.
“Barka da safiya Innayi”.
Hannunta tasa ta shafa fuskarsa tare da cewa.
“Fatan ka tashi lafiya ya ƙoƙari?”.
Ya amsa da. “Alhamdulillah” sai kuma ya miƙe tare da kallon M Jameel da still hannunsa ke cikin na Innayi yace.
“Mu je ko”.
Bai jira cewarsa ba ya fice daga sashen nata kana ya nufi nasa yana shiga kai tsaye Bedroom ya wuce ya cire naɗin Hiramin dake wuyan sa da kuma jallabiyar.
Kai ya shiga bathroom Masha Allah Komai na cikin toilet wanka ya fesa kana ya fito bakinsa ɗauke da addu'a
“Gufra naka”.Alokacin daya ziro ƙafarsa ta dama zuwa cikin Bedroom ɗin ya fito M Jameel kuwa jin ƙamshin sabulun wankan da kuma tularensa yasa ya ɗago kai sai kuma ya miƙe ya shiga toilet ɗin.
Shi kuwa Moddibo zama yayi agaban dressing mirrow ya shafa mayukan sa tare da taje yalwataccen sumarsa kana ya miƙe ya buɗe durowarsa
Masha Allah kayane aciki masu uban yawa fannin jallabiya da ban fannin yaduka da ban haka zalika fannin ƙananun kaya daban duk da cewa bai fiye amfani dasu ba yana tsaye awajen har M Jameel ya fito daga wanka bai ɗauki komai ba.
Murmushi m Jameel yayi tare da nufar jikin durowar yana cewa.
“Nasan koda zaka kwana nan ba zaka taɓa cire kayan da zamu sanya ba kai de inba jallabiya ba baka ganewa ko wani irin kaya”.
Moddibo kuwa murmushi yayi Aransa yana jinjinawa M Jameel yanda yake iya fahimtar komai nasa koda kuwa ƙwaƙa-ƙwaran motsi yayi yasan me yake nufi...
M Jameel kuwa Wani boyel Sky blue mai gidan dara-dara ya ciro musu tare da boxer da kuma singlet Fari ƙal.
Kallon Moddibo yayi tare da miƙa masa.
Murmushi Moddibo yayi tare da karɓa yana kallon kayan amma bai ce komai ba sai ya juya ya kimtsa.
Masha Allah wani irin kyau na musamman Moddibo yayi acikin kayan kalar shigar sai ta kasance tamkar kalar sararin samaniya ƙirjinsa na ƙiran jarumtaka ya bayyana acikin rigar kana yalwataccen sumar kansa ya kwanta luf yana sheƙi,Anutse ya juya wajen M Jameel dake miƙo masa takalmi da hula kalar sky blue Masha Allah m Jameel ma sosai Yayi kyau acikin kayan sai suka kasance tamkar tagwaye masu tsananin ƙaunar junansu.
Atare suka fice sashen Innayi suka nufa tun daga farfajiyar tsakar gidan Moddibo ya lumshe idanunsa yana jinjinawa tsaftar Kakar tasa har sanda suka isa ƙofanta inda sanyayyan ƙamshi turaren wuta ke tashi.
Ganinsu atare yasa ta sakar musu da murmushi atare suka shiga ɗakin suka zauna.
Ta dubesu cikin ƙaunarsu tace.
“Ubangiji Allah ya Albarkanci rayuwar ku Allah yasanya farin ciki acikin rayuwarku Ubangiji ya tsareku da dukkan sharrin mai sharri”.
“Ki kwantar da hankalinki kada ki damu tashi kiyi alwala ga ruwan zafi abuta”.
Batace komai ba ta miƙe ta ɗauki butar ta zaga bayi sannan ta fito tayi alwala ɗakin Goggo Nanne suka shiga da Dije cikin ɗakin duhu.
Araunane Khausar tace.
“Daƙin duhu ni gani nake ma ko ina akwai kuliya”.
Dafa kafaɗar ta Dije tayi tace.
“ki kwantar da hankalinki nan babu kuliya”.
Ta ƙare mgnar tana kunna lantansu mai ɗan karen haske,
Kai kawai ta jinjina tare da sauƙe ajiyar zuciya ganin hasken, sannan ta tada sallah suka idar da Sallah maghariba Khausar kuwa jingina bayanta da jikin bango tayi ta fara addu'a.
Dije kuwa miƙewa tayi zata fita, Kallon ta Khausar tayi tace.
“Ina kuma zaki je?”.
Juyawa Dije tayi ta fuskance ta tace.
“Zanje in dafa mana ƙwoyin da kika ce kina so ne”.
“A'a kibari ba da fawa zamuyi ba soyawa zamuyi ina akwai attaruhu da albasa da kuma maggi?”.
Kai Dije ta gyaɗa tace.
“Eh akwai”.
“Ok to kibari sai munyi Azkhar”.
“Toh”,Dije tace.Sannan ta dawo ta zauna suka cigaba da yin Azkhar ɗin Khausar nayi da ƙarfi Dije na binta wani ta iya wani kuma bata iya ba sai Khausar ta tsaya ta gyara mata suna zaune har akira Isha'i suka Idar...
GEMBILA
Anutse Momy ta gama shirin baccinta bayan tayi addu'a sai kuma ta lumshe Idanunta ahankali ta sake buɗesu ta juya kwanciyar ta daga hagu zuwa dama sai kuma ta tashi ta zauna baki ɗaya kewan Khausar ɗin ta ke damunta acikin yini ɗaya da bata kusa da ita se taji kamar wata tayi ba tare da ita ba gashi basu da network bare ta kira taji muryanta.
Jin ƙaran Knowking ɗin ƙofa yasa Momy gyara zamanta kana ta bada izinin shiga,Anutse Haiydar ya shigo bakinsa ɗauke da Sallama kana ya zauna kusa da Momy.
Murmushi Mommy tayi tace.
“Haiydar lafiya ko kana bukatar wani abu?”.
Kai ya girgiza yace.
“Momy wallahi yau gidan nan ba daɗi da Addah Khausi bata nan”.
Murmushi Momy tayi cike da ƙaunar 'ya'yan nata da kuma yanda suke nunawa juna kulawa tace.
“Yau kuma?,Ko da yake dama haka kuke bakwa shiri sannan bakwa san rabuwa da juna”.
Fuska ya Marerece kafin yace.
“Allah yau gidan babu daɗi yau tunda gari Ya waye babu wanda yace min Haiydar kar kayi kaza, Haiydar zo in aikeka, Haiydar bakaji, Haiydar karenani, Haiydar kada fa kaci komai wurinsu Umma, Haiydar ban girme ka bane kam wai da in na saka abu bazakayi ba, Yau duk babu wanda ya faɗa min haka nayi missing ɗinta! Sosai wlh Momy Ina son Adda Khausi”.
Murmushi mai cike da shauƙi Momy tayi tare da zuba musu ido.
Raudat da shigowarta kenan ta Shagwaɓe fuska tace.
“Wallahi nima nayi kewarta Mommy yaukam tare zamu kwana ko?”.
Janyo hannunta Momy tayi tace.
“Autanah ba dole ba yau In kwana dake tunda Addah Khausar bata nan”.
Haiydar ne ya sake kallon Momy cikin yanayin kewar 'yar uwarsa yace.
“Momy dan Allah ki kira kice ta dawo munyi missing ɗin ta”.
Ramadan da Raudat suma sukayi saurin cewa.
“Please Momy ki kira”.
Kai Momy ta girgiza tace.
“Basu da network sai dai idan sunje wajen bishiyar ƙare magarka sun kira”.
Ramadan yace.
“Toh yanzu Mommy Gobe wa zai Miki shara?,da wanke-wanke da kuma gyaran falo?”.
Murmushi Momy tayi tana shafa kansa tace.
“Zanyi ƙoƙari nayi da kaina”.
Zare Ido Ramadan yayi yace.
“To wallahi Momy aɗauko Miki Addah Khausi yafi Miki gidan babu daɗi idan bata nan”.
Murmushi tayi tace.
“Toh”,Da haka hiran yazo ƙarshe Haiydar ya miƙe kana ya ɗauki Ramadan suka tafi ɗakinsu wanda zai ka fita falon Momy ƙofar nasu na jere da ƙofar falonta,
ita kuma Raudat gadon ta hau ta kwanta gefen Momyn.
Acan ɓangaren su Moddibo kuwa.
Zaune yake Atsarerren falonsa da yagaji da tsaruwa kana yana fitar da sihirtaccen ƙamshi mai masifar daɗin shaƙa.
Yayin da M Jameel ke kwance akan 3sitter da waya maƙale akunnensa, Anutse Moddibo ya juya ya zuba masa Idanunsa tare tsarasa da su, still wayan yake Amsawa ɗauke kansa yayi ya cigaba da operating system ɗin sa kana ahankali ya sake maida Kallonsa kan M Jameel still wayar ne maƙale akunnensa.
Cikin ga jiyawa da wayar da yake yi Moddibo ya zuba masa idanunsa tare da motsa laɓɓansa da suka sake yin pinch kana suka tattare saboda tsananin sanyi da akeyi yace.
“Wai kai da wa kake yin wayar?”.
Gyaɗa masa kai M Jameel yayi tare da juya hannunsa alamar ya kusa gamawa.
Ganin haka yasa Moddibo maida hankalinsa kan system ɗin sa yana cigaba da duba muhimman saƙonnin da suke shigo masa.
Wayarsa dake gefen Centre table ne yayi ƙara hannu yasa ya ɗaga nan yaga sunan Abba na yawo a screen ɗin wato Abban M Jameel.
Cikin han zari yayi picking call ɗin kana yace.
“Assalamu alaikum Abba Barka da dare”.
Daga ɓangaren Abba yace.
“Barka dai Moddibo ya gida ya kuma ɗalibai?”.
“Lafiya lau Alhamdulillah Abba”.
“Masha Allah kana tare da Hassan ɗinna ka ne?”.
Murmushi Moddibo yayi wanda ke sake fitar da ainihin kyawun fuskarsa yace.
“Eh Abba muna tare waya yake tun ɗazu nayi zaton ma da kai yake yin wayar”.
Abba yace.
“Aina kira wayarsa naji Line busy shiyasa nace bari na kira ka naga dare yayi bai dawo ba za'a rufe ƙofar gida”.
Murmushi Moddibo yayi yace.
“Ayyah Abba yau kam abarshi mu kwana tare gashi naga alamun Agajiye yake bacci ma yake ji”.
Kai Abba ya gyaɗa yace.
“Toh shikenan Moddibo ayi bacci lafiya Allah ya tashe mu lafiya amma gobe da safe kuzo ina son ganin ku”.
Kai Moddibo ya gyaɗa cike da mutuntaka yace.
“Toh insha Allah Abbah”.
Kana ya katse kiran.
kallon M Jameel yayi sai kuma ya ajiye System dake kan ƙafarsa ya miƙe ya isa inda M Jameel yake yasa hannu ya cire wayar daga kunnensa ya duba screen ɗin sai yaga number ba suna saidai aƙasan Number ansa Bahrain wato ƙasan Bahrain.
Kallon M Jameel yayi yace.
“Ooo kaida Jalaludeen ne dama?”.
Kai M Jameel ya gyaɗa yace.
“Eh shi ya hana ince da kai dashi nake waya”.
Murmushi M Jameel yayi yace.
“Yayi kyau”.
Jalaludeen abokinsa ne tare sukayi karatu a Jami'atul Madina asalin Balarabe Bahrain ne...
Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe yace.
“Abba ya kira yace baka koma ba har dare yayi sai nace zamu kwana tare yace gobe yana son ganinmu”.
Kai M Jameel ya gyaɗa da faɗin.
“Allah ya kaimu”.
“Ameen”.
Moddibo ya amsa tare da kallon M Jameel yace.
Bacci na keji zanje nayi wanka”.
Zare Ido M Jameel yayi yana kallon Moddibo yace.
“Wallahi inba cikin kashi na faɗa yanzu ba ba zanyi wanka ba yanda ake tsuga wannan sanyi agarin nan.
Kai Moddibo ya girgiza ba tare da yace komai ba ya wuce Bedroom.
wanka yayi da ruwa mai ɗumi, kana yayi shirin bacci.
Washe gari, da safe bayan sun dawo daga masallaci sashen Innayi suka nufa lokacin da suka shiga tana zaune kan darduma tana lazimi M Jameel ya zauna kusa da ita tare da riƙo tafin hannunta yace.
“Barka da safiya tsohuwa mai ran ƙarfe!”.
Murmushin fuskarta ta faɗaɗa tare da damƙe hannunsa dake cikin nata tace.
“Jameel Ubangiji Allah ya Albarkanci rayuwarku”.
Ya amsa da.
”Ameen Innayi”.
Shi kuwa Moddibo kusa da ita ya matsa ya ɗaura kansa akafaɗarta yana mai lumshe idanunsa ahankali yace.
“Barka da safiya Innayi”.
Hannunta tasa ta shafa fuskarsa tare da cewa.
“Fatan ka tashi lafiya ya ƙoƙari?”.
Ya amsa da. “Alhamdulillah” sai kuma ya miƙe tare da kallon M Jameel da still hannunsa ke cikin na Innayi yace.
“Mu je ko”.
Bai jira cewarsa ba ya fice daga sashen nata kana ya nufi nasa yana shiga kai tsaye Bedroom ya wuce ya cire naɗin Hiramin dake wuyan sa da kuma jallabiyar.
Kai ya shiga bathroom Masha Allah Komai na cikin toilet wanka ya fesa kana ya fito bakinsa ɗauke da addu'a
“Gufra naka”.Alokacin daya ziro ƙafarsa ta dama zuwa cikin Bedroom ɗin ya fito M Jameel kuwa jin ƙamshin sabulun wankan da kuma tularensa yasa ya ɗago kai sai kuma ya miƙe ya shiga toilet ɗin.
Shi kuwa Moddibo zama yayi agaban dressing mirrow ya shafa mayukan sa tare da taje yalwataccen sumarsa kana ya miƙe ya buɗe durowarsa
Masha Allah kayane aciki masu uban yawa fannin jallabiya da ban fannin yaduka da ban haka zalika fannin ƙananun kaya daban duk da cewa bai fiye amfani dasu ba yana tsaye awajen har M Jameel ya fito daga wanka bai ɗauki komai ba.
Murmushi m Jameel yayi tare da nufar jikin durowar yana cewa.
“Nasan koda zaka kwana nan ba zaka taɓa cire kayan da zamu sanya ba kai de inba jallabiya ba baka ganewa ko wani irin kaya”.
Moddibo kuwa murmushi yayi Aransa yana jinjinawa M Jameel yanda yake iya fahimtar komai nasa koda kuwa ƙwaƙa-ƙwaran motsi yayi yasan me yake nufi...
M Jameel kuwa Wani boyel Sky blue mai gidan dara-dara ya ciro musu tare da boxer da kuma singlet Fari ƙal.
Kallon Moddibo yayi tare da miƙa masa.
Murmushi Moddibo yayi tare da karɓa yana kallon kayan amma bai ce komai ba sai ya juya ya kimtsa.
Masha Allah wani irin kyau na musamman Moddibo yayi acikin kayan kalar shigar sai ta kasance tamkar kalar sararin samaniya ƙirjinsa na ƙiran jarumtaka ya bayyana acikin rigar kana yalwataccen sumar kansa ya kwanta luf yana sheƙi,Anutse ya juya wajen M Jameel dake miƙo masa takalmi da hula kalar sky blue Masha Allah m Jameel ma sosai Yayi kyau acikin kayan sai suka kasance tamkar tagwaye masu tsananin ƙaunar junansu.
Atare suka fice sashen Innayi suka nufa tun daga farfajiyar tsakar gidan Moddibo ya lumshe idanunsa yana jinjinawa tsaftar Kakar tasa har sanda suka isa ƙofanta inda sanyayyan ƙamshi turaren wuta ke tashi.
Ganinsu atare yasa ta sakar musu da murmushi atare suka shiga ɗakin suka zauna.
Ta dubesu cikin ƙaunarsu tace.
“Ubangiji Allah ya Albarkanci rayuwar ku Allah yasanya farin ciki acikin rayuwarku Ubangiji ya tsareku da dukkan sharrin mai sharri”.