Sashe 111
Sakayyah Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Suna isa dajin bayan sunyi Parking din Motar daga can nesa, suka fara haurawa saman dutsen.
Da sauri suka fara kallon juna sabida jin wani irin ni'imtaccen ƙamshi mai sanyin shaƙa, babu wari kamar yanda ya faɗa musu yasa Moddibo juyawa ya kalli Ori kana cikin sanyi yace.
“Ya gaba ɗaya babu warin da kace sai ma wani irin amintaccen ƙamshi”.
Kallonsa Ori yayi da faɗin.
“Toh yaufa kusan kwana takwas kenan da labarin dana baku ai dole wari ya baje dan zuwa yanzu Nasan gawar ya fashe bare kuma ruwan sama da ake ai dole zai za gonye sai dai kuma nima nayi mamakin wannan ƙamshi!”.
Cikin sanyi Malam Arɗo yace.
“Allah mai iko wannan wani irin ni'imtaccen ƙamshi ne a tsakiyar daji”.
Abba kuwa kasa furta komai yayi sai zuciyarsa dake bugawa da masifar ƙarfi yana jin wani irin masifaffen tsinkewar zuciya haka zalika Moddibo suna masu shaƙar ƙamshi.
Lamiɗo da polices din kuma sai lumshe idanu suke sabida daɗin ƙamshin da Ubangijin talikai ya wadata wurin dashi.
Yayinda suna kara haurawa suna ƙara jin ƙamshin.
Cikin tsanananin fargaba da tsinkewar zuciya suka cigaba da haurawa wajen suna gama haurawa Ori yayi saurin cewa.
“Yawwa ga can bishiyar”.
Da sauri Moddibo ya ɗaga Idanunsa tare da kallon jikin Bishiyar ganin gawa ɗaure ajikin Bishiya yayi har ya zagwanye idanunsa sun rarake sai ramuka kaɗai sai kuma maiƙo dake zube aƙasa da wani irin sassayan ƙamshin dake tashi a wurin.
Cikin tsanananin tsinkewar zuciya ya sauƙe idanunsa akasa dai-dai kan ƙafar gawar dake maƙale da takalmin cikin sauri ya runtse Idanunsa tare da dafe ƙahon zuciyarsa dake bugawa da masifar ƙarfi.
Abba kuwa da sauri ya ƙarasa jikin Bishiyar dai-dai Inda goran faron ke ajiye Idanunsa suka sauƙa akan wayoyin dake wajen hannunsa na rawa ya ɗago wayar tare da jujjuyawa.
Cikin tsanananin tashin hankali da ruɗu yace.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n!”.
Juyawa yayi tare da kallon Moddibo cikin raunin murya yace.
“Aliyu wayoyin Jameelu na neeeee”.
Cikin sauri Moddibo ya juya tare da dafe saitin ƙohon zuciyarsa cikin raunin murya mai cike da tsantsar tashin hankali yace.
“Abba wayar J kuma”.
Kai Abba ya gyaɗa yayin da wasu irin hawaye masu masifar zafi ke koro juna subabin kuncinsa murya na rawa yace.
“Eh”, Ahankali Moddibo ya juya ta gefen da gawar ke daure tare da tsaida idanunsa akan hannun gawar na dama da har ya bushe idanunsa ya zubawa zoben dake hannu gawar.
Cikin tsanananin kaɗuwa da wani masifaffen tsinkewar zuciya mai cike da ɗimuwa da tashin hankali Moddibo yace.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Abba kalli zobunnan hannunsa zobunnan hannun J ɗina ne da agogon”.
Ya ida maganar tare da yanke jiki ya faɗi babu numfashi atare dashi....!
Wannan littafin dai na kuɗi ne.
By
*GARKUWAR MARUBUTA*
[30/07, 1:42 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: Spndeɗɗ. Baya Moddibo ya koma. Suuuuuu ya faɗi a sume, cikin sauri Lamiɗo ya tarosa, ya faɗa jikinsa cike da tashin hankali Lamiɗo yace.
“Innalillahi ya suma fa Subhanallah!”.
Cikin sauri Malam Arɗo ya ƙara sa kusa da Lamiɗo idanunsa akan Moddibo ya shiga kiran sunan sa yana faɗin.
“Moddibo!, Moddibo!!, Moddibo!!!”.
Ina tuni Moddibo ya sume babu alamar numfashi atare dashi.
Abba kuwa kansa ya ɗaga tare da kallon fuskar skeleton M Jameel kana ya maida Idanunsa ƙasa kan takalmin dake sanye aƙafarsa ahankali ya leƙa bayan idanunsa suka sauƙa akan guntun rigarsa da bai gama sauƙa daga jikin skeleton ba jinjina kansa yayi cikin wata dakakkiyar murya ya juya ya kalli Moddibo dake sume kai ya girgiza tare da sakin murmushin da yafi kuka ciwo murmushi da yafi ihu zafi, murmushin da yafi ciwo, Ciwo murmushin da yafi raɗaɗi zafi, ya saki kana ya juya ya kalli sauran mutanen dake tsaye sai ya kuma kalli fuskar skeleton tare da maida kallonsa kan yatsun hannunsa.
Cikin wata dakakkiyar murya me ɗauke da tarin raɗaɗi da ƙuna yace.
“Uhmmm Jameelu na ne”.
Kallonsa ya mayar kan Moddibo da har zuwa lokacin yake. Rungume a jikin Lamiɗo taune lips ɗinsa yayi tare da cewa.
“Kai kam Aliyu kahuta, inama ace nima zan sume ko kuma in mace ma gaba ɗaya da hakan yafi min sauƙi”.
Cikin sauri ɗaya police ɗin ya juya tare da isa gefen Abba ya riƙe sa cike da alhini da tarin tausayawa yace.
“Alhj Bashir kayi addu'a kaji”.
Kai Abba ya gyaɗa cikin wata dakakkiyar murya yace.
_“Innalillahi wa'inna Ilahi rajiu'n lahaula wala ƙuwwata Illah billahil aliyul Azhim Hasbunallahu wani'imal wakil Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan minha La'ilaha Illah anta subhanaka Inni kuntu Minal Zhalimin”_ sune Adduo'in da yake iya maimaitawa afili da kuma ransa.
Ori dake tsaye ciki ruɗu da tausayawa yayi saurin ƙarasawa gaban skeleton gawar M Jameel ya ɗauko goran ruwan kana ya dawo tare da miƙawa Lamiɗo yana mai cewa.
“Lamiɗo gashi ayayyafa masa”.
Karɓa Lamiɗo yayi kana ya buɗe tare da yayyafawa Moddibo dake kwance jikinsa amma ko kaɗan Moddibo bai motsa ba.
Kallon Buba Lamiɗo yayi kana yace.
“Ori taimaka min mu saka shi cikin Mota”.
Kai Buba ya gyaɗa.
Ɗaya daga cikin Folisawan ne yace.
“Ranka shi daɗe bari mu saka shi”.
Ya faɗa tare da kallon ɗan gidansa da Ido ya masa alamar yazo su kama Moddibo ƙarasawa yayi sannan suka ɗauki Moddibo suka sauƙa kasan dutsen, tare da sanya shi abayan Motar Malam Arɗo.
Folisawan kuwa ƙara sawa sukayi suka shiga ɗaukar hoton gawar skeleton M Jameel.
Bayan sun gama ɗauka tare yan dube-dubensu, da Babbansu da sauran suka saka handglove suka ƙarasa gaban gawar da niyyar sunjanye gawar Babbansun najan Igiyar da aka ɗauɗaureshi ƙasusuwan suka kakkarye tare da zubewa a ƙasa babu ta yanda zasu iya daukarsa Babban su ya umarci Coustable yaje ya ɗauko musu kwali abayan mota kana suka tattara gawar suka zuba acikin kwalin kana suka kwashe takalmansa da wayoyinsa suka saka awata leda.
Abba kuwa cikin wani irin yanayi ya nufi cikin jejin yana tafiya ba tare da shi kansa yasan inda ya nufaba.
Cikin sauri Lamiɗo ya nufesa tare da riƙe hannunsa cike da tausayawa yace.
“Alhj banan zamu bi ba can baya ne, hanyar kazo innu na maka hanyar da zamu bi”.
Kai Abba ya gyaɗa tare da bin bayan Lamiɗo baki ɗaya baya cikin nutsuwarsa ya kasa gane shin mafarki yake ko kuma azahirance komai ke faruwa.
Bayan sun isa Lamiɗo da kansa ya buɗe masa mota yashiga sannan shima yashiga.
Folisawan kuwa kwalin da gawar M Jameel ke ciki suka ɗauka tare da sawa abayan motarsu suka tafi gida.
Abba kuwa kallon hanya kawai yake baki ɗaya baya cikin hayyacinsa ganin yanayin da yake ciki ne yasa Malam Arɗo ya fara yi masa Adduo'i yana tofa masa kana yana faɗa afili.
Ahankali Abba ya fara sakin Ajiyar zuciya kana yashiga maimaita Adduo'in sannu Ahankali ya fara jin hankalinsa ya fara dawowa jikinsa.
Motar da Moddibo ke ciki Ori da police ɗaya ne aciki direct Asibiti suka nufa dashi.
Yayin da Motar dasu Abba da kuma gawar M Jameel ke ciki kai tsaye gida suka wuce, suna isa kai tsaye falonsa suka wuce police ɗin ne ya ɗauko kwalin Gawar M Jameel ya shigo dashi kana ya ajiye agabansu.
Hajiya Turai dake sashenta tana jin tsayuwar motoci ta fito zuwa falon Abba.
Ganin Abba zaune tare dasu Lamiɗo yasa ta nufi gefen Abba cikin yanayin damuwa tace.
“Alhj lafiya ya ake ciki Gawar waye kuka samu?”.
Ahankali ya ɗago Idanunsa da suka kaɗa sukayi jawur ya kalleta kana yayi ƙasa da kansa cikin raunin murya yace.
“Gawar Jameelu na ne!”.
Arazane Hajiya Turai ta kallesa zuciyarta na bugawa da masifar ƙarfi Idanunta akansa tace.
“Gawar Jameelu kuma!?”.
Kai ya gyaɗa mata Cikin tsananin tashin hankali da ruɗu ta fashe da kuka me tsuma zuciya tana furta.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n ina gawar yake?”.
Da hannu ya nuna mata kwalin dake gabansa.
Da kallo tabi kwalin cikin sauri ta sake Kallonsa Idanunta cike da ruwan hawaye tace.
“Gawar Jameelu ne acikin kwali haka?”.
Kai ya gyaɗa batare daya ɗago kaiba yace.
“Shine”.
Wani sabon kuka ta fashe dashi tana Girgiza kai Kukanta ne ya fito da Hajiya Karima itama ganin abinda ke faruwa yasa ta fashe da kuka.
Da sauri suka fara kallon juna sabida jin wani irin ni'imtaccen ƙamshi mai sanyin shaƙa, babu wari kamar yanda ya faɗa musu yasa Moddibo juyawa ya kalli Ori kana cikin sanyi yace.
“Ya gaba ɗaya babu warin da kace sai ma wani irin amintaccen ƙamshi”.
Kallonsa Ori yayi da faɗin.
“Toh yaufa kusan kwana takwas kenan da labarin dana baku ai dole wari ya baje dan zuwa yanzu Nasan gawar ya fashe bare kuma ruwan sama da ake ai dole zai za gonye sai dai kuma nima nayi mamakin wannan ƙamshi!”.
Cikin sanyi Malam Arɗo yace.
“Allah mai iko wannan wani irin ni'imtaccen ƙamshi ne a tsakiyar daji”.
Abba kuwa kasa furta komai yayi sai zuciyarsa dake bugawa da masifar ƙarfi yana jin wani irin masifaffen tsinkewar zuciya haka zalika Moddibo suna masu shaƙar ƙamshi.
Lamiɗo da polices din kuma sai lumshe idanu suke sabida daɗin ƙamshin da Ubangijin talikai ya wadata wurin dashi.
Yayinda suna kara haurawa suna ƙara jin ƙamshin.
Cikin tsanananin fargaba da tsinkewar zuciya suka cigaba da haurawa wajen suna gama haurawa Ori yayi saurin cewa.
“Yawwa ga can bishiyar”.
Da sauri Moddibo ya ɗaga Idanunsa tare da kallon jikin Bishiyar ganin gawa ɗaure ajikin Bishiya yayi har ya zagwanye idanunsa sun rarake sai ramuka kaɗai sai kuma maiƙo dake zube aƙasa da wani irin sassayan ƙamshin dake tashi a wurin.
Cikin tsanananin tsinkewar zuciya ya sauƙe idanunsa akasa dai-dai kan ƙafar gawar dake maƙale da takalmin cikin sauri ya runtse Idanunsa tare da dafe ƙahon zuciyarsa dake bugawa da masifar ƙarfi.
Abba kuwa da sauri ya ƙarasa jikin Bishiyar dai-dai Inda goran faron ke ajiye Idanunsa suka sauƙa akan wayoyin dake wajen hannunsa na rawa ya ɗago wayar tare da jujjuyawa.
Cikin tsanananin tashin hankali da ruɗu yace.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n!”.
Juyawa yayi tare da kallon Moddibo cikin raunin murya yace.
“Aliyu wayoyin Jameelu na neeeee”.
Cikin sauri Moddibo ya juya tare da dafe saitin ƙohon zuciyarsa cikin raunin murya mai cike da tsantsar tashin hankali yace.
“Abba wayar J kuma”.
Kai Abba ya gyaɗa yayin da wasu irin hawaye masu masifar zafi ke koro juna subabin kuncinsa murya na rawa yace.
“Eh”, Ahankali Moddibo ya juya ta gefen da gawar ke daure tare da tsaida idanunsa akan hannun gawar na dama da har ya bushe idanunsa ya zubawa zoben dake hannu gawar.
Cikin tsanananin kaɗuwa da wani masifaffen tsinkewar zuciya mai cike da ɗimuwa da tashin hankali Moddibo yace.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Abba kalli zobunnan hannunsa zobunnan hannun J ɗina ne da agogon”.
Ya ida maganar tare da yanke jiki ya faɗi babu numfashi atare dashi....!
Wannan littafin dai na kuɗi ne.
By
*GARKUWAR MARUBUTA*
[30/07, 1:42 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: Spndeɗɗ. Baya Moddibo ya koma. Suuuuuu ya faɗi a sume, cikin sauri Lamiɗo ya tarosa, ya faɗa jikinsa cike da tashin hankali Lamiɗo yace.
“Innalillahi ya suma fa Subhanallah!”.
Cikin sauri Malam Arɗo ya ƙara sa kusa da Lamiɗo idanunsa akan Moddibo ya shiga kiran sunan sa yana faɗin.
“Moddibo!, Moddibo!!, Moddibo!!!”.
Ina tuni Moddibo ya sume babu alamar numfashi atare dashi.
Abba kuwa kansa ya ɗaga tare da kallon fuskar skeleton M Jameel kana ya maida Idanunsa ƙasa kan takalmin dake sanye aƙafarsa ahankali ya leƙa bayan idanunsa suka sauƙa akan guntun rigarsa da bai gama sauƙa daga jikin skeleton ba jinjina kansa yayi cikin wata dakakkiyar murya ya juya ya kalli Moddibo dake sume kai ya girgiza tare da sakin murmushin da yafi kuka ciwo murmushi da yafi ihu zafi, murmushin da yafi ciwo, Ciwo murmushin da yafi raɗaɗi zafi, ya saki kana ya juya ya kalli sauran mutanen dake tsaye sai ya kuma kalli fuskar skeleton tare da maida kallonsa kan yatsun hannunsa.
Cikin wata dakakkiyar murya me ɗauke da tarin raɗaɗi da ƙuna yace.
“Uhmmm Jameelu na ne”.
Kallonsa ya mayar kan Moddibo da har zuwa lokacin yake. Rungume a jikin Lamiɗo taune lips ɗinsa yayi tare da cewa.
“Kai kam Aliyu kahuta, inama ace nima zan sume ko kuma in mace ma gaba ɗaya da hakan yafi min sauƙi”.
Cikin sauri ɗaya police ɗin ya juya tare da isa gefen Abba ya riƙe sa cike da alhini da tarin tausayawa yace.
“Alhj Bashir kayi addu'a kaji”.
Kai Abba ya gyaɗa cikin wata dakakkiyar murya yace.
_“Innalillahi wa'inna Ilahi rajiu'n lahaula wala ƙuwwata Illah billahil aliyul Azhim Hasbunallahu wani'imal wakil Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan minha La'ilaha Illah anta subhanaka Inni kuntu Minal Zhalimin”_ sune Adduo'in da yake iya maimaitawa afili da kuma ransa.
Ori dake tsaye ciki ruɗu da tausayawa yayi saurin ƙarasawa gaban skeleton gawar M Jameel ya ɗauko goran ruwan kana ya dawo tare da miƙawa Lamiɗo yana mai cewa.
“Lamiɗo gashi ayayyafa masa”.
Karɓa Lamiɗo yayi kana ya buɗe tare da yayyafawa Moddibo dake kwance jikinsa amma ko kaɗan Moddibo bai motsa ba.
Kallon Buba Lamiɗo yayi kana yace.
“Ori taimaka min mu saka shi cikin Mota”.
Kai Buba ya gyaɗa.
Ɗaya daga cikin Folisawan ne yace.
“Ranka shi daɗe bari mu saka shi”.
Ya faɗa tare da kallon ɗan gidansa da Ido ya masa alamar yazo su kama Moddibo ƙarasawa yayi sannan suka ɗauki Moddibo suka sauƙa kasan dutsen, tare da sanya shi abayan Motar Malam Arɗo.
Folisawan kuwa ƙara sawa sukayi suka shiga ɗaukar hoton gawar skeleton M Jameel.
Bayan sun gama ɗauka tare yan dube-dubensu, da Babbansu da sauran suka saka handglove suka ƙarasa gaban gawar da niyyar sunjanye gawar Babbansun najan Igiyar da aka ɗauɗaureshi ƙasusuwan suka kakkarye tare da zubewa a ƙasa babu ta yanda zasu iya daukarsa Babban su ya umarci Coustable yaje ya ɗauko musu kwali abayan mota kana suka tattara gawar suka zuba acikin kwalin kana suka kwashe takalmansa da wayoyinsa suka saka awata leda.
Abba kuwa cikin wani irin yanayi ya nufi cikin jejin yana tafiya ba tare da shi kansa yasan inda ya nufaba.
Cikin sauri Lamiɗo ya nufesa tare da riƙe hannunsa cike da tausayawa yace.
“Alhj banan zamu bi ba can baya ne, hanyar kazo innu na maka hanyar da zamu bi”.
Kai Abba ya gyaɗa tare da bin bayan Lamiɗo baki ɗaya baya cikin nutsuwarsa ya kasa gane shin mafarki yake ko kuma azahirance komai ke faruwa.
Bayan sun isa Lamiɗo da kansa ya buɗe masa mota yashiga sannan shima yashiga.
Folisawan kuwa kwalin da gawar M Jameel ke ciki suka ɗauka tare da sawa abayan motarsu suka tafi gida.
Abba kuwa kallon hanya kawai yake baki ɗaya baya cikin hayyacinsa ganin yanayin da yake ciki ne yasa Malam Arɗo ya fara yi masa Adduo'i yana tofa masa kana yana faɗa afili.
Ahankali Abba ya fara sakin Ajiyar zuciya kana yashiga maimaita Adduo'in sannu Ahankali ya fara jin hankalinsa ya fara dawowa jikinsa.
Motar da Moddibo ke ciki Ori da police ɗaya ne aciki direct Asibiti suka nufa dashi.
Yayin da Motar dasu Abba da kuma gawar M Jameel ke ciki kai tsaye gida suka wuce, suna isa kai tsaye falonsa suka wuce police ɗin ne ya ɗauko kwalin Gawar M Jameel ya shigo dashi kana ya ajiye agabansu.
Hajiya Turai dake sashenta tana jin tsayuwar motoci ta fito zuwa falon Abba.
Ganin Abba zaune tare dasu Lamiɗo yasa ta nufi gefen Abba cikin yanayin damuwa tace.
“Alhj lafiya ya ake ciki Gawar waye kuka samu?”.
Ahankali ya ɗago Idanunsa da suka kaɗa sukayi jawur ya kalleta kana yayi ƙasa da kansa cikin raunin murya yace.
“Gawar Jameelu na ne!”.
Arazane Hajiya Turai ta kallesa zuciyarta na bugawa da masifar ƙarfi Idanunta akansa tace.
“Gawar Jameelu kuma!?”.
Kai ya gyaɗa mata Cikin tsananin tashin hankali da ruɗu ta fashe da kuka me tsuma zuciya tana furta.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n ina gawar yake?”.
Da hannu ya nuna mata kwalin dake gabansa.
Da kallo tabi kwalin cikin sauri ta sake Kallonsa Idanunta cike da ruwan hawaye tace.
“Gawar Jameelu ne acikin kwali haka?”.
Kai ya gyaɗa batare daya ɗago kaiba yace.
“Shine”.
Wani sabon kuka ta fashe dashi tana Girgiza kai Kukanta ne ya fito da Hajiya Karima itama ganin abinda ke faruwa yasa ta fashe da kuka.