Sashe 52
Sakayyah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin awa biyu Hajja Nana suka isa Jauro Yaya Washe gari Da safe yaya Ali ya koma Adamawa dashi da Abba suka tafi.
A ɓangaren Khausar kuwa tunda daga ranan da Hajja Nana tayi mata maganar aure ta watsar da maganar kasancewar Momynta bata sake yi mata maganar ba ita ma bata sake tada maganar ba hakan yasa bata ɗauki maganar da muhimmanci ba ita kuwa Mommy tasa aranta tun daga Ramadan ya kawo kai ta samu dama ta yanda zata roƙowa ƴar ta al'khairi idan har Aliyu al'khairi ne agareta Allah ya tabbatar mata da al'khairi idan kuma ba al'khairi bane Allah ya zaɓa mata mafi al'khairi shima kuma Allah ya musanya masa da mafi al'khairi.
Yau ya rage azumi saura kwana biyu da hantsi Mommy na zaune afalo taji Sallamar sabon mai gadinsu da aka kawo kallon Khausar dake riƙe da hisnul Muslim tana Azkhar tayi sai kuma ta maida kallonta ga Haiydar dake danna wayarta ta gyara zamanta tare da cewa.
“Haidar jeka duba lafiya Namadi ke Sallama”.
Kai Haiydar ya gyaɗa kana yace.
“Toh Mommy”.
Sannan ya miƙe ya fita.
Kallon Namadi dake tsaye yayi kana yace.
“Lafiya kuwa”.
Kai Namadi ya gyaɗa tare da faɗin.
“Kayane Alhaji ya aiko dasu Azo ashiga dashi ciki”.
“Ok kashigo dasu”. Ya faɗa tare da juyawa ya koma ciki.
Kallon Mommy Haiydar yayi kana yace.
“Kayan azumine Abbah ya aiko dasu shine Namadi zai shigo dasu”.
Jinjina kai Mommy tayi tare da cewa.
“Ok”.
Da Sallama Namadi yashigo kansa ɗauke da buhun shin kafa ya ajiye a store kana ya koma ya ɗauko na ɗanyen shinka yakai, sannan ya kuma kimawa ya rinƙa shigo da catton ɗin indomie, Catoon ɗin Spaghetti, Cotton ɗin Macoroni, Couscous, Buhun fulawa, Buhun niƙeƙƙen garin gero na kunu, buhun wake, buhun sugar Corn Flakes, Madara, Patoto, Doya Crate din ƙwoyi Jarkan mai Jarkan man ja haka ya riƙa shigowa da tarkacen kayan buƙata na Ramadan.
Kamar yanda ya kawo sashen su Khausar haka ya kai sashen Hajiya Bunayya.
Yayinda hakan take a kowani gida haka magidanta suka riƙa shiga da kayan azumi domin shiryawa wannan wata mai falala.
Acan ɓangaren gidansu Moddibo kuwa shida M Jameel amota Moddibo ke driving yayin da M Jameel ke gefen mai zaman banza sai kuma wani yaro daga baya mai suna Iro wanda ke musu aika hong sukayi aƙofar gidansu Moddibo kana suka shiga cikin gidan bayan Iro ya fita ya buɗe musu.
Innayi na zaune atsakar gida akan kujera ƴar tsugunno taji ƙaran mota na shiga cikin harabar gidan aranta tace yau lafiya Moddibo ke shigowa da mota har cikin gidan.
Moddibo kuwa kusa da Innayi yayi Parking motar tare da buɗe Murfin motar ya zira ƙafarsa ɗaya awaje ɗaya kuma na ciki M Jameel da Sadik kuma suka fita kusa da Innayi M Jameel ya zauna shi kuwa Sadik Boot ɗin motar ya buɗe tare da fito da buhun far n gero, Buhun wake, Buhun shinkafa ɗanye da gumi, Catoon ɗin indomie, Catoon, Spaghetti, Bushesh-shen kifi crate ɗin ƙwoyi, Gongwanaye mayen madara da Vournvita buhun, Sugar kwalin Lipton sai kuma naman rago da aka gyara gaba ɗaya ga kuma na shanu ga kifaye duk Sadik yasa su a fridge
Kallon Moddibo Innayi tayi sai kuma ta maida kallonta kan M Jameel dake kusa da ita tayi tare da cewa.
“Lalle kayan Azumi sun saƙƙo ga Azumi sai ƙaratowa yake yau saura kwana biyu ko uku”.
Kai M Jameel ya gyaɗa kana yace.
“Ai dai kam Innayi azumi yazo”.
Ya ida maganar tare dasa hannu acikin aljihunsa ya ciro Bandir ɗin kuɗi kimanin dubu ɗari ya miƙawa Innayi tare da faɗin.
“Innayi gashi babu yanda banyi da Moddibo ba yabarni in saya miki kayan Azumi amma dake ɗan baƙin haline baya so in samu lada yaƙi furrr yace komai shi zai siya gashi wannan ki riƙe kiyi yadda kika ga dama dasu”.
Kallon kuɗin Innayi tare da Girgiza kai kana tace.
“Ayyah Jameel am bana son wannan shungullan yanzu ni kuma me zanyi da wannan kuɗin kabar su Jameel am ni ba ɓuƙatar su nake ba”.
M Jameel kuwa zama ya gyara tare da fuskantar Innayi da kyau kana cikin wata raunan'niyar Murya ya lumshe idanunsa tare da cewa.
“Tunda muke tare daku tsawon shekaru Innayi daga ke har Moddibo ban taɓa ɗaukar abu in baku ku karɓa ba, duk abinda na baku sai kun mayar min dashi baya, ban sani ba wataƙil shi Moddibo yana ɗaukar Maganar Aunty Karima keyi amatsayin matakin ƙin karɓan abu awajena”.
Lumshe idanu Moddibo yayi tare da jingina kansa da Murfin motar yana sauraron abinda aminsa ke faɗa.
Ita kuwa Innayi idanu ta zuba masa tana nazarin kalamansa.
M Jameel ya cigaba da cewa.
“Abinda Moddibo bai saniba koya karɓi abu awajena ko karya karɓa ita gani take komai na rayuwarsa Ni nake masa dan haka gwara ma ya karɓa idan yaso ta tuhumesa da tushe”.
Ya furzar da iska mai zafi kana ya cigaba da cewa.
“Kema kuma Innayi ina ganin maganar mutane kike ɗauka da suke cewa Babana ke daukar ɗawainiyar ku amma ni nasan ba haka bane. Allah ne kaɗai ya barwa kansa sanin yanda kuke rayuwarku duk da aminantakar dake tsakani na da Moddibo har yau ɗin nan bansan taya kuke mu'amala da rayuwarku ba bansan ta yanda kuke samun abinda kuke biyan buƙatar rayuwarku ba kama daga karatun Moddibo kab babu aƙaramar makaranta zuwa hidimar fitanmu Makarantar waje ina sane ina kuma tunawa Naira biyar kun ƙi karɓan tallafi awajen Babana ku keyin komai abinda yasa mutanen gari suke ɗaukar haka suna lura da Moddibo ba wani sana'a yake ba sannan ana mamakin irin buƙatun da kuke yafi ƙarfin samun ku ko kuma tattalin ku Innayi!”.
Dariya mara sauti Innayi tayi tare da jinjina kai kana ta tsaida idanunta akan Moddibo daya dafe kansa sai kuma ta kalli M Jameel daya dafe kansa tayi murmushi tare da cewa.
“Abun aduhu ne Jamilu barshi kawai babu ɓuƙatar sai ansani, shi kansa Moddibo bai san komai akan al'amuran rayuwar nan ba bare ya gaya maka”.
Moddibo kuwa Sanyayyar Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da kallon M Jameel ya buɗe masa hannunsa alamar kaji dai nima bansan komai ba a cikin abubuwan da kake son sani.
Sai kuma Moddibo ya numfasa tare da lumshe Idanunsa kana cikin sanyin murya mai cike da rauni ya kalli Innayi tare da cewa.
“Kagani ni kaina ban san komai ba kama daga lokacin dana ke karatu.
Ni dai nasan tana min komai idan nayi magana sai tace gadon Iyayena da suka bar min ne, bansan inda ta ɓoye kuɗin ba na girma ma yanzu ta bani gadona ahannuna taƙi ko gani take har yanzu ban kai ba oho.
Kai kuma kana tuhumata kamar acikin aminantakar mu akwai abinda nake ɓoye maka, bayan kuma J ka sani babu wani shamaƙi tsakaninmu”.
Ya ƙarisa mgnar tare da
runtse idanunsa a take kuma ya buɗe su akan M Jameel da shima shi yake kallo, a hankali ya furzar da iska mai sanyi tare da cewa.
“J ba'ayi wani abu na duniya da ni Aliyu zan iya ɓoye maka ba, aminantakar mu ta wuce babin in ɓoye maka wani abu”.
Jinjina kai M Jameel yayi yana kallon amininsa cike da tausayawa.
Innayi kuwa murmushi tayi tare da jinjina kai amma ba tace komaiba ba.
Moddibo kuwa kallon Innayi yayi kana yace.
“Yanzu kuma hidimar da nake kai kan ka kasan inda nake samu tunda muna aiki kuma ana biyan mu sannan kuma. Ni kaina wataran saidai inga tayi min abu misali yanzu mota dai ni bansa araina ba kafin in ankara har ta saya anyi komai kafin ma mu dawo”.
Numfashi ya sauke kana ya cigaba da cewa.
“Babu yanda banyi da ita ta faɗa min ba idan ma a kuɗin gado nane tunda na girma ta bani abuna zan iya sarrafawa”.
Hararansa Innayi tayi kana tace.
“Anƙi abaka”.
Shiru M Jameel da Moddibo kai ya jinjina ba tare da tace komai ba sai tsirawa Innayi ido da sukayi.
Miƙewa M Jameel yayi yace.
“Bari mu tafi Innayi”.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Allah ya tsare”
Suka amsa da.
Amin
Shi kuwa Moddibo Kallon Innayi yayi kana yace.
“Innayi har yanzu yarinyar nan bata zoba?"
Jinjina kai Innayi tayi tare da cewa.
“Dama wannan shekarar Ummin Asma'u tace in bari zata turo min Asma'u dan ƴaƴan ƙabilun in sun zo gaba ɗaya lalata sukeyi sannan basajin magana to Asma'u zata zo ta tayani”.
Cikin kula ya kalli Innayi kana yace.
“Innayi anya Asma'u zata iya ayyukan da suna da yawa fa kinga akwai abincin da za'a dinga fitarwa na masallaci”.
Jinjina kai Innayi tayi kana tace.
“Zamu iya ai naga Asma'u tana da kuzari kuma nima da kuzarina da kuma lafiyata zan iya”.
Kai ya gyaɗa kana yace.
“Toh Allah ya temaka”.
Ta amsa da.
“Ameen”,Kana tace.
“Ai girkin ma na iya tsawon kwana goma sha biyar ne zamuyi”.
Kai M Jameel ya Jinjina kana yace.
”Eh haka ne Innayi”.
Sallama suka mata sannan M Jameel ya Miƙe.
Dama already Moddibo na cikin motar yaja suka tafi.
Kai tsaye kasuwa Moddibo ya sake nufa Kallonsa M Jameel yayi kana yace.
“Mai zamu kuma yi a kasuwa?".
Ba tare da Moddibo ya juya ya kallesa ba ya lumshe idanunsa kana yace.
“Idan muka je za kaga ni”.
Shiru M Jameel yayi har suka isa kasuwar kamar yanda Moddibo yayiwa Innayi siyayya haka ya sake sayan wasu Kallonsa M Jameel yayi tare da cewa.
“Wannan kayan na waye haka?”.
Anutse Moddibo yace.
“Ina ruwanka”.
Daga haka yaja motar suka fita kai tsaye hanyar gidan Ummi ya nufa.
Da sauri M Jameel ya juya ya kallesa kana yace.
“Ai baka isa ba Ummi ba zata karba ba ai kai ma idan zan kaiwa Innayi abu hana wa kakeyi”.
Moddibo kuwa baki ya taɓe kana yace.
“Ai ba Umminka kai ka ɗai bane harda ni dan haka kabarni in samu lada”.
Murmushi M Jameel yayi Amma baice komaiba.
A ɓangaren Khausar kuwa tunda daga ranan da Hajja Nana tayi mata maganar aure ta watsar da maganar kasancewar Momynta bata sake yi mata maganar ba ita ma bata sake tada maganar ba hakan yasa bata ɗauki maganar da muhimmanci ba ita kuwa Mommy tasa aranta tun daga Ramadan ya kawo kai ta samu dama ta yanda zata roƙowa ƴar ta al'khairi idan har Aliyu al'khairi ne agareta Allah ya tabbatar mata da al'khairi idan kuma ba al'khairi bane Allah ya zaɓa mata mafi al'khairi shima kuma Allah ya musanya masa da mafi al'khairi.
Yau ya rage azumi saura kwana biyu da hantsi Mommy na zaune afalo taji Sallamar sabon mai gadinsu da aka kawo kallon Khausar dake riƙe da hisnul Muslim tana Azkhar tayi sai kuma ta maida kallonta ga Haiydar dake danna wayarta ta gyara zamanta tare da cewa.
“Haidar jeka duba lafiya Namadi ke Sallama”.
Kai Haiydar ya gyaɗa kana yace.
“Toh Mommy”.
Sannan ya miƙe ya fita.
Kallon Namadi dake tsaye yayi kana yace.
“Lafiya kuwa”.
Kai Namadi ya gyaɗa tare da faɗin.
“Kayane Alhaji ya aiko dasu Azo ashiga dashi ciki”.
“Ok kashigo dasu”. Ya faɗa tare da juyawa ya koma ciki.
Kallon Mommy Haiydar yayi kana yace.
“Kayan azumine Abbah ya aiko dasu shine Namadi zai shigo dasu”.
Jinjina kai Mommy tayi tare da cewa.
“Ok”.
Da Sallama Namadi yashigo kansa ɗauke da buhun shin kafa ya ajiye a store kana ya koma ya ɗauko na ɗanyen shinka yakai, sannan ya kuma kimawa ya rinƙa shigo da catton ɗin indomie, Catoon ɗin Spaghetti, Cotton ɗin Macoroni, Couscous, Buhun fulawa, Buhun niƙeƙƙen garin gero na kunu, buhun wake, buhun sugar Corn Flakes, Madara, Patoto, Doya Crate din ƙwoyi Jarkan mai Jarkan man ja haka ya riƙa shigowa da tarkacen kayan buƙata na Ramadan.
Kamar yanda ya kawo sashen su Khausar haka ya kai sashen Hajiya Bunayya.
Yayinda hakan take a kowani gida haka magidanta suka riƙa shiga da kayan azumi domin shiryawa wannan wata mai falala.
Acan ɓangaren gidansu Moddibo kuwa shida M Jameel amota Moddibo ke driving yayin da M Jameel ke gefen mai zaman banza sai kuma wani yaro daga baya mai suna Iro wanda ke musu aika hong sukayi aƙofar gidansu Moddibo kana suka shiga cikin gidan bayan Iro ya fita ya buɗe musu.
Innayi na zaune atsakar gida akan kujera ƴar tsugunno taji ƙaran mota na shiga cikin harabar gidan aranta tace yau lafiya Moddibo ke shigowa da mota har cikin gidan.
Moddibo kuwa kusa da Innayi yayi Parking motar tare da buɗe Murfin motar ya zira ƙafarsa ɗaya awaje ɗaya kuma na ciki M Jameel da Sadik kuma suka fita kusa da Innayi M Jameel ya zauna shi kuwa Sadik Boot ɗin motar ya buɗe tare da fito da buhun far n gero, Buhun wake, Buhun shinkafa ɗanye da gumi, Catoon ɗin indomie, Catoon, Spaghetti, Bushesh-shen kifi crate ɗin ƙwoyi, Gongwanaye mayen madara da Vournvita buhun, Sugar kwalin Lipton sai kuma naman rago da aka gyara gaba ɗaya ga kuma na shanu ga kifaye duk Sadik yasa su a fridge
Kallon Moddibo Innayi tayi sai kuma ta maida kallonta kan M Jameel dake kusa da ita tayi tare da cewa.
“Lalle kayan Azumi sun saƙƙo ga Azumi sai ƙaratowa yake yau saura kwana biyu ko uku”.
Kai M Jameel ya gyaɗa kana yace.
“Ai dai kam Innayi azumi yazo”.
Ya ida maganar tare dasa hannu acikin aljihunsa ya ciro Bandir ɗin kuɗi kimanin dubu ɗari ya miƙawa Innayi tare da faɗin.
“Innayi gashi babu yanda banyi da Moddibo ba yabarni in saya miki kayan Azumi amma dake ɗan baƙin haline baya so in samu lada yaƙi furrr yace komai shi zai siya gashi wannan ki riƙe kiyi yadda kika ga dama dasu”.
Kallon kuɗin Innayi tare da Girgiza kai kana tace.
“Ayyah Jameel am bana son wannan shungullan yanzu ni kuma me zanyi da wannan kuɗin kabar su Jameel am ni ba ɓuƙatar su nake ba”.
M Jameel kuwa zama ya gyara tare da fuskantar Innayi da kyau kana cikin wata raunan'niyar Murya ya lumshe idanunsa tare da cewa.
“Tunda muke tare daku tsawon shekaru Innayi daga ke har Moddibo ban taɓa ɗaukar abu in baku ku karɓa ba, duk abinda na baku sai kun mayar min dashi baya, ban sani ba wataƙil shi Moddibo yana ɗaukar Maganar Aunty Karima keyi amatsayin matakin ƙin karɓan abu awajena”.
Lumshe idanu Moddibo yayi tare da jingina kansa da Murfin motar yana sauraron abinda aminsa ke faɗa.
Ita kuwa Innayi idanu ta zuba masa tana nazarin kalamansa.
M Jameel ya cigaba da cewa.
“Abinda Moddibo bai saniba koya karɓi abu awajena ko karya karɓa ita gani take komai na rayuwarsa Ni nake masa dan haka gwara ma ya karɓa idan yaso ta tuhumesa da tushe”.
Ya furzar da iska mai zafi kana ya cigaba da cewa.
“Kema kuma Innayi ina ganin maganar mutane kike ɗauka da suke cewa Babana ke daukar ɗawainiyar ku amma ni nasan ba haka bane. Allah ne kaɗai ya barwa kansa sanin yanda kuke rayuwarku duk da aminantakar dake tsakani na da Moddibo har yau ɗin nan bansan taya kuke mu'amala da rayuwarku ba bansan ta yanda kuke samun abinda kuke biyan buƙatar rayuwarku ba kama daga karatun Moddibo kab babu aƙaramar makaranta zuwa hidimar fitanmu Makarantar waje ina sane ina kuma tunawa Naira biyar kun ƙi karɓan tallafi awajen Babana ku keyin komai abinda yasa mutanen gari suke ɗaukar haka suna lura da Moddibo ba wani sana'a yake ba sannan ana mamakin irin buƙatun da kuke yafi ƙarfin samun ku ko kuma tattalin ku Innayi!”.
Dariya mara sauti Innayi tayi tare da jinjina kai kana ta tsaida idanunta akan Moddibo daya dafe kansa sai kuma ta kalli M Jameel daya dafe kansa tayi murmushi tare da cewa.
“Abun aduhu ne Jamilu barshi kawai babu ɓuƙatar sai ansani, shi kansa Moddibo bai san komai akan al'amuran rayuwar nan ba bare ya gaya maka”.
Moddibo kuwa Sanyayyar Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da kallon M Jameel ya buɗe masa hannunsa alamar kaji dai nima bansan komai ba a cikin abubuwan da kake son sani.
Sai kuma Moddibo ya numfasa tare da lumshe Idanunsa kana cikin sanyin murya mai cike da rauni ya kalli Innayi tare da cewa.
“Kagani ni kaina ban san komai ba kama daga lokacin dana ke karatu.
Ni dai nasan tana min komai idan nayi magana sai tace gadon Iyayena da suka bar min ne, bansan inda ta ɓoye kuɗin ba na girma ma yanzu ta bani gadona ahannuna taƙi ko gani take har yanzu ban kai ba oho.
Kai kuma kana tuhumata kamar acikin aminantakar mu akwai abinda nake ɓoye maka, bayan kuma J ka sani babu wani shamaƙi tsakaninmu”.
Ya ƙarisa mgnar tare da
runtse idanunsa a take kuma ya buɗe su akan M Jameel da shima shi yake kallo, a hankali ya furzar da iska mai sanyi tare da cewa.
“J ba'ayi wani abu na duniya da ni Aliyu zan iya ɓoye maka ba, aminantakar mu ta wuce babin in ɓoye maka wani abu”.
Jinjina kai M Jameel yayi yana kallon amininsa cike da tausayawa.
Innayi kuwa murmushi tayi tare da jinjina kai amma ba tace komaiba ba.
Moddibo kuwa kallon Innayi yayi kana yace.
“Yanzu kuma hidimar da nake kai kan ka kasan inda nake samu tunda muna aiki kuma ana biyan mu sannan kuma. Ni kaina wataran saidai inga tayi min abu misali yanzu mota dai ni bansa araina ba kafin in ankara har ta saya anyi komai kafin ma mu dawo”.
Numfashi ya sauke kana ya cigaba da cewa.
“Babu yanda banyi da ita ta faɗa min ba idan ma a kuɗin gado nane tunda na girma ta bani abuna zan iya sarrafawa”.
Hararansa Innayi tayi kana tace.
“Anƙi abaka”.
Shiru M Jameel da Moddibo kai ya jinjina ba tare da tace komai ba sai tsirawa Innayi ido da sukayi.
Miƙewa M Jameel yayi yace.
“Bari mu tafi Innayi”.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Allah ya tsare”
Suka amsa da.
Amin
Shi kuwa Moddibo Kallon Innayi yayi kana yace.
“Innayi har yanzu yarinyar nan bata zoba?"
Jinjina kai Innayi tayi tare da cewa.
“Dama wannan shekarar Ummin Asma'u tace in bari zata turo min Asma'u dan ƴaƴan ƙabilun in sun zo gaba ɗaya lalata sukeyi sannan basajin magana to Asma'u zata zo ta tayani”.
Cikin kula ya kalli Innayi kana yace.
“Innayi anya Asma'u zata iya ayyukan da suna da yawa fa kinga akwai abincin da za'a dinga fitarwa na masallaci”.
Jinjina kai Innayi tayi kana tace.
“Zamu iya ai naga Asma'u tana da kuzari kuma nima da kuzarina da kuma lafiyata zan iya”.
Kai ya gyaɗa kana yace.
“Toh Allah ya temaka”.
Ta amsa da.
“Ameen”,Kana tace.
“Ai girkin ma na iya tsawon kwana goma sha biyar ne zamuyi”.
Kai M Jameel ya Jinjina kana yace.
”Eh haka ne Innayi”.
Sallama suka mata sannan M Jameel ya Miƙe.
Dama already Moddibo na cikin motar yaja suka tafi.
Kai tsaye kasuwa Moddibo ya sake nufa Kallonsa M Jameel yayi kana yace.
“Mai zamu kuma yi a kasuwa?".
Ba tare da Moddibo ya juya ya kallesa ba ya lumshe idanunsa kana yace.
“Idan muka je za kaga ni”.
Shiru M Jameel yayi har suka isa kasuwar kamar yanda Moddibo yayiwa Innayi siyayya haka ya sake sayan wasu Kallonsa M Jameel yayi tare da cewa.
“Wannan kayan na waye haka?”.
Anutse Moddibo yace.
“Ina ruwanka”.
Daga haka yaja motar suka fita kai tsaye hanyar gidan Ummi ya nufa.
Da sauri M Jameel ya juya ya kallesa kana yace.
“Ai baka isa ba Ummi ba zata karba ba ai kai ma idan zan kaiwa Innayi abu hana wa kakeyi”.
Moddibo kuwa baki ya taɓe kana yace.
“Ai ba Umminka kai ka ɗai bane harda ni dan haka kabarni in samu lada”.
Murmushi M Jameel yayi Amma baice komaiba.