Sashe 81
Sakayyah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sauƙe ajiyar zuciya tayi tare da share hawaye masu zafin gaske da suka zubo mata kana tace.
“Kaga ma min komai Jamilu, kayi min komai Jamilu. Ubangiji Allah Yamaka albarka Allah Ubangiji ya rufa maka asiri duniya da lahira Allah yasa kagama da duniya lafiya”.
M Jameel kuwa sake Matsawa jikin Ummi yayi tare da ɗaura kansa akan cinyarta hawaye masu zafin gaske suka shiga bin kuncinsa Shar-shar-shar.
Ganin haka yasa Asma'u dake gefe ita hawaye suka shiga bin kuncinsa.
Kusa da Asma'u Bashir ya matsa tare da sanya hannu ya shiga share mata hawayen cikin raunin murya yace.
“Kiyi haƙuri Asma'u kada kiyi kuka kinga zaki ƙara karyarwa Ummi zuciya”.
Kai ta gyaɗa yayin da hawaye suka cigaba da zubowa daga Idanunta cikin sheshsheƙan Kuka tace.
“Ka gani fa Yah Jameel ma kuka ya keyi”.
Jin haka yasa M Jameel da Idanunsa ke jiƙe da hawaye ya ɗago kansa tare da sakar mata da murmushi kana yace.
“Hmmm Asma'u kinsan meyake sani kuka?”.
Kai ta girgiza still Hawaye na bin kuncinta.
Lumshe Idanunsa yayi tare da taune lips ɗin sa kana yace.
“Kada kiyi kuka saboda ke baki da abinda zai saki kuka”.
Cikin sheshsheƙan kuka ta kallesa still hawaye na zuba daga Idanunsa cikin wata raunan'niyar murya tace.
“Toh Yah Jameel me yake saka kuka Idan muna da iko zamu raba ka dashi”.
Girgiza kai yayi tare da rintse idanunsa kana yace.
“Ba zai rabu ba Asma'u tun tasowa ta aduniya bayan shekara goma sha huɗu bani da damuwar data wuce ganin Ummi bata gidan mahaifina, hankalina yana tashi akan hakan, kuma ina tunanin hakane badan faɗa da ƙaddararta ba, a'a saidai inajin maraici inajin kewar ta, inajin ciwon rashi mahaifiyata a cikin gidanmu, ina so ko yaushe Idan na tashi naga Ummi kusa dani haka zalika idan zan kwanta ya zama naje gareta taimin addu'a muyi saida safe”.
lumshe idonsa yayi yana mai jin wani irin yanayi azuciyar kana ya buɗe su tare da cewa.
“Ina so kafin naje na kwanta akowani dare in ganta kafin naje nayi bacci ina jin kamar nayi rashin komai na duniya da Ummi bata kusa dani ina jin mai zan mata na sauƙe hakkinta na uwa akaina”.
Shafa kansa Ummi tayi still hawaye nabin fuskarta kana cikin raunin murya tace.
“Toh wai meye rage da bakayi min ba? Ka kaini Makka, Ka kai ni Madina ka gina min kyakkyawan muhalli ka zuba min Kyakkyawan kayan ƙawa, ka riƙe cina shana suturata jinyata nawa dana ƙannen ka harma mijin da nake tare dashi har maƙotan dake tare dani baka barsu sun zubda hawayeba kanai musu dukkan abin buƙata”.
A hankali ta danne kukan dake ƙoƙarin sufce mata kana tace.
“Jamilu har maƙota nafa kagama yi musu komai”.
Murmushi M Jameel yayi still Hawaye na bin kyakkyawar fuskarsa kana yace.
“Har yanzu ban gama ba Ummi, sai dai ki tayani da addu'a Allah yasa in gama Allah yabani ikon gamawa”.
Sai kuma ya maida kallonsa kan Asma'u dake zubda hawaye har zuwa lokacin take kuka kana ya maida kallonsa ga Ummi yace.
“Ina Son inga na Aurar da Asma'u sannan inga Bashir ya zama babban mutum magidanci kafin wannan lokacin Ummi *INA SON INYI AURE”*.
Cikin sauri Ummi ta ɗago Idanunta dake jiƙe da hawaye ta kallesa kana tace.
“Me kace Jamilu?”.
Ɗago kansa yayi tare da kallonta kana ya jinjina mata kai tare da cewa.
*“Ummi ina so inyi Aure”.*
Cike da mamaki Ummi ke kallon aranta tace tunda nake arayuwarta Jameel bai taɓa faɗa min magana makamancin haka ba”.
Sake Kallonsa tayu akaro na barkatai kana tace.
Babana kaine? Kai da bakinka kake ce min kana so kayi Aure?”.
Jinjina kai yayi tare da faɗin.
“Ummi ina so inyi Aure in ɗaukeki ku dawo gidana dake da Malam sannan Asma'u da Bashir duk mu zauna tare dasu duk sanda gari ya waye na dawo gidana in ganki Kusa dani mu zauna afalonki ki bamu tea musha Idan dare yayi kafin na kwanta nazo na zauna afalonki ki bani Tea nasha”.
Sauƙe ajiyar zuciya yayi tare da lumshe idanunsa kana ya buɗesu tare da cewa.
“Sannan nayi hira da ƙanne na. Ina son haka Ummi shiyasa nake so nayi Aure Insha Allah Ummi zanyi Aure zanyi Aure”.
Ummi kuwa cike da mamaki da kuma jin daɗin kalamansa tayi yalwataccen murmushi kana tace.
“Haka naka”.
Da sauri ya rufe idanunsa tare da cewa.
“Ummi ni ɗin?”.
Cikin shafa kansa tace.
“Eh kai ɗin, wato dan kana son ka sanarmin zakayi aurene, sai kabi ka kashe min jiki, ka zauna ka tasani gaba harda kukanka, ko gaisawafa baka bari kunyiba, ashe du mgnar auren ce ke tsaburarka”.
Murmushi Asma'u da Bashir sukeyi cike da jin daɗi,
Shima M Jameel murmushi yakeyi tare da sunkuyar da kansa cike da alamun kunya.
Ita kuwa Ummi numfashin jin dadi ta fesar tare da cewa.
“Allah ya yarda Babana Ubangiji Allah ya nufa. Allah ya Al'barkanci rayuwar ka Allah ya nufa. Allah ya rufa maka asiri Allah ya maka kyakkyawan tanadi agidan Aljanna ya kuma yima zaɓi da mace ta gari”.
Murmushi yayi cike da jin daɗin Addu'ar ta ya shafa sajensa tare da cewa.
“Ameen Ummina”.
Asma'u da Bashir kuwa dariya sukayi suna jin ƙaunar Yayan nasu, miƙewa yayi tare da yiwa Ummi Sallama kana ya fice bayan tayi masa Allah ya tsare.
Kai tsaye gidansu ya nufa cikin nutsuwa yake Driving har ya isa gida bayan yayi Parking ya fito atsaye ya hango Abbansa akan barandar sashen sa ya goya hannunsa abaya.
Ganin Abba yasa ya nufesa Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe tare da kallon sa kana yace.
“Babana daga ina haka kake?”.
Langwaɓar da kai M Jameel yayi tare da sanyaya muryarsa kana yace.
“Abbah daga gidan Ummina nake”.
Numfashi Abbah ya fesar kana ya kalli agogon dake ɗaure atsintsiyar hannunsa tare da cewa.
“Babana kalli fa yanzu ƙarfe sha ɗaya da rabi Meyesa baka tsoro ne”.
Ajiyar zuciya M Jameel ya sauƙe tare da kallon Abba kana yace.
“To Abba tsoron me Mutum zaiji, duk guduna fa bazan guji ƙaddarata ba haka zalika duk saurina ƙaddarata ta fini sauri, kana duk hamzarina da kuma ɓuyana ƙaddarata tafini sanin inda nake”.
Jinjina kai Abba yayi kana yace.
“Duk da haka bana so Babana, duk inda kake indai ƙarfe sha ɗaya yayi ka kwana awajen, ba wani abin ni na amince ma nasan ba baza kwana alalaceccen waje ba ko kuma inda zai jaza min magana”.
Cike da ladabi ya jinjina kai kana yace.
“Toh Abbana”.
Kansa Abba ya shafa yace.
“Ubangiji Allah ya Albarkanci rayuwar ka Allah yatsareka da duk kan abinƙi”.
Murmushi yayi tare da faɗin.
“Ameen Abbana”.
Kana ya juya ya nufi ɗakinsa.
Acan gidan Lamiɗo kuwa Hajiya Aysha ce zaune da ƴaƴanta acikin falon su.
Ramadan dake zaune gefen Khausar ya ɗago kai tare da kallon ta kana yace.
“Addah Khausi ke kam kin huta da zuwa makaranta”.
Murmushi Khausar tayi tare da kallon Ramadan kana tace.
“Yanzu zan fara wani ai Ramadan”.
Ya mutse fuska yayi kana ya kalli Mommy dake zaune kan 2sitter yace.
“Mommy na”.
Ahankali Mommy ta ɗago kanta tare da cewa.
“Na'am Ramadan ɗina”.
Langwaɓar da kai yayi tare da marairaice murya kana yace.
“Ayyah Mommy am gobe abarni kar Inje makaranta mana”.
Kallonsa Mommy tayi tare da cewa.
“Toh Meyesa Ramadan?”.
Kai ya Girgiza kana ya marairaice murya tare da cewa.
“Mommy nidai kawai bana son zuwa Makarantar nan”.
Hankalinta ta mayar kansa kana tace.
“A'a Babana ba yadda za'a yi haka ace baka son zuwa makaranta. Ai yanzu ka fara zuwa ma”.
Araunace ya kalli Mommy tare da cewa.
“Dan Allah Mommy Gobe kawai.
Na goben nan dan Allah Mommy na kada Inje Mommy na goben nan kawai kada abarni Inje makaranta kada inje”.
Girgiza Kai Mommy tayi cike da kulawa tace.
“A'a Ramadan ya za'a yi inbarka ba kaje makaranta ba ai bazai yuwu ba dole ne kaje makaranta kam”.
Jan zuciya yayi tare da dafe kuncinsa kana yace.
“Mommy shikenan kin yarda in tafi?”.
Jinjina masa kai tayi tare da cewa.
“Na yarda mana kaje”.
Miƙewa yayi daga wajenta ya koma kusa da Khausar tare da riƙe Hannunta cikin yanayin roƙo ya langwaɓar da kai tare da marairaice murya yace.
“Addah Khausy ki tayani bawa Mommy haƙuri gobe kada Inje makaranta kice tabarni gobe kar Inje makaranta mu zauna da ita bana son zuwa makarantar nan Addah Khausi bana so ki faɗawa Mommy”.
Khausar kuwa Kallonsa ta riƙa yi har ya kai ƙarshe, ajiyar zuciya ta sauƙe tare da riƙe tafin hannunsa acikin nata kana tace.
“Toh Ramadan tun daga yanzun ka kana primary 3 sannan kace bakason zuwa makaranta Primary mafa yanzu kayi rabin gamawa ai Ramadan ka fara da wuri”.
Araunace Ramadan ya kalleta tare da cewa.
“Yanzu Addah Khausi zaki bari inje”.
Cikin rashin ɗaukar maganarsa da muhimmanci Khausar tace.
“Eh Sosai ma”.
Haiydar dake kwance kan 3sitter ya ɗago kansa tare da kallon Ramadan kana yace.
“Eh dolenka. Dolenka ma kaje”.
Sai kuma ya maida kallonsa kan Mommy dake kallon Ramadan kana yace.
“Allah Mommy Idan aka sakewa Ramadan ma bazai yi karatu ba”.
Tura baki Ramadan yayi tare da sake hannun Khausar ya koma jikin Mommy kana yace.
“Mommy ki faɗa masa ƙoƙarin da nake a hadda ai yasani ko.
Gasa akaje ni nake zuwa mana na ɗaya a sate ɗin mu”.
Jinjina kai Mommy tayi tare da cewa.
“Na sani Ramadan kana ma da kokari kawai dai da kake cewa kar abari kaje gobe abarka ka hutane bai yi ba. Idan ka tuna ma gobe Laraba ne idan kaje gobe jibi Alhamis zaka huta gata Friday shima zaka huta kaji ko Ramadan”.
Girgiza kai yayi still Idanunsa akan Mommy yace.
“Ayyah Mommy ni Banason zuwa ki barni mana”.
Khausar ne ta kallesa cike da mamaki tace.
“Ohh Ni Khausar yau kam naga ikon Allah da nacin yaro”.
Taɓe baki Haiydar yayi tare da cewa.
“Rabu dashi duk zai gama kuma dole gobe sai yaje makaranta”.
“Kaga ma min komai Jamilu, kayi min komai Jamilu. Ubangiji Allah Yamaka albarka Allah Ubangiji ya rufa maka asiri duniya da lahira Allah yasa kagama da duniya lafiya”.
M Jameel kuwa sake Matsawa jikin Ummi yayi tare da ɗaura kansa akan cinyarta hawaye masu zafin gaske suka shiga bin kuncinsa Shar-shar-shar.
Ganin haka yasa Asma'u dake gefe ita hawaye suka shiga bin kuncinsa.
Kusa da Asma'u Bashir ya matsa tare da sanya hannu ya shiga share mata hawayen cikin raunin murya yace.
“Kiyi haƙuri Asma'u kada kiyi kuka kinga zaki ƙara karyarwa Ummi zuciya”.
Kai ta gyaɗa yayin da hawaye suka cigaba da zubowa daga Idanunta cikin sheshsheƙan Kuka tace.
“Ka gani fa Yah Jameel ma kuka ya keyi”.
Jin haka yasa M Jameel da Idanunsa ke jiƙe da hawaye ya ɗago kansa tare da sakar mata da murmushi kana yace.
“Hmmm Asma'u kinsan meyake sani kuka?”.
Kai ta girgiza still Hawaye na bin kuncinta.
Lumshe Idanunsa yayi tare da taune lips ɗin sa kana yace.
“Kada kiyi kuka saboda ke baki da abinda zai saki kuka”.
Cikin sheshsheƙan kuka ta kallesa still hawaye na zuba daga Idanunsa cikin wata raunan'niyar murya tace.
“Toh Yah Jameel me yake saka kuka Idan muna da iko zamu raba ka dashi”.
Girgiza kai yayi tare da rintse idanunsa kana yace.
“Ba zai rabu ba Asma'u tun tasowa ta aduniya bayan shekara goma sha huɗu bani da damuwar data wuce ganin Ummi bata gidan mahaifina, hankalina yana tashi akan hakan, kuma ina tunanin hakane badan faɗa da ƙaddararta ba, a'a saidai inajin maraici inajin kewar ta, inajin ciwon rashi mahaifiyata a cikin gidanmu, ina so ko yaushe Idan na tashi naga Ummi kusa dani haka zalika idan zan kwanta ya zama naje gareta taimin addu'a muyi saida safe”.
lumshe idonsa yayi yana mai jin wani irin yanayi azuciyar kana ya buɗe su tare da cewa.
“Ina so kafin naje na kwanta akowani dare in ganta kafin naje nayi bacci ina jin kamar nayi rashin komai na duniya da Ummi bata kusa dani ina jin mai zan mata na sauƙe hakkinta na uwa akaina”.
Shafa kansa Ummi tayi still hawaye nabin fuskarta kana cikin raunin murya tace.
“Toh wai meye rage da bakayi min ba? Ka kaini Makka, Ka kai ni Madina ka gina min kyakkyawan muhalli ka zuba min Kyakkyawan kayan ƙawa, ka riƙe cina shana suturata jinyata nawa dana ƙannen ka harma mijin da nake tare dashi har maƙotan dake tare dani baka barsu sun zubda hawayeba kanai musu dukkan abin buƙata”.
A hankali ta danne kukan dake ƙoƙarin sufce mata kana tace.
“Jamilu har maƙota nafa kagama yi musu komai”.
Murmushi M Jameel yayi still Hawaye na bin kyakkyawar fuskarsa kana yace.
“Har yanzu ban gama ba Ummi, sai dai ki tayani da addu'a Allah yasa in gama Allah yabani ikon gamawa”.
Sai kuma ya maida kallonsa kan Asma'u dake zubda hawaye har zuwa lokacin take kuka kana ya maida kallonsa ga Ummi yace.
“Ina Son inga na Aurar da Asma'u sannan inga Bashir ya zama babban mutum magidanci kafin wannan lokacin Ummi *INA SON INYI AURE”*.
Cikin sauri Ummi ta ɗago Idanunta dake jiƙe da hawaye ta kallesa kana tace.
“Me kace Jamilu?”.
Ɗago kansa yayi tare da kallonta kana ya jinjina mata kai tare da cewa.
*“Ummi ina so inyi Aure”.*
Cike da mamaki Ummi ke kallon aranta tace tunda nake arayuwarta Jameel bai taɓa faɗa min magana makamancin haka ba”.
Sake Kallonsa tayu akaro na barkatai kana tace.
Babana kaine? Kai da bakinka kake ce min kana so kayi Aure?”.
Jinjina kai yayi tare da faɗin.
“Ummi ina so inyi Aure in ɗaukeki ku dawo gidana dake da Malam sannan Asma'u da Bashir duk mu zauna tare dasu duk sanda gari ya waye na dawo gidana in ganki Kusa dani mu zauna afalonki ki bamu tea musha Idan dare yayi kafin na kwanta nazo na zauna afalonki ki bani Tea nasha”.
Sauƙe ajiyar zuciya yayi tare da lumshe idanunsa kana ya buɗesu tare da cewa.
“Sannan nayi hira da ƙanne na. Ina son haka Ummi shiyasa nake so nayi Aure Insha Allah Ummi zanyi Aure zanyi Aure”.
Ummi kuwa cike da mamaki da kuma jin daɗin kalamansa tayi yalwataccen murmushi kana tace.
“Haka naka”.
Da sauri ya rufe idanunsa tare da cewa.
“Ummi ni ɗin?”.
Cikin shafa kansa tace.
“Eh kai ɗin, wato dan kana son ka sanarmin zakayi aurene, sai kabi ka kashe min jiki, ka zauna ka tasani gaba harda kukanka, ko gaisawafa baka bari kunyiba, ashe du mgnar auren ce ke tsaburarka”.
Murmushi Asma'u da Bashir sukeyi cike da jin daɗi,
Shima M Jameel murmushi yakeyi tare da sunkuyar da kansa cike da alamun kunya.
Ita kuwa Ummi numfashin jin dadi ta fesar tare da cewa.
“Allah ya yarda Babana Ubangiji Allah ya nufa. Allah ya Al'barkanci rayuwar ka Allah ya nufa. Allah ya rufa maka asiri Allah ya maka kyakkyawan tanadi agidan Aljanna ya kuma yima zaɓi da mace ta gari”.
Murmushi yayi cike da jin daɗin Addu'ar ta ya shafa sajensa tare da cewa.
“Ameen Ummina”.
Asma'u da Bashir kuwa dariya sukayi suna jin ƙaunar Yayan nasu, miƙewa yayi tare da yiwa Ummi Sallama kana ya fice bayan tayi masa Allah ya tsare.
Kai tsaye gidansu ya nufa cikin nutsuwa yake Driving har ya isa gida bayan yayi Parking ya fito atsaye ya hango Abbansa akan barandar sashen sa ya goya hannunsa abaya.
Ganin Abba yasa ya nufesa Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe tare da kallon sa kana yace.
“Babana daga ina haka kake?”.
Langwaɓar da kai M Jameel yayi tare da sanyaya muryarsa kana yace.
“Abbah daga gidan Ummina nake”.
Numfashi Abbah ya fesar kana ya kalli agogon dake ɗaure atsintsiyar hannunsa tare da cewa.
“Babana kalli fa yanzu ƙarfe sha ɗaya da rabi Meyesa baka tsoro ne”.
Ajiyar zuciya M Jameel ya sauƙe tare da kallon Abba kana yace.
“To Abba tsoron me Mutum zaiji, duk guduna fa bazan guji ƙaddarata ba haka zalika duk saurina ƙaddarata ta fini sauri, kana duk hamzarina da kuma ɓuyana ƙaddarata tafini sanin inda nake”.
Jinjina kai Abba yayi kana yace.
“Duk da haka bana so Babana, duk inda kake indai ƙarfe sha ɗaya yayi ka kwana awajen, ba wani abin ni na amince ma nasan ba baza kwana alalaceccen waje ba ko kuma inda zai jaza min magana”.
Cike da ladabi ya jinjina kai kana yace.
“Toh Abbana”.
Kansa Abba ya shafa yace.
“Ubangiji Allah ya Albarkanci rayuwar ka Allah yatsareka da duk kan abinƙi”.
Murmushi yayi tare da faɗin.
“Ameen Abbana”.
Kana ya juya ya nufi ɗakinsa.
Acan gidan Lamiɗo kuwa Hajiya Aysha ce zaune da ƴaƴanta acikin falon su.
Ramadan dake zaune gefen Khausar ya ɗago kai tare da kallon ta kana yace.
“Addah Khausi ke kam kin huta da zuwa makaranta”.
Murmushi Khausar tayi tare da kallon Ramadan kana tace.
“Yanzu zan fara wani ai Ramadan”.
Ya mutse fuska yayi kana ya kalli Mommy dake zaune kan 2sitter yace.
“Mommy na”.
Ahankali Mommy ta ɗago kanta tare da cewa.
“Na'am Ramadan ɗina”.
Langwaɓar da kai yayi tare da marairaice murya kana yace.
“Ayyah Mommy am gobe abarni kar Inje makaranta mana”.
Kallonsa Mommy tayi tare da cewa.
“Toh Meyesa Ramadan?”.
Kai ya Girgiza kana ya marairaice murya tare da cewa.
“Mommy nidai kawai bana son zuwa Makarantar nan”.
Hankalinta ta mayar kansa kana tace.
“A'a Babana ba yadda za'a yi haka ace baka son zuwa makaranta. Ai yanzu ka fara zuwa ma”.
Araunace ya kalli Mommy tare da cewa.
“Dan Allah Mommy Gobe kawai.
Na goben nan dan Allah Mommy na kada Inje Mommy na goben nan kawai kada abarni Inje makaranta kada inje”.
Girgiza Kai Mommy tayi cike da kulawa tace.
“A'a Ramadan ya za'a yi inbarka ba kaje makaranta ba ai bazai yuwu ba dole ne kaje makaranta kam”.
Jan zuciya yayi tare da dafe kuncinsa kana yace.
“Mommy shikenan kin yarda in tafi?”.
Jinjina masa kai tayi tare da cewa.
“Na yarda mana kaje”.
Miƙewa yayi daga wajenta ya koma kusa da Khausar tare da riƙe Hannunta cikin yanayin roƙo ya langwaɓar da kai tare da marairaice murya yace.
“Addah Khausy ki tayani bawa Mommy haƙuri gobe kada Inje makaranta kice tabarni gobe kar Inje makaranta mu zauna da ita bana son zuwa makarantar nan Addah Khausi bana so ki faɗawa Mommy”.
Khausar kuwa Kallonsa ta riƙa yi har ya kai ƙarshe, ajiyar zuciya ta sauƙe tare da riƙe tafin hannunsa acikin nata kana tace.
“Toh Ramadan tun daga yanzun ka kana primary 3 sannan kace bakason zuwa makaranta Primary mafa yanzu kayi rabin gamawa ai Ramadan ka fara da wuri”.
Araunace Ramadan ya kalleta tare da cewa.
“Yanzu Addah Khausi zaki bari inje”.
Cikin rashin ɗaukar maganarsa da muhimmanci Khausar tace.
“Eh Sosai ma”.
Haiydar dake kwance kan 3sitter ya ɗago kansa tare da kallon Ramadan kana yace.
“Eh dolenka. Dolenka ma kaje”.
Sai kuma ya maida kallonsa kan Mommy dake kallon Ramadan kana yace.
“Allah Mommy Idan aka sakewa Ramadan ma bazai yi karatu ba”.
Tura baki Ramadan yayi tare da sake hannun Khausar ya koma jikin Mommy kana yace.
“Mommy ki faɗa masa ƙoƙarin da nake a hadda ai yasani ko.
Gasa akaje ni nake zuwa mana na ɗaya a sate ɗin mu”.
Jinjina kai Mommy tayi tare da cewa.
“Na sani Ramadan kana ma da kokari kawai dai da kake cewa kar abari kaje gobe abarka ka hutane bai yi ba. Idan ka tuna ma gobe Laraba ne idan kaje gobe jibi Alhamis zaka huta gata Friday shima zaka huta kaji ko Ramadan”.
Girgiza kai yayi still Idanunsa akan Mommy yace.
“Ayyah Mommy ni Banason zuwa ki barni mana”.
Khausar ne ta kallesa cike da mamaki tace.
“Ohh Ni Khausar yau kam naga ikon Allah da nacin yaro”.
Taɓe baki Haiydar yayi tare da cewa.
“Rabu dashi duk zai gama kuma dole gobe sai yaje makaranta”.