Sashe 38
Sakayyah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Drower gefen dama ta ta kuma buɗe wa, wani farin roba ta jawo mai cike da ƙuli-ƙuli irin dogayen nan plate ta ɗauka saida ta cikashi kana ta maida ta rufe.
Sannan ta ɗebi borkono dai-dai misali.
Tasa a turmi kana ta sa kanamfari tare da Maggi star, Noo, Tera, Rayco, da dai sauransu, dakasu tayi , sannan tasa ƙaragon duk ta haɗa su ta dake su luƙui.
Kana ta kwashesa a wasu ƴan robobi masu masifar kyau da yan marafensu guda huɗu.
Fridge ɗin dake gefenta ta bude ta dauko goran ma shanu, ɗan wani tukunyan ƙasa ta ɗauka tare da tsulala manshanun,
Daya gefen ta kunna gas ɗin, kana ta ɗaura, sai kuma ta ɗauki manyan albasa har guda huɗu, gyarasu tayi kana ta yayyankasu.
Tukunyar da doyan ke ciki ta buɗe,
Kai ta jinjina ganin ya kusa dafuwa, da sauri ta watsa rabin albasan da ta yanka ɗin a kai.
Kana ta maida marfin ta rufe, tare da rage wutan.
Ɗan ludayi, tasa cikin man shanun jin ya daina bada sauti alamun ruwan ciki ya ƙare, sake raba albasan biyu tayi ta watsashi cikin man shanun.
Hhummmmmm taja wani dogon numfashi sabida wani irin masifeffen ƙamshi mai tsinka yawun mutun daya buɗe illahirin gidan.
Kashe wutan babbar tukunyar tayi dan ya dafu albasar, ta razanu.
Kana ta ɗauko kulli ta kwashe na sashin Hajia Bunayya tare dana Gimbiya Dadu.
Sai kuma na Abbansu,
Sannan na side dinsu.
Sauƙe man tayi kana ta cire wannan albasan daya fara ƙonewa, sai kuma ta juye wannan sauran, shuyuuuu ya bada sautin soyuwa da zafin man.
ɗaya daga cikin manyan ƙullin naman dake cikin fridge ta ɗauka mai sokoki zalla anyi ta kansu dogo-dogo.
Ɗaurayewa tayi tasa a yar madaidaicin tukunya ta zuba naman,
dama already ta jajjaga ɗanyen citta da tafarnuwa ta buɗe ta zuba aciki sannan ta Marmasa Maggi da time kana ta jajjaga attaruhu da albasa ta zuba tare da diban man shanun data soya ta watsa a ciki da duk sauran spices,Cikin Mintuna kaɗan kichen ɗin ya ɗauki mayataccen ƙamshin girkin dana man shanu daya wadata aciki zazzafan gashin da takeyiwa Abban.
Mommy kuwa ahankali ta miƙe tashiga kichen ɗin Idanunta akan Khausar dake wanke yan kwanunkan data ɓata, cikin alamun bacci tace.
“Ƙamshin girkin ki ne ya tasheni da gaba baccin.
nazo in tayaki gashi kuma naga kamar ma kin gama”.
Murmushi Khausar tayi tana motsa gashin naman mai romon da takeyi wanda tuni yanata ɓararraka kai ta jinjina kana tace.
“Mommy kije ki huta nama gama fa”.
Murmushi Mommy tayi kana tace.
“A'a kada ki damu ai baccin ya sakeni”.
Kai kawai Khausar ta gyaɗa sannan ta cigaba da aikinta tana sauƙe gashin Mommy ta taimaka mata suka juye kulan Abba da kuma na Dadu, saura kuma suka sawa Hajia Bunayya saura kuma suka barwa kansu.
“Yauwa ɗauki na Ummanki ki kai mata”.
cewar Mommy, cikin sauƙe numfashi Khausar ta ɗauka bayan ta sa jera yan robobin man shanun da yajin ƙuli-ƙulin, sai yar kulan gashin naman.
Kana ta nufi sashen bakinta ɗauke da sallama tashiga.
Amina dake zaune riƙe da waya ahannu ta watsa mata kallon tsana batare data amsa sallamar taba tace.
“Agola kin zo kina wani tunƙaho kamar gidan tsohonki ne Masarautar very soon zaki bar gidan nan dan nafi ƙarfin nayi shearing abinda nake so dake”.
Ya mutsa fuska Khausar tayi tare da jan siririn tsaki tace.
“Iska na wahalar dame kayan kara wannan ƴar masarautar kike mgn a kai har wata siyace”.
tana ida maganar ta fice batare data jira jin abinda Amina zata ceba.
Kai tsaye kichen ta nufa tsaye ta samu Mommy tana ɗauraye tukwanen da Khausar tayi amfani dashi kallon ta tayi tace.
“Ki ɗauki kular Gimbiya Dadu ki kai mata”.
Langwaɓar da kai Khausar tayi tace.
“Ayyah Mommy Haiydar ya Kai mana”.
Juyawa Mommy tayi ta kalleta da faɗin.
“Wai Khausar Meyesa idan na aike ki sashen Gimbiya Dadu sai kice in aiki Haiydar bana jin daɗin abinda kike min fa wato kina nuna min cewa ke ba jikarta bace?”.
Girgiza kai Khausar tayi tace.
“Wallahi Mommy Ina tsoron zuwa wajenta bana shiri da ita”.
Kallon Mamaki Mommy tayi mata kafin ta watsa mata harara da faɗin.
“Rufe min baki zakiji tsoronta ita ɗin kurace? wato kinje kakar ki tasa Miki ra'ayi da batun cewa ita Mayya ce da sauransu ko?”.
Girgiza kai Khausar tayi Idanunta cike da ruwan hawaye aranta tace. har yanzu Mommy ba zata gane ba taya zan ganar da ita cewa ni kaina na gamsu da cewa matar nan Mayya ce.
Amma nasan kona faɗa ba zata yarda ba dan yanda take haƙiƙan cewa akan ba Mayya bace ko ‘ya‘yan cikinta basa haƙiƙan cewa akan hakan, ita babu dama ace Gimbiya Dadu Mayya ce bayan ni da kaina naga alamomin hakan kuma ya fito da bakinta ta faɗa min ita Mayyace kawai ya rage amma sam Mommy taƙi yarda idan taji mutum ya fadawa Gimbiya Dadu Mayya aita bala'i da ita se kace Uwarta aka kira Mayya.
Ita kuwa Mommy ganin yanda Khausar ta tsirawa waje ɗaya idanu yasa aɗan fusace tace.
“Khausar ba magana nake Miki ba ko baza kije bane Inje da kaina?!”.
Asanyaye tace.
“Ayyah Mommy kiyi haƙuri zanje”.
Ta Faɗa tare da ɗaukar kulan ta fice tana furta.
”اعذبكلمتلله تممت منشررم حلق“.
Bakinta ɗauke da Sallama tashiga falon akan darduma taga Gimbiya Dadu na sallar maghariba cikin sauri ta ajiye kular.
Ita kuwa Gimbiya jin Muryan Khausar yasa cikin hanzari tayi sallama batare data idar ba ta juya ta zuba mata Na mujiya.
Ita kuwa Khausar cikin sauri ta juya ta fice daga sashen ta nufi sashen su tana sakin Ajiyar zuciya sai kuma ta furta.
“Alhamdulillah”.
Sosai tayi farin cikin tarar da Gimbiya Dadu tana Sallah.
Koda ta shiga Falon nasu bata samu Mommy ba da alama tana ciki tana sallah kai tsaye Bedroom ɗin su ta wuce tare da shiga toilet bayan tayi addu'a.
Anutse tayi alwala tare da fitowa da ƙafar dama.
Darduma mai taushi dake fitar da sanyayyan ƙamshi ta shimfiɗa kana ta sanya dogon hijabinta ta fuskanci alƙibla cikin nutsuwa tare da maida komai zuwa ga mahalicci ta gabatar da sallah bayan ta idar ta ɗaga hannunta biyu sama tare da lumshe Idanunta cikin tsantsar nutsuwa tare da ladabi alokacin neman wani buƙata ga Ubangiji mabuwayi gagara Misali ta ɗaga hannunta biyu tace.
“Ya waduud,Ya zul'arshil Majeed,Ya fa'alil lima yureed As'aluka bi izzatil lati la yura wa mulki kallazi la yurad wa nuru wajihikallazi mala alkana arshik najjini min hazal mujrimin ya Allah ka tsare min mahaifiyata da abinda ke cikinta daga sharrin Mai sharri”.
ta faɗa tare da shafawa Alkur'ani ta ɗauka ta fara Muraja'a tun daga Kahf sai data je Hajj kafin ta tsaya ta miƙe ta ida da Isha'i awajen ta kishingiɗa da haka bacci ya ɗauke ta.
Washe gari juma'a Khausar na zauna afalon Mommy akan Lallausan Capet yayin da Mommy ke saman kujera Khausar na matsa mata ƙafafunta ahankali Khausar ta ɗago kai tare da kallon Mommy da Idanunta ke lumshe tace.
“Mommy wallahi nayi missing Hajja Nana, Baffa Jauro Sadik, Dije duka mutanen Rugar ma nayi kewarsu gashi babu network bare nakira naji Muryansa”.
Murmushi Mommy tayi tare da jan numfashi kana ta buɗe Idanunta dake lumshe tace.
“Lalle kam Khausar yau kece ke faɗin Kinyi kewar Hajja Nana da bakin ki?”.
Murmushi Khausar tayi wanda ya lotsar da dimple ɗin ta kana tana cigaba da yiwa Mommy massaging ƙafafunta tace.
“Allah tana da daɗin zama kawai dai faɗanta da kuma mulkin mallaka da take nunawa yasa bamu jituwa amma tanason Babana da yawa sannan tana masa addu'a ni kuwa kinga duk mai yiwa Babana addu'a ina ƙaunarsa”.
Ta ƙarashe tare da buɗe Idanunta dake lumshe wanda ruwan hawaye ya cika su.
Shafa kanta Mommy tayi tare tace.
“Ubangiji Allah yajiƙan sa da rahma Allah ya gafarta masa Ubangiji ya jiƙan dukkan musulman da suka rigamu gidan gaskiya”.
Sanyayyar Ajiyar zuciya me haɗe da kyewa Khausar ta saki kana ahankali ta furta.
“Ameen”.
Mommy tace.
“Sai ki shirya idan kunyi wani hutun kije ki gansu”.
Wara ido Khausar tayi tare da gyara zamanta kana fuskarta ɗauke da murmushi tace.
“Ai lalle kam”.
Sai kuma tayi saurin juyawa jin Muryan Asma'u na sallama.
Ƙarasawa Falon Asma'u tayi tare da zama daga gefen hagun Khausar ta ajiye Handbag dake hannunta ta shiga Matsawa Mommy ƙafanta na hagu da faɗin.
“Mommy ina kwana yasu Raudat?”.
Hannu Mommy ta sanya ta shafa kanta da faɗin.
“Lafiya lau Asma'u ya gida yasu Umminki?”.
Asma'u na cigaba da Matsawa Mommy ƙafanta tace.
“Tana lafiya tace na gaisheki”.
Mommy tace.
“Ina amsawa”.
Ita kuwa khausar kallon Asma'u tayi tace.
“Sannu da zuwa taso mu shiga ciki”.
Kai Asma'u ta gyaɗa sannan ta miƙe ta ɗauki Handbag ɗin ta suka shiga.
Zama tayi agefen gadon Idanunta akan Khausar data buɗe ƙaramin fridge ta ɗebo mata kayan marmari tace.
“Anbani saƙon gaisuwa in kawo miki”.
Ajiye ƙaramin Plate ɗin Khausar tayi tare da zama tace.
“Toh ina Amsawa wani bawan Allah ne?”.
Da sauri Asma'u ta ƙumshe dariyar dake cikinta kana tace.
“Moddibo ne yace agaisheki da hannu”.
Zare idanu Khausar tayi lokaci ɗaya ta ƙware da Inabi dake bakinta da dugu ta miƙe ta nufi fridge ta ɓude Goran Swan water ta ɓude ta kafa abakinta saida tasha fiye da rabi kafin ta janye roban daga bakinta tana maida numfashi.
Asma'u kuwa kasa riƙe dariyar ta tayi cikin dariya sosai tace.
“Me haka Khausar daga jin sunan Moddibo zaki wani ruɗe haka?,sai kace wani abin tsoro!?”.
Zama Khausar tayi tana maida numfashi tace.
“Wallahi mutumin nan ya wuce inda kike tunani yanda kika san bashida zuciya aƙirjinsa baya jin bada haƙuri fa”.
Ta ida maganar tare da jan siririn tsaki tana tuno fuskar Moddibo lokacin da take bashi haƙuri.
Sannan ta ɗebi borkono dai-dai misali.
Tasa a turmi kana ta sa kanamfari tare da Maggi star, Noo, Tera, Rayco, da dai sauransu, dakasu tayi , sannan tasa ƙaragon duk ta haɗa su ta dake su luƙui.
Kana ta kwashesa a wasu ƴan robobi masu masifar kyau da yan marafensu guda huɗu.
Fridge ɗin dake gefenta ta bude ta dauko goran ma shanu, ɗan wani tukunyan ƙasa ta ɗauka tare da tsulala manshanun,
Daya gefen ta kunna gas ɗin, kana ta ɗaura, sai kuma ta ɗauki manyan albasa har guda huɗu, gyarasu tayi kana ta yayyankasu.
Tukunyar da doyan ke ciki ta buɗe,
Kai ta jinjina ganin ya kusa dafuwa, da sauri ta watsa rabin albasan da ta yanka ɗin a kai.
Kana ta maida marfin ta rufe, tare da rage wutan.
Ɗan ludayi, tasa cikin man shanun jin ya daina bada sauti alamun ruwan ciki ya ƙare, sake raba albasan biyu tayi ta watsashi cikin man shanun.
Hhummmmmm taja wani dogon numfashi sabida wani irin masifeffen ƙamshi mai tsinka yawun mutun daya buɗe illahirin gidan.
Kashe wutan babbar tukunyar tayi dan ya dafu albasar, ta razanu.
Kana ta ɗauko kulli ta kwashe na sashin Hajia Bunayya tare dana Gimbiya Dadu.
Sai kuma na Abbansu,
Sannan na side dinsu.
Sauƙe man tayi kana ta cire wannan albasan daya fara ƙonewa, sai kuma ta juye wannan sauran, shuyuuuu ya bada sautin soyuwa da zafin man.
ɗaya daga cikin manyan ƙullin naman dake cikin fridge ta ɗauka mai sokoki zalla anyi ta kansu dogo-dogo.
Ɗaurayewa tayi tasa a yar madaidaicin tukunya ta zuba naman,
dama already ta jajjaga ɗanyen citta da tafarnuwa ta buɗe ta zuba aciki sannan ta Marmasa Maggi da time kana ta jajjaga attaruhu da albasa ta zuba tare da diban man shanun data soya ta watsa a ciki da duk sauran spices,Cikin Mintuna kaɗan kichen ɗin ya ɗauki mayataccen ƙamshin girkin dana man shanu daya wadata aciki zazzafan gashin da takeyiwa Abban.
Mommy kuwa ahankali ta miƙe tashiga kichen ɗin Idanunta akan Khausar dake wanke yan kwanunkan data ɓata, cikin alamun bacci tace.
“Ƙamshin girkin ki ne ya tasheni da gaba baccin.
nazo in tayaki gashi kuma naga kamar ma kin gama”.
Murmushi Khausar tayi tana motsa gashin naman mai romon da takeyi wanda tuni yanata ɓararraka kai ta jinjina kana tace.
“Mommy kije ki huta nama gama fa”.
Murmushi Mommy tayi kana tace.
“A'a kada ki damu ai baccin ya sakeni”.
Kai kawai Khausar ta gyaɗa sannan ta cigaba da aikinta tana sauƙe gashin Mommy ta taimaka mata suka juye kulan Abba da kuma na Dadu, saura kuma suka sawa Hajia Bunayya saura kuma suka barwa kansu.
“Yauwa ɗauki na Ummanki ki kai mata”.
cewar Mommy, cikin sauƙe numfashi Khausar ta ɗauka bayan ta sa jera yan robobin man shanun da yajin ƙuli-ƙulin, sai yar kulan gashin naman.
Kana ta nufi sashen bakinta ɗauke da sallama tashiga.
Amina dake zaune riƙe da waya ahannu ta watsa mata kallon tsana batare data amsa sallamar taba tace.
“Agola kin zo kina wani tunƙaho kamar gidan tsohonki ne Masarautar very soon zaki bar gidan nan dan nafi ƙarfin nayi shearing abinda nake so dake”.
Ya mutsa fuska Khausar tayi tare da jan siririn tsaki tace.
“Iska na wahalar dame kayan kara wannan ƴar masarautar kike mgn a kai har wata siyace”.
tana ida maganar ta fice batare data jira jin abinda Amina zata ceba.
Kai tsaye kichen ta nufa tsaye ta samu Mommy tana ɗauraye tukwanen da Khausar tayi amfani dashi kallon ta tayi tace.
“Ki ɗauki kular Gimbiya Dadu ki kai mata”.
Langwaɓar da kai Khausar tayi tace.
“Ayyah Mommy Haiydar ya Kai mana”.
Juyawa Mommy tayi ta kalleta da faɗin.
“Wai Khausar Meyesa idan na aike ki sashen Gimbiya Dadu sai kice in aiki Haiydar bana jin daɗin abinda kike min fa wato kina nuna min cewa ke ba jikarta bace?”.
Girgiza kai Khausar tayi tace.
“Wallahi Mommy Ina tsoron zuwa wajenta bana shiri da ita”.
Kallon Mamaki Mommy tayi mata kafin ta watsa mata harara da faɗin.
“Rufe min baki zakiji tsoronta ita ɗin kurace? wato kinje kakar ki tasa Miki ra'ayi da batun cewa ita Mayya ce da sauransu ko?”.
Girgiza kai Khausar tayi Idanunta cike da ruwan hawaye aranta tace. har yanzu Mommy ba zata gane ba taya zan ganar da ita cewa ni kaina na gamsu da cewa matar nan Mayya ce.
Amma nasan kona faɗa ba zata yarda ba dan yanda take haƙiƙan cewa akan ba Mayya bace ko ‘ya‘yan cikinta basa haƙiƙan cewa akan hakan, ita babu dama ace Gimbiya Dadu Mayya ce bayan ni da kaina naga alamomin hakan kuma ya fito da bakinta ta faɗa min ita Mayyace kawai ya rage amma sam Mommy taƙi yarda idan taji mutum ya fadawa Gimbiya Dadu Mayya aita bala'i da ita se kace Uwarta aka kira Mayya.
Ita kuwa Mommy ganin yanda Khausar ta tsirawa waje ɗaya idanu yasa aɗan fusace tace.
“Khausar ba magana nake Miki ba ko baza kije bane Inje da kaina?!”.
Asanyaye tace.
“Ayyah Mommy kiyi haƙuri zanje”.
Ta Faɗa tare da ɗaukar kulan ta fice tana furta.
”اعذبكلمتلله تممت منشررم حلق“.
Bakinta ɗauke da Sallama tashiga falon akan darduma taga Gimbiya Dadu na sallar maghariba cikin sauri ta ajiye kular.
Ita kuwa Gimbiya jin Muryan Khausar yasa cikin hanzari tayi sallama batare data idar ba ta juya ta zuba mata Na mujiya.
Ita kuwa Khausar cikin sauri ta juya ta fice daga sashen ta nufi sashen su tana sakin Ajiyar zuciya sai kuma ta furta.
“Alhamdulillah”.
Sosai tayi farin cikin tarar da Gimbiya Dadu tana Sallah.
Koda ta shiga Falon nasu bata samu Mommy ba da alama tana ciki tana sallah kai tsaye Bedroom ɗin su ta wuce tare da shiga toilet bayan tayi addu'a.
Anutse tayi alwala tare da fitowa da ƙafar dama.
Darduma mai taushi dake fitar da sanyayyan ƙamshi ta shimfiɗa kana ta sanya dogon hijabinta ta fuskanci alƙibla cikin nutsuwa tare da maida komai zuwa ga mahalicci ta gabatar da sallah bayan ta idar ta ɗaga hannunta biyu sama tare da lumshe Idanunta cikin tsantsar nutsuwa tare da ladabi alokacin neman wani buƙata ga Ubangiji mabuwayi gagara Misali ta ɗaga hannunta biyu tace.
“Ya waduud,Ya zul'arshil Majeed,Ya fa'alil lima yureed As'aluka bi izzatil lati la yura wa mulki kallazi la yurad wa nuru wajihikallazi mala alkana arshik najjini min hazal mujrimin ya Allah ka tsare min mahaifiyata da abinda ke cikinta daga sharrin Mai sharri”.
ta faɗa tare da shafawa Alkur'ani ta ɗauka ta fara Muraja'a tun daga Kahf sai data je Hajj kafin ta tsaya ta miƙe ta ida da Isha'i awajen ta kishingiɗa da haka bacci ya ɗauke ta.
Washe gari juma'a Khausar na zauna afalon Mommy akan Lallausan Capet yayin da Mommy ke saman kujera Khausar na matsa mata ƙafafunta ahankali Khausar ta ɗago kai tare da kallon Mommy da Idanunta ke lumshe tace.
“Mommy wallahi nayi missing Hajja Nana, Baffa Jauro Sadik, Dije duka mutanen Rugar ma nayi kewarsu gashi babu network bare nakira naji Muryansa”.
Murmushi Mommy tayi tare da jan numfashi kana ta buɗe Idanunta dake lumshe tace.
“Lalle kam Khausar yau kece ke faɗin Kinyi kewar Hajja Nana da bakin ki?”.
Murmushi Khausar tayi wanda ya lotsar da dimple ɗin ta kana tana cigaba da yiwa Mommy massaging ƙafafunta tace.
“Allah tana da daɗin zama kawai dai faɗanta da kuma mulkin mallaka da take nunawa yasa bamu jituwa amma tanason Babana da yawa sannan tana masa addu'a ni kuwa kinga duk mai yiwa Babana addu'a ina ƙaunarsa”.
Ta ƙarashe tare da buɗe Idanunta dake lumshe wanda ruwan hawaye ya cika su.
Shafa kanta Mommy tayi tare tace.
“Ubangiji Allah yajiƙan sa da rahma Allah ya gafarta masa Ubangiji ya jiƙan dukkan musulman da suka rigamu gidan gaskiya”.
Sanyayyar Ajiyar zuciya me haɗe da kyewa Khausar ta saki kana ahankali ta furta.
“Ameen”.
Mommy tace.
“Sai ki shirya idan kunyi wani hutun kije ki gansu”.
Wara ido Khausar tayi tare da gyara zamanta kana fuskarta ɗauke da murmushi tace.
“Ai lalle kam”.
Sai kuma tayi saurin juyawa jin Muryan Asma'u na sallama.
Ƙarasawa Falon Asma'u tayi tare da zama daga gefen hagun Khausar ta ajiye Handbag dake hannunta ta shiga Matsawa Mommy ƙafanta na hagu da faɗin.
“Mommy ina kwana yasu Raudat?”.
Hannu Mommy ta sanya ta shafa kanta da faɗin.
“Lafiya lau Asma'u ya gida yasu Umminki?”.
Asma'u na cigaba da Matsawa Mommy ƙafanta tace.
“Tana lafiya tace na gaisheki”.
Mommy tace.
“Ina amsawa”.
Ita kuwa khausar kallon Asma'u tayi tace.
“Sannu da zuwa taso mu shiga ciki”.
Kai Asma'u ta gyaɗa sannan ta miƙe ta ɗauki Handbag ɗin ta suka shiga.
Zama tayi agefen gadon Idanunta akan Khausar data buɗe ƙaramin fridge ta ɗebo mata kayan marmari tace.
“Anbani saƙon gaisuwa in kawo miki”.
Ajiye ƙaramin Plate ɗin Khausar tayi tare da zama tace.
“Toh ina Amsawa wani bawan Allah ne?”.
Da sauri Asma'u ta ƙumshe dariyar dake cikinta kana tace.
“Moddibo ne yace agaisheki da hannu”.
Zare idanu Khausar tayi lokaci ɗaya ta ƙware da Inabi dake bakinta da dugu ta miƙe ta nufi fridge ta ɓude Goran Swan water ta ɓude ta kafa abakinta saida tasha fiye da rabi kafin ta janye roban daga bakinta tana maida numfashi.
Asma'u kuwa kasa riƙe dariyar ta tayi cikin dariya sosai tace.
“Me haka Khausar daga jin sunan Moddibo zaki wani ruɗe haka?,sai kace wani abin tsoro!?”.
Zama Khausar tayi tana maida numfashi tace.
“Wallahi mutumin nan ya wuce inda kike tunani yanda kika san bashida zuciya aƙirjinsa baya jin bada haƙuri fa”.
Ta ida maganar tare da jan siririn tsaki tana tuno fuskar Moddibo lokacin da take bashi haƙuri.