Sashe 4
Sakayyah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tuni su Khausar kuwa sun shiga school bos ɗinsu,
Amina ce ƙanwar Asiya mai binta ta kalli Ramadan dake cewa.
“Kalli fa 8:13 na tabbatar yauma zamu zanu”.
Cikin sanyi tace.
“Mu dai Allah ya rufa mana asiri daga SS 2 akwai matan aure da yawa a ciki, so ba batun duka a side ɗin mu.
Kuma ma duk bama saɓa doka cikin nitsuwa da tarbiyyar mu muke, ko nayi litting nasan za'ayi min uzuri.
Cike da jin daɗi, Khausar tace.
“Nima dai Allah ya yaye min masifa da cin zalin su Moddibo tunda yau dai zan tafi Ss 1 ɗin, da ba duka ba zagi, wlh inci karena babu babbaka”.
Taɓe baki Haydar yayi tare da cewa.
“Mu gefen maza, babu manya, duk yarane, manyan da dare suke zuwa, shiyasa babu roggomi”.
Asiya ce ta kalli Khausar cikin yanayin son yarinyar tare da cewa.
“Ai wlh ke dai in baki nitsuwa ba ko jami'a kikaje in dai Moddibo na cikin malamanku, na tabbatar zai san matakin da zai ɗauka a kanki.
Sannan ma da kike batun kin tafi Ss1 akwai matan aure, kin mance cewa, na safene, na islami.
Akwai na rana zuwa biyar bokone, kuma kuna tare da moddibo.”
Kwaffa tayi tare da cewa.
“Kai na shiga ukuna wlh”..
Anan gefen su Modibbo ku, fir innayi taki aje asibitin. Su kuna su kasa fahimtar ta, gani suke zafin zazzaɓin maleria ne yake son sata surutai shiyasa suke hanata mgn sukayi ta mata addu'o'i hardai ta ɗan fara samun nitsuwa har bacci ya ɗan sureta.
Gani ta ɗan rumtsane yasa suka tafi wurin Ummin M Jameel suka ɗauko Ummin dan tazo ta ɗan kula da ita.
Suna isa bakin gate, ba tare da sun shigaba, Ummin ta kalli M Jamil da yayi saurin fitowa bayan yayi parking marfin motar ya buɗe, mata cikin tsananin son mahaifiyar tasa, yace.
“Bismillah Ummi fito ki shiga wurin Innayinki, domin mu dai yau mun gaza gane kanta, da alamun Ita dai dare ɗaya gigin tsufa ya sauƙo mata”.
Ɗan buge ƙeyarsa tayi tare da ciwa.
“Tsufa kan zai cimma taka uwar mafa, kawai dai inaga zafin zazzaɓine kusan wasu lokutan yanasa yara surutai, to ita kuma girma yazo dole in ciwon yayi zafi zatayi kamar na yara”.
Juyowa tayi ta kalli Moddibo daya jingina kansa jikin kujerar gaban motar gefen mai zaman banza,
Cikin sanyin murya yace.
“Uhmmmm Ummi waifa cewa tai taga taurari suna sauƙowa ƙasa har kamar zasu taɓa rufin side nan, anya kuwa Ummi wannan zazzaɓi ne?”.
Sai kuma ya ɗan fesar da numfashi tare da lumshe idanunsa cikin alamun nazari yace.
“Ina tsoron kada fa matsalar ƙwaƙwalwa ce, nayi nayi muje asibiti kuma taƙi.”
Ya dire mgn tare haɗa kan yatsun hannunsa.
Jamil ne yaci gaba da cewa.
“Saida fa Moddibo yayi ta mata tofi kafin muka samu tayi bacci har muka fito ɗin.”
Cikin kulawa Ummi tace.
“In sha Allah babu komai, bari in shiga, ku kuje”.
To Jamil yace kana ya shiga mota, ita kuma tayi cikin gidan.
A hankali ya miƙa dalleliyar motarsa ƙirar BMW kan shimfiɗeɗen titin,
Yana tafiyar hawainiya, murmushin yayi ganin kallon da Moddibo yake masa.
“Sanin yau za'a dawo makaranta ne, yasa nayi ƙoƙarin dawowa baro Marrocco, duk da akwai ayyukan da ban gama dasu a company'nba,”.
Cewar M Jamil shi kuwa Moddibo kai ya jinjina alamun yana jinsa, shi kuwa M Jamil gudu ya ɗan ƙara tare da ci gaba da mgn dan yasan ba lallai ne Moddibo ya amsa mishi da bakiba, inda sabo ya saba, kuma shi yasan cewa body language al'adane ko ɗabi'a koma yace halittar Moddibo ne.
Juyowa yayi ya kalleshi tare da cewa.
“Na zaƙu muje makarantar nan, dan nasan zaiyi kyau sosai a tsarin gyarashi da akayi”.
Cikin ɗan ƙwaɓe fuska yace.
“In an gama gyaran ba”.
Da sauri M Jamil yace.
“Kamar yaya za'a gama mana”.
Juyowa yayi ya ɗan kalli M Jamil ta gefen ido kana a takaice yace.
“Toh ba'a gaman ba”.
Cikin sauri M Jamil yace.
“A.S da gaske ba'a gama ba?”.
A.S shine sunan da yake kiran Moddibo dashi kuma su biyu kaɗai suka san ma'anar sai kuma abokan karatunsu.
Shi kuwa Modibbo littafin dake gaban motar ya ɗauka tare da buɗe wa kana yace.
“Dama tun lokacin da za'a bada hutun na faɗa bazai isa a gama gyaran school ɗin ba, musamman da ya zama an ƙara yawan class, kana ga gina hall din da akace za'ayi, kuma dole aikin bazaiyi guduba sabida Ramadan, tun lokacin nace a ƙara kwanakin hutun, sabida samun isasshen lokacin, wannan Ba fulatanin yaƙi”.
Murmushin M Jamil yayi tare da cewa.
“Toh kai meyasa baka ƙara hutunba, ai da sai ka sanar”.
Juyowa yayi ya kalleshi bayan hannunsa yasa ya shafa tattausan sajensa tare da cewa.
“Uhmmmm”.
Ya san me wannan Uhmmm ɗin take nufi, kai ya jinjina tare da cewa, “Mu dai yan kallone,".
Da sauri yace.
“Nima haka, dan na gaji ko yaushe sai ya kwaɓa abu yazo yana cemin ina mafita”.
Dai-dai lokacin aka buɗe musu gate din makarantar, Ya Salam.
Wani irin tsarine da zubi makarantar yake dashi, tsari mai burgewa, yayinda shima makarantar Moddibo ya ƙawatata da tsirrai na kyautata muhalli.
Tabbas gyara kam da saura ba'a gama shi ba.
Domin daga woje dai kam an kammala komai amman daga ciki, duk cikin ajujuwan a hargitse yake.
M Jamil nayin parking, wani kekkyawan dattijo bafulatani ya nufo matar tasu da sauri, bisa alamu dai shine shugaban makarantar domin duk malaman na miƙa gaisuwar garesa cikin mutuntawa.
“Moddibo! Moddibo!! Moddibo!!!.”
Jamil ne ya fito yana murmushin tare da cewa.
“Allah rene,”.
Da sauri yace.
“Ina Moddibo”.
Cikin motar Jamil ya nuna masa, da sauri ya sunkuyo,
Yayinda shi kuwa Moddibo meda bayansa yayi ya jingina tare da lumshe idanunsa, murmushi Dattijon yayi tare da cewa.
“Ga ɗalibai duk sun dawo makaranta ta cika maƙil ga sabbin ɗauka, kuma aiki baifi rabi ba, ya zamuyi?”.
Cikin taɓe baki yace.
“Allahu a'lamu!”.
Jamil ne ya juyo ya kalli Malam Ahmad da Malam Habibullah da suma fitowar su kenan daga can cikin makarantar.
Shi kuwa Malam Arɗo Umaru mamallakin makarantar kuma .
Kai ya ɗan dafe tare da cewa.
“Dan Allah ka fito Moddibo kasan bayanin da zakayi musu, kana ka kara musu kwanakin hutun, tsawon lokacin da kakega za'a iya gama gyaran”.
Yadda ya dire mgnar da karya wuyane yasa Moddibo fitowa.
Murmushin sauran malaman sukayi, domin sosai tsufa ya fara cimma Mala Arɗo, zuwa yanzu ya kamata ragamar makarantar ya zama a hannun yara, domin badon Allah yasa Moddibo ke tsara komai na jadawalin abubuwan ciki da wajen makarantar ba, da tuni ta durƙushe, to amman sabida shi da sauran haziƙan malamai da suke da tsananin kula da tarbiyyar yara da sukeyi yasa har yau makarantar bata da na biyu a faɗin birnin Gembila.
Kusan a tare suka rakaya cikin makarantar.
Yayinda hayanin ɗalibai manya da yara maza da mata, ke tashi.
Juyowa yayi ya kalli Jamil tare da cewa.
“J kaje masallaci kayi mgn duk mu su haɗu a tsohon halla ɗin mu na sama.”.
To Jamil yace yana tunanin to me zaice musu,
Masallacin ya wuce tare da yin sanarwan.
Nan take kuwa, duk ɗaliban suka haura sama, suka shiga cikin babban hall ɗin nasu wanda yake ƙato sai dai duk da haka yanzu ya musu ƙaramin,.
A gafen mazama suma duk sun haɗu a halla nasu.
Shi kuwa Moddibo office nasa ya wuce.
Jim kaɗan ya fito, da Lapel Microphone a hannunsa yana saƙalasa a wuyan tattausan jallabiyar jikinsa Malam Ahmad ne ya matso kusa dashi tare da cewa.
“Zamu jirane ko an ƙara mana hutu”.
Ɗan murmushin gefen baki yayi tare da cewa.
“Hutu kuwa sosai ma har na tsawon mako uku za'a ƙara”.
Cike da murmushi yace.
“Mu tafi kenan”.
Kai ya gyaɗa masa tare da cewa.
“Suma duk yanzu zan kaɗa kansu ko wacce tai gida sai dai muma muna da zama na musamman”.
Ai kuwa jin haka yasa duk malam suka zauna jiran.
Shi kuwa ya haura saman yana mgn da M Jamil a waya.
“Su maza basu da hayaniya, kawai J ka ɗanyi musu nasiha, kana kace sai bayan mako uku zasu dawo kafin nan an gama gyara,
Sai dai masu zuwa hadda suci gaba da zuwa."
Cike da gamsuwa M Jamil yace to.
Kana sukayi sallama.
Dai-dai lokacin kuma su Khausar suka shiga cikin makarantar,
Da in ka gani kace a ƙasashen ƙetarene, domin makaranta ce mai zaman kanta, mai cike da haziƙan malamai, duk da sunyi makarar mintuna 20, an bar motarsu ta shiga ne, sabida magiyar da sukayi tayi da kuma girman gidan da suka fito, da bada uzurin motar ta ɗan lalacemusu a hanyane kana da kuma ganin ma yau ba karatun za'ayi ba, hutun za'a kuma ruɓanyawa.
Suna shiga kuwa, ga mamaki su aka barsu suka shige ba hukuncin komai.
Kana ko wa ya nufi sashin da ajinsa yake.
Da sauri duk suka tsaya jin Malam Habibullah na cewa.
“Fattanah uwar yan letti yau makarar har ta 20 minute duk da yau aka dawo, duk kuyi sama ana taro a hall”.
Cikin ɗan tura baki tace.
“Toh Malam”.
Yayinda tuni su Asiya kam sun haura har sun shiga hall ɗin.
Da ɗan sassarfa ta fara take steps ɗin da zai sasanta, da hall da yake a sama ganin ita kaɗai ta rage.
Daga corridor'n steps ɗin, ta ɗan lumshe idanu ta, tare da gyara saƙala school bag ɗinta a kafaɗar dama.
Sabida ƙamshin turarensa ya shaida mata, tabbas tuni ya shiga hall ɗin.
Amina ce ƙanwar Asiya mai binta ta kalli Ramadan dake cewa.
“Kalli fa 8:13 na tabbatar yauma zamu zanu”.
Cikin sanyi tace.
“Mu dai Allah ya rufa mana asiri daga SS 2 akwai matan aure da yawa a ciki, so ba batun duka a side ɗin mu.
Kuma ma duk bama saɓa doka cikin nitsuwa da tarbiyyar mu muke, ko nayi litting nasan za'ayi min uzuri.
Cike da jin daɗi, Khausar tace.
“Nima dai Allah ya yaye min masifa da cin zalin su Moddibo tunda yau dai zan tafi Ss 1 ɗin, da ba duka ba zagi, wlh inci karena babu babbaka”.
Taɓe baki Haydar yayi tare da cewa.
“Mu gefen maza, babu manya, duk yarane, manyan da dare suke zuwa, shiyasa babu roggomi”.
Asiya ce ta kalli Khausar cikin yanayin son yarinyar tare da cewa.
“Ai wlh ke dai in baki nitsuwa ba ko jami'a kikaje in dai Moddibo na cikin malamanku, na tabbatar zai san matakin da zai ɗauka a kanki.
Sannan ma da kike batun kin tafi Ss1 akwai matan aure, kin mance cewa, na safene, na islami.
Akwai na rana zuwa biyar bokone, kuma kuna tare da moddibo.”
Kwaffa tayi tare da cewa.
“Kai na shiga ukuna wlh”..
Anan gefen su Modibbo ku, fir innayi taki aje asibitin. Su kuna su kasa fahimtar ta, gani suke zafin zazzaɓin maleria ne yake son sata surutai shiyasa suke hanata mgn sukayi ta mata addu'o'i hardai ta ɗan fara samun nitsuwa har bacci ya ɗan sureta.
Gani ta ɗan rumtsane yasa suka tafi wurin Ummin M Jameel suka ɗauko Ummin dan tazo ta ɗan kula da ita.
Suna isa bakin gate, ba tare da sun shigaba, Ummin ta kalli M Jamil da yayi saurin fitowa bayan yayi parking marfin motar ya buɗe, mata cikin tsananin son mahaifiyar tasa, yace.
“Bismillah Ummi fito ki shiga wurin Innayinki, domin mu dai yau mun gaza gane kanta, da alamun Ita dai dare ɗaya gigin tsufa ya sauƙo mata”.
Ɗan buge ƙeyarsa tayi tare da ciwa.
“Tsufa kan zai cimma taka uwar mafa, kawai dai inaga zafin zazzaɓine kusan wasu lokutan yanasa yara surutai, to ita kuma girma yazo dole in ciwon yayi zafi zatayi kamar na yara”.
Juyowa tayi ta kalli Moddibo daya jingina kansa jikin kujerar gaban motar gefen mai zaman banza,
Cikin sanyin murya yace.
“Uhmmmm Ummi waifa cewa tai taga taurari suna sauƙowa ƙasa har kamar zasu taɓa rufin side nan, anya kuwa Ummi wannan zazzaɓi ne?”.
Sai kuma ya ɗan fesar da numfashi tare da lumshe idanunsa cikin alamun nazari yace.
“Ina tsoron kada fa matsalar ƙwaƙwalwa ce, nayi nayi muje asibiti kuma taƙi.”
Ya dire mgn tare haɗa kan yatsun hannunsa.
Jamil ne yaci gaba da cewa.
“Saida fa Moddibo yayi ta mata tofi kafin muka samu tayi bacci har muka fito ɗin.”
Cikin kulawa Ummi tace.
“In sha Allah babu komai, bari in shiga, ku kuje”.
To Jamil yace kana ya shiga mota, ita kuma tayi cikin gidan.
A hankali ya miƙa dalleliyar motarsa ƙirar BMW kan shimfiɗeɗen titin,
Yana tafiyar hawainiya, murmushin yayi ganin kallon da Moddibo yake masa.
“Sanin yau za'a dawo makaranta ne, yasa nayi ƙoƙarin dawowa baro Marrocco, duk da akwai ayyukan da ban gama dasu a company'nba,”.
Cewar M Jamil shi kuwa Moddibo kai ya jinjina alamun yana jinsa, shi kuwa M Jamil gudu ya ɗan ƙara tare da ci gaba da mgn dan yasan ba lallai ne Moddibo ya amsa mishi da bakiba, inda sabo ya saba, kuma shi yasan cewa body language al'adane ko ɗabi'a koma yace halittar Moddibo ne.
Juyowa yayi ya kalleshi tare da cewa.
“Na zaƙu muje makarantar nan, dan nasan zaiyi kyau sosai a tsarin gyarashi da akayi”.
Cikin ɗan ƙwaɓe fuska yace.
“In an gama gyaran ba”.
Da sauri M Jamil yace.
“Kamar yaya za'a gama mana”.
Juyowa yayi ya ɗan kalli M Jamil ta gefen ido kana a takaice yace.
“Toh ba'a gaman ba”.
Cikin sauri M Jamil yace.
“A.S da gaske ba'a gama ba?”.
A.S shine sunan da yake kiran Moddibo dashi kuma su biyu kaɗai suka san ma'anar sai kuma abokan karatunsu.
Shi kuwa Modibbo littafin dake gaban motar ya ɗauka tare da buɗe wa kana yace.
“Dama tun lokacin da za'a bada hutun na faɗa bazai isa a gama gyaran school ɗin ba, musamman da ya zama an ƙara yawan class, kana ga gina hall din da akace za'ayi, kuma dole aikin bazaiyi guduba sabida Ramadan, tun lokacin nace a ƙara kwanakin hutun, sabida samun isasshen lokacin, wannan Ba fulatanin yaƙi”.
Murmushin M Jamil yayi tare da cewa.
“Toh kai meyasa baka ƙara hutunba, ai da sai ka sanar”.
Juyowa yayi ya kalleshi bayan hannunsa yasa ya shafa tattausan sajensa tare da cewa.
“Uhmmmm”.
Ya san me wannan Uhmmm ɗin take nufi, kai ya jinjina tare da cewa, “Mu dai yan kallone,".
Da sauri yace.
“Nima haka, dan na gaji ko yaushe sai ya kwaɓa abu yazo yana cemin ina mafita”.
Dai-dai lokacin aka buɗe musu gate din makarantar, Ya Salam.
Wani irin tsarine da zubi makarantar yake dashi, tsari mai burgewa, yayinda shima makarantar Moddibo ya ƙawatata da tsirrai na kyautata muhalli.
Tabbas gyara kam da saura ba'a gama shi ba.
Domin daga woje dai kam an kammala komai amman daga ciki, duk cikin ajujuwan a hargitse yake.
M Jamil nayin parking, wani kekkyawan dattijo bafulatani ya nufo matar tasu da sauri, bisa alamu dai shine shugaban makarantar domin duk malaman na miƙa gaisuwar garesa cikin mutuntawa.
“Moddibo! Moddibo!! Moddibo!!!.”
Jamil ne ya fito yana murmushin tare da cewa.
“Allah rene,”.
Da sauri yace.
“Ina Moddibo”.
Cikin motar Jamil ya nuna masa, da sauri ya sunkuyo,
Yayinda shi kuwa Moddibo meda bayansa yayi ya jingina tare da lumshe idanunsa, murmushi Dattijon yayi tare da cewa.
“Ga ɗalibai duk sun dawo makaranta ta cika maƙil ga sabbin ɗauka, kuma aiki baifi rabi ba, ya zamuyi?”.
Cikin taɓe baki yace.
“Allahu a'lamu!”.
Jamil ne ya juyo ya kalli Malam Ahmad da Malam Habibullah da suma fitowar su kenan daga can cikin makarantar.
Shi kuwa Malam Arɗo Umaru mamallakin makarantar kuma .
Kai ya ɗan dafe tare da cewa.
“Dan Allah ka fito Moddibo kasan bayanin da zakayi musu, kana ka kara musu kwanakin hutun, tsawon lokacin da kakega za'a iya gama gyaran”.
Yadda ya dire mgnar da karya wuyane yasa Moddibo fitowa.
Murmushin sauran malaman sukayi, domin sosai tsufa ya fara cimma Mala Arɗo, zuwa yanzu ya kamata ragamar makarantar ya zama a hannun yara, domin badon Allah yasa Moddibo ke tsara komai na jadawalin abubuwan ciki da wajen makarantar ba, da tuni ta durƙushe, to amman sabida shi da sauran haziƙan malamai da suke da tsananin kula da tarbiyyar yara da sukeyi yasa har yau makarantar bata da na biyu a faɗin birnin Gembila.
Kusan a tare suka rakaya cikin makarantar.
Yayinda hayanin ɗalibai manya da yara maza da mata, ke tashi.
Juyowa yayi ya kalli Jamil tare da cewa.
“J kaje masallaci kayi mgn duk mu su haɗu a tsohon halla ɗin mu na sama.”.
To Jamil yace yana tunanin to me zaice musu,
Masallacin ya wuce tare da yin sanarwan.
Nan take kuwa, duk ɗaliban suka haura sama, suka shiga cikin babban hall ɗin nasu wanda yake ƙato sai dai duk da haka yanzu ya musu ƙaramin,.
A gafen mazama suma duk sun haɗu a halla nasu.
Shi kuwa Moddibo office nasa ya wuce.
Jim kaɗan ya fito, da Lapel Microphone a hannunsa yana saƙalasa a wuyan tattausan jallabiyar jikinsa Malam Ahmad ne ya matso kusa dashi tare da cewa.
“Zamu jirane ko an ƙara mana hutu”.
Ɗan murmushin gefen baki yayi tare da cewa.
“Hutu kuwa sosai ma har na tsawon mako uku za'a ƙara”.
Cike da murmushi yace.
“Mu tafi kenan”.
Kai ya gyaɗa masa tare da cewa.
“Suma duk yanzu zan kaɗa kansu ko wacce tai gida sai dai muma muna da zama na musamman”.
Ai kuwa jin haka yasa duk malam suka zauna jiran.
Shi kuwa ya haura saman yana mgn da M Jamil a waya.
“Su maza basu da hayaniya, kawai J ka ɗanyi musu nasiha, kana kace sai bayan mako uku zasu dawo kafin nan an gama gyara,
Sai dai masu zuwa hadda suci gaba da zuwa."
Cike da gamsuwa M Jamil yace to.
Kana sukayi sallama.
Dai-dai lokacin kuma su Khausar suka shiga cikin makarantar,
Da in ka gani kace a ƙasashen ƙetarene, domin makaranta ce mai zaman kanta, mai cike da haziƙan malamai, duk da sunyi makarar mintuna 20, an bar motarsu ta shiga ne, sabida magiyar da sukayi tayi da kuma girman gidan da suka fito, da bada uzurin motar ta ɗan lalacemusu a hanyane kana da kuma ganin ma yau ba karatun za'ayi ba, hutun za'a kuma ruɓanyawa.
Suna shiga kuwa, ga mamaki su aka barsu suka shige ba hukuncin komai.
Kana ko wa ya nufi sashin da ajinsa yake.
Da sauri duk suka tsaya jin Malam Habibullah na cewa.
“Fattanah uwar yan letti yau makarar har ta 20 minute duk da yau aka dawo, duk kuyi sama ana taro a hall”.
Cikin ɗan tura baki tace.
“Toh Malam”.
Yayinda tuni su Asiya kam sun haura har sun shiga hall ɗin.
Da ɗan sassarfa ta fara take steps ɗin da zai sasanta, da hall da yake a sama ganin ita kaɗai ta rage.
Daga corridor'n steps ɗin, ta ɗan lumshe idanu ta, tare da gyara saƙala school bag ɗinta a kafaɗar dama.
Sabida ƙamshin turarensa ya shaida mata, tabbas tuni ya shiga hall ɗin.