Sashe 19
Sakayyah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kai Dije ta gyaɗa tace.
“Lalle kam da alama shi ya tare”.
Ta dubi Sadik dake tsintar ƙwai tace.
“Muje inga wajen”.
Kai ya gyaɗa sannan yashiga gaba ita da Dije na biye dashi ta cikin wata siririyar hanya Sadik na cigaba da tsintar ƙwo'yin suna fita asirin hanyar Khausar ta hango wani ƙaton bishiyar ɗaurawa dake ɗauke da rassan bishiya masu taren yawa saura daga sama saura kuma sun zuba yayin da ƙasansa bishiyar duwatsu ne baƙaƙe masu sheƙi ke zube wanda suke kamar kujeru.
Juyawa tayi ta maida Idanunta kan dandazon mutanen dake wajen mafi yawa Matasane sai kuma Dattijai tana ɗaga kanta sama ta hango Baffa Jauro yana waya.
Dariya ta ƙyalƙyale dashi tace.
“Baka tsoron ka faɗo ko tsohon nan?".
Dije ce ta ɗan bigi ƙeyarta tare da yi mata hararan wasa tace.
“Baban nawa ne tsoho?”.
Murmushi Khausar tayi tace.
“Toh baya tsoro ne kiga ya hau kan bishiya ya ɗane kamar birin can”.
Tsayuwa Dije ta gyara tare da mata hararar wasa tace.
“Ai shikam dole seya zo nan yayi waya tunda shine Jauron garin nan akwai ɓuƙatar magana da Jauro da sauran Jaurorin garirruwa”.
Khausar kuwa kai ta gyaɗa tace.
“Ikon Allah lalle de kam irin wannan gari haka”.
Tayi maganar tana kallon matasan dake sanye da kayan Fulani kowa na amsa wayar, Idanunta ne suka sauƙa akan wata tsohuwa dake waya.
Ta maida kallonta kan Dije tace.
“Wannan kuma fa?”.
Dije tace.
“Tafff!, Wannan ƙawar Hajja Nana ce”.
Kallonta Khausar ta sake yi tace.
“Ƙawar Masifa de zaki ce”.
Sadik dake gyara kwandon ƙwai yace.
“Ki bari fa”.
Ta kallesa da manyan Idanunta dake lumshe tace.
“Ai da gskene Hajja Nana in ba masifa ba meta iya!?”.
Duk mutanen wajen juyawa sukayi tare da zuba mata idanu jin tana kiran Hajja Nana Masifa,Wasu daga cikin mutanen ne suka ce Dije ina kika samu wannan yarinyar.
Dije kuwa tayi murmushi tace.
“ 'Yar Baffa Usmanu ne”.
Jin Abinda Dije tace yasa sauran mutane dake saman bishiyar kashe wayansu suka sauƙo.
Wani kyakkyawan Matashi fari ne ya nufosu kallo ɗaya zaka masa kasan akwai wayewa atare dashi yace.
“Wannan itace 'yar Baffa Usmanu itace ƙanwar Nenne ko Masha Allah?”.
Kai Dije ta gyaɗa tare da nunawa Khausar matashin tace.
“Kinga wannan?”.
Kai Khausar ta gyaɗa.
Dije tace.
“Yaron Baffa Liman ne acikin Birni yake karatun sa”.
Murmushi Khausar tayi tace.
“Ayyah Allah Sarki yayi kyau".
Ya dubi Khausar da murmushi afuskarsa yace.
“Hi Sister how are you?”.
Ta mayar masa da martanin Murmushin tace.
“Am fine how's everyone?”.
“Fine Long time?".
“Thank God”.
Dije ta wani ɓata fuska Idanunta akan Khausar tace.
“Kuyi magana da yaren da zanji”.
Murmushi Khausar tayi tace.
“Ba wani magana muka yiba kawai gaisawa ne fa”.
“Toh”.
Dije tace sai kuma ta maida kallonta kan Matashin saurayin tace.
“Ayyah Yaya Abba nima ka koya min turancin”.
Murmushi yayi yace.
“Ba matsala zan koya miki Kinga ga wata ma zata koya miki”.
Hira suka cigaba dayi yayin da Sadik ya cigaba da tsintar ƙwoyaye wasu ma da yawa nata tsintar ƙwoyin ko wannensu da alama akwai inda ƙwan Zabbinsa ke tsayawa akwai waya da ake sakawa atsakanin waje-jen...
Baffa Jauro daya gama waya ya sauƙo tare da zuwa inda Khausar take ya riƙe hannunta suka fara tafiya sai kuma ya fara matsa hannun, Janye hannun tayi tace.
“Wallahi tsohon nan ka iya mugunta inka riƙe hannun mutum kaita matsewa da faratu ni banaso”.
Murmushi Baffa Jauro yayi tare da sake matse hannun!.
Ashagwaɓe tace.
“Wayyo na tuba ka sake”.
Sake mata hannun yayi yana dariya yace.
“Ohhh in dai baki daina yiwa Adda Nana rashin jiba, toh fa hakan zanyi ta matse mata ke, ga jiki ba ƙwari ba'ason wahala”.
Sai kuma ya juya ya dubi Dije yace.
“Dije”.
“Na'am Baba”.
Yace.
“Kishirya Gobe idan Allah ya kaimu da sassafe zaki ɗauke ta kuje kuyi tsar Nono tare”.
Kai Dije ta gyaɗa kana tace.
“Insha Allah zan ɗauke ta muje tare”.
Kallonsa Khausar tayi still hannunta na cikin nasa tace.
“Nide inda wuya bazan yiba”.
Dije tace.
“Ba wuya ai zamu baki man shanu ki shafawa yatsunki yanda zai yi santsi.
Kai ta gyaɗa tace.
“Toh shikenan ba damuwa zanje”.
Kallon Dije Sadik yayi tare da bata kwandon Ƙwan Zabbin yace.
“Ki tafi dashi".
Sannan ya juya ya cigaba da tafiya.
“Khausar kuwa murya ta ɗan ɗaga tace.
“Kaifa baza ka bimu bane”.
Girgiza Kai yayi yace.
“A'a ban ƙarasa ɗiba ba”.
Kai ta gyaɗa tace.
“Toh inde kazo ka kawo min nawa”.
“Toh”,Yace sannan suka juya suka tafi.
Suna shiga rugar suka nufi hanyar gidan Hajja Nana kasancewar duk gidan da zaka je seka wuce ta ƙofanta,sannan duk lokacin da taji motsi seta tambaya waye.
Sallama Dija tayi cikin ladani kana suka shiga, Hajja Nana dake cikin uwar ɗaka tace.
“Waye”.
Cike da ladabi Dije tace.
“Dije ce".
Haɓa Khausar ta riƙe tare da cewa.
“Ikon Allah duk mai wucewa saita tambayesa waye sai kace wata Traffick light?”.
Ƙasa da murya Dije tayi tace.
“Aaa ki bari Khausar kiyi ahankali kar taji”.
Khausar kuwa baki ta taɓe tace.
“Ai wannan abu yayi yawa wannan mulkin mallaka haka ake yi muku agarin nan”.
Daga ciki Hajja Nana tace.
“Dije keda waye naji kamar ana magana ƙasa-ƙasa?”.
Dije tace.
“Nida Khausar ce zamuje gida kai saƙo ne ƙwoyi muka kawo”.
Ita kuwa Hajja Nana cewa tayi.
“Toh shikenan”.
Ajiyar zuciya Dije ta sauƙe sannan suka fice.
Lokacin da suka fita makiyaya sun fara dawowa daga kiwo sannan sanyin magriba na sake sauƙa sanyin ya fara yawa ahaka suka isa gidansu Dije Khausar sai lumahe ido take.
Suna isa suka ajiye Ƙwoyin.
Dije na ƙoƙarin shiga ɗaki Khausar da Idanunta suka sake lumshewa tace.
“Dije muje ki rakani ɗaukan Sweater na sanyi nake ji sosai”.
Kai Dije ta gyaɗa sannan suka fice kallon garin Khausar tayi ko ina baƙi ba alamar hasken wutar lantarki ta dubi Khausar tace.
“Wai kam garin nan baku da wuta ne?,tun da nazo banga ƙyallin wuta ko sau ɗaya ba?”.
Kai Khausar ta gyaɗa tace.
“Eh babu amma ana tada Generator”.
Khausar kuwa hankalin tane ya tashi jin babu wuta garin!.
Ganin yanda tayi yasa Dije sakin murmushi tace.
“Kada ki damu kinga Yaya Abba shike tada Generator sannan yake sa kawa mutane Caji kuma aƙofar gidan Hajja Generator yake akwai ɗan haske kaɗan koda ba farin wata, bare kuma in akwai farin wata rana zakiga garin”.
Sai asannan Khausar ta ɗan saki ajiyar zuciya dan Allah ya sani tana tsoron duhu.
Bakinsu ɗauke da sallama suka shiga gidan shigarsu yayi dai-dai da kiran Sallar Magriba da akayi.
A tsakar gida suka samu Hajja Nana na alwala, kallonsu tayi tace.
“Kuzo kuyi alwala kuyi Sallah”.
Kallon ta Khausar tayi tace.
“Ni gaskiya sanyi nake ji yanzu ma rigar sanyi na nazo ɗauko kuma asamar min ruwan zafi dashi zanyi alwala”.
Harara Hajja Nana ta watsa mata kafin tace.
“Wa zai samar miki ruwan zafi?,Kina yarinya ƙarama yau har wani sanyi kirki akeyi! da har zaki nemi ruwan zafi”.
Bakinta ta tura amma ba tace komaiba.
Dije ce tace.
“Muje gidanmu akwai ruwan zafi sai kiyi acan”.
Kai Khausar ta gyaɗa da faɗin.
“Toh shikenan”
Sannan tashiga ɗakin Hajja Nana kasancewar akwai hasken lanta da aka kunna inda trolley ta yake ta nufa ta buɗe tare da ɗaukar Sweater ta sannan ta rufe trolley juyawar da za tayi Idanunta suka sauƙa akan kuliya (Mage) dake kwance akan ɗaya daga cikin gadon Hajja Nana kasancewar gado biyu ne aɗakin sai kuma ɗan shirge-shigen ta na Tsoffin ruga.
Cikin matsananci tashin hankali da ruɗu mara misaltuwa daya bayyana afuskarta take faɗin.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n!!,Hasbunallahu!!!, wani'imal wakin Astagfirullah wa'atubu ilaik!!!”.
Aruɗe Dije ta shiga ɗakin tana cewa.
“Lafiya Khausar meye faru?”.
Aruɗe Khausar ke yarfe hannunta takamar wacce ta ƙone duk jikinta na rawa takasa furta komai numfashinta na wani irin fusga na tsananin tsoro da tashin hankali, da ƙyar ta iya furta.
“Kuliya”.
Sai asannan Dije ta lura da kuliyar da har zuwa lokacin ke kwance akan gadon Hajja Nana.
Ita kuwa Hajja Nana wani dogon numfashi taja.
Dan da kusan mutuwar zaune tayi dan jin irin karajin da Khausar ɗin tayi.
Ita kuwa Dija hannu tasa tashiga koran kuliyar.
Daga can waje Hajja Nana ke cewa.
“Kuliyar take wa wannan Ihun? zata kasheni tun kwanana bai ƙareba”.
Ina ita kam Khausar bata san sunayi ba, har zuwa yanzu tsalle takeyi a tsakiyar ɗakin tana yarfa hannunta tare da furta duk addu'ar da tazo bakin, istagfari takeyi ba ƙaƙƙautawa.
A gigice Dije ta fitar da kuliyar tana mai cewa.
“Khausar ki nitsu ya fita, na koreshi, kuliyar Goggo Hajja cefa.
Cikin tsananin tsoro da rawar jiki cike da gigita,
Ta fito cikin ɗakin Hajja Nana ta nufi gidan Baffa Jauro tana cigaba da faɗin.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n
Ya Allah na tuba ka yafe min”.
Yayin da gaba ɗaya ilahirin jikinta ke rawa na tsananin tsoratan da tayi.
Jin shiganta Aruɗe yasa Goggo Nanne fitowa daga ɗaki wato Mahaifiyar Dije.
Matsawa kusa da Khausar tayi ta riƙe Hannunta tace.
“Lafiya”.
Asanyaye Dije tace.
“Kuliya take tsoro taga kuliyar Goggo
Hajjs ce take haka”.
Cike da tausayinta Goggo Nanne tace.
“Ayyah Subhanallah ki kwantar da hankalinki nan babu kuliya kar ki damu Khausar ki kwantar da hankalinki ki nutsu kinji?”.
Kasa furta komai Khausar tayi sai Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n da take yi aƙasan ranta.
Addu'a Goggo Nanne tashiga tofa mata kafin ta samu hankalinta ya dawo jikinta.
Jauro daya fito daga banɗaki yana alwala yace.
“Yau kuliya ce haka kamar wanda taga kura haka?”.
Ya faɗa yana kallon yanda tsananin razana ya bayyana afuskarta.
Juyawa yayi yana kallon Goggo Nanne yace.
“Lalle wannan baƙunta akwai saɓani a cikinsa. Ita Addah Hajja ba zata iya rayuwa babu kuliya ba ita kuma wannan ga tsoron kuliya”.
Tana sakin ajiyar zuciya tace.
“Nide bazan sake shiga ɗakinta ba shegen ɗaki ga tarukuce ga duhu sannan ga kuliya wannan ɗakin har macizai za asamu acikinsa bazan sake shiga ɗakinta ba”.
“Lalle kam da alama shi ya tare”.
Ta dubi Sadik dake tsintar ƙwai tace.
“Muje inga wajen”.
Kai ya gyaɗa sannan yashiga gaba ita da Dije na biye dashi ta cikin wata siririyar hanya Sadik na cigaba da tsintar ƙwo'yin suna fita asirin hanyar Khausar ta hango wani ƙaton bishiyar ɗaurawa dake ɗauke da rassan bishiya masu taren yawa saura daga sama saura kuma sun zuba yayin da ƙasansa bishiyar duwatsu ne baƙaƙe masu sheƙi ke zube wanda suke kamar kujeru.
Juyawa tayi ta maida Idanunta kan dandazon mutanen dake wajen mafi yawa Matasane sai kuma Dattijai tana ɗaga kanta sama ta hango Baffa Jauro yana waya.
Dariya ta ƙyalƙyale dashi tace.
“Baka tsoron ka faɗo ko tsohon nan?".
Dije ce ta ɗan bigi ƙeyarta tare da yi mata hararan wasa tace.
“Baban nawa ne tsoho?”.
Murmushi Khausar tayi tace.
“Toh baya tsoro ne kiga ya hau kan bishiya ya ɗane kamar birin can”.
Tsayuwa Dije ta gyara tare da mata hararar wasa tace.
“Ai shikam dole seya zo nan yayi waya tunda shine Jauron garin nan akwai ɓuƙatar magana da Jauro da sauran Jaurorin garirruwa”.
Khausar kuwa kai ta gyaɗa tace.
“Ikon Allah lalle de kam irin wannan gari haka”.
Tayi maganar tana kallon matasan dake sanye da kayan Fulani kowa na amsa wayar, Idanunta ne suka sauƙa akan wata tsohuwa dake waya.
Ta maida kallonta kan Dije tace.
“Wannan kuma fa?”.
Dije tace.
“Tafff!, Wannan ƙawar Hajja Nana ce”.
Kallonta Khausar ta sake yi tace.
“Ƙawar Masifa de zaki ce”.
Sadik dake gyara kwandon ƙwai yace.
“Ki bari fa”.
Ta kallesa da manyan Idanunta dake lumshe tace.
“Ai da gskene Hajja Nana in ba masifa ba meta iya!?”.
Duk mutanen wajen juyawa sukayi tare da zuba mata idanu jin tana kiran Hajja Nana Masifa,Wasu daga cikin mutanen ne suka ce Dije ina kika samu wannan yarinyar.
Dije kuwa tayi murmushi tace.
“ 'Yar Baffa Usmanu ne”.
Jin Abinda Dije tace yasa sauran mutane dake saman bishiyar kashe wayansu suka sauƙo.
Wani kyakkyawan Matashi fari ne ya nufosu kallo ɗaya zaka masa kasan akwai wayewa atare dashi yace.
“Wannan itace 'yar Baffa Usmanu itace ƙanwar Nenne ko Masha Allah?”.
Kai Dije ta gyaɗa tare da nunawa Khausar matashin tace.
“Kinga wannan?”.
Kai Khausar ta gyaɗa.
Dije tace.
“Yaron Baffa Liman ne acikin Birni yake karatun sa”.
Murmushi Khausar tayi tace.
“Ayyah Allah Sarki yayi kyau".
Ya dubi Khausar da murmushi afuskarsa yace.
“Hi Sister how are you?”.
Ta mayar masa da martanin Murmushin tace.
“Am fine how's everyone?”.
“Fine Long time?".
“Thank God”.
Dije ta wani ɓata fuska Idanunta akan Khausar tace.
“Kuyi magana da yaren da zanji”.
Murmushi Khausar tayi tace.
“Ba wani magana muka yiba kawai gaisawa ne fa”.
“Toh”.
Dije tace sai kuma ta maida kallonta kan Matashin saurayin tace.
“Ayyah Yaya Abba nima ka koya min turancin”.
Murmushi yayi yace.
“Ba matsala zan koya miki Kinga ga wata ma zata koya miki”.
Hira suka cigaba dayi yayin da Sadik ya cigaba da tsintar ƙwoyaye wasu ma da yawa nata tsintar ƙwoyin ko wannensu da alama akwai inda ƙwan Zabbinsa ke tsayawa akwai waya da ake sakawa atsakanin waje-jen...
Baffa Jauro daya gama waya ya sauƙo tare da zuwa inda Khausar take ya riƙe hannunta suka fara tafiya sai kuma ya fara matsa hannun, Janye hannun tayi tace.
“Wallahi tsohon nan ka iya mugunta inka riƙe hannun mutum kaita matsewa da faratu ni banaso”.
Murmushi Baffa Jauro yayi tare da sake matse hannun!.
Ashagwaɓe tace.
“Wayyo na tuba ka sake”.
Sake mata hannun yayi yana dariya yace.
“Ohhh in dai baki daina yiwa Adda Nana rashin jiba, toh fa hakan zanyi ta matse mata ke, ga jiki ba ƙwari ba'ason wahala”.
Sai kuma ya juya ya dubi Dije yace.
“Dije”.
“Na'am Baba”.
Yace.
“Kishirya Gobe idan Allah ya kaimu da sassafe zaki ɗauke ta kuje kuyi tsar Nono tare”.
Kai Dije ta gyaɗa kana tace.
“Insha Allah zan ɗauke ta muje tare”.
Kallonsa Khausar tayi still hannunta na cikin nasa tace.
“Nide inda wuya bazan yiba”.
Dije tace.
“Ba wuya ai zamu baki man shanu ki shafawa yatsunki yanda zai yi santsi.
Kai ta gyaɗa tace.
“Toh shikenan ba damuwa zanje”.
Kallon Dije Sadik yayi tare da bata kwandon Ƙwan Zabbin yace.
“Ki tafi dashi".
Sannan ya juya ya cigaba da tafiya.
“Khausar kuwa murya ta ɗan ɗaga tace.
“Kaifa baza ka bimu bane”.
Girgiza Kai yayi yace.
“A'a ban ƙarasa ɗiba ba”.
Kai ta gyaɗa tace.
“Toh inde kazo ka kawo min nawa”.
“Toh”,Yace sannan suka juya suka tafi.
Suna shiga rugar suka nufi hanyar gidan Hajja Nana kasancewar duk gidan da zaka je seka wuce ta ƙofanta,sannan duk lokacin da taji motsi seta tambaya waye.
Sallama Dija tayi cikin ladani kana suka shiga, Hajja Nana dake cikin uwar ɗaka tace.
“Waye”.
Cike da ladabi Dije tace.
“Dije ce".
Haɓa Khausar ta riƙe tare da cewa.
“Ikon Allah duk mai wucewa saita tambayesa waye sai kace wata Traffick light?”.
Ƙasa da murya Dije tayi tace.
“Aaa ki bari Khausar kiyi ahankali kar taji”.
Khausar kuwa baki ta taɓe tace.
“Ai wannan abu yayi yawa wannan mulkin mallaka haka ake yi muku agarin nan”.
Daga ciki Hajja Nana tace.
“Dije keda waye naji kamar ana magana ƙasa-ƙasa?”.
Dije tace.
“Nida Khausar ce zamuje gida kai saƙo ne ƙwoyi muka kawo”.
Ita kuwa Hajja Nana cewa tayi.
“Toh shikenan”.
Ajiyar zuciya Dije ta sauƙe sannan suka fice.
Lokacin da suka fita makiyaya sun fara dawowa daga kiwo sannan sanyin magriba na sake sauƙa sanyin ya fara yawa ahaka suka isa gidansu Dije Khausar sai lumahe ido take.
Suna isa suka ajiye Ƙwoyin.
Dije na ƙoƙarin shiga ɗaki Khausar da Idanunta suka sake lumshewa tace.
“Dije muje ki rakani ɗaukan Sweater na sanyi nake ji sosai”.
Kai Dije ta gyaɗa sannan suka fice kallon garin Khausar tayi ko ina baƙi ba alamar hasken wutar lantarki ta dubi Khausar tace.
“Wai kam garin nan baku da wuta ne?,tun da nazo banga ƙyallin wuta ko sau ɗaya ba?”.
Kai Khausar ta gyaɗa tace.
“Eh babu amma ana tada Generator”.
Khausar kuwa hankalin tane ya tashi jin babu wuta garin!.
Ganin yanda tayi yasa Dije sakin murmushi tace.
“Kada ki damu kinga Yaya Abba shike tada Generator sannan yake sa kawa mutane Caji kuma aƙofar gidan Hajja Generator yake akwai ɗan haske kaɗan koda ba farin wata, bare kuma in akwai farin wata rana zakiga garin”.
Sai asannan Khausar ta ɗan saki ajiyar zuciya dan Allah ya sani tana tsoron duhu.
Bakinsu ɗauke da sallama suka shiga gidan shigarsu yayi dai-dai da kiran Sallar Magriba da akayi.
A tsakar gida suka samu Hajja Nana na alwala, kallonsu tayi tace.
“Kuzo kuyi alwala kuyi Sallah”.
Kallon ta Khausar tayi tace.
“Ni gaskiya sanyi nake ji yanzu ma rigar sanyi na nazo ɗauko kuma asamar min ruwan zafi dashi zanyi alwala”.
Harara Hajja Nana ta watsa mata kafin tace.
“Wa zai samar miki ruwan zafi?,Kina yarinya ƙarama yau har wani sanyi kirki akeyi! da har zaki nemi ruwan zafi”.
Bakinta ta tura amma ba tace komaiba.
Dije ce tace.
“Muje gidanmu akwai ruwan zafi sai kiyi acan”.
Kai Khausar ta gyaɗa da faɗin.
“Toh shikenan”
Sannan tashiga ɗakin Hajja Nana kasancewar akwai hasken lanta da aka kunna inda trolley ta yake ta nufa ta buɗe tare da ɗaukar Sweater ta sannan ta rufe trolley juyawar da za tayi Idanunta suka sauƙa akan kuliya (Mage) dake kwance akan ɗaya daga cikin gadon Hajja Nana kasancewar gado biyu ne aɗakin sai kuma ɗan shirge-shigen ta na Tsoffin ruga.
Cikin matsananci tashin hankali da ruɗu mara misaltuwa daya bayyana afuskarta take faɗin.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n!!,Hasbunallahu!!!, wani'imal wakin Astagfirullah wa'atubu ilaik!!!”.
Aruɗe Dije ta shiga ɗakin tana cewa.
“Lafiya Khausar meye faru?”.
Aruɗe Khausar ke yarfe hannunta takamar wacce ta ƙone duk jikinta na rawa takasa furta komai numfashinta na wani irin fusga na tsananin tsoro da tashin hankali, da ƙyar ta iya furta.
“Kuliya”.
Sai asannan Dije ta lura da kuliyar da har zuwa lokacin ke kwance akan gadon Hajja Nana.
Ita kuwa Hajja Nana wani dogon numfashi taja.
Dan da kusan mutuwar zaune tayi dan jin irin karajin da Khausar ɗin tayi.
Ita kuwa Dija hannu tasa tashiga koran kuliyar.
Daga can waje Hajja Nana ke cewa.
“Kuliyar take wa wannan Ihun? zata kasheni tun kwanana bai ƙareba”.
Ina ita kam Khausar bata san sunayi ba, har zuwa yanzu tsalle takeyi a tsakiyar ɗakin tana yarfa hannunta tare da furta duk addu'ar da tazo bakin, istagfari takeyi ba ƙaƙƙautawa.
A gigice Dije ta fitar da kuliyar tana mai cewa.
“Khausar ki nitsu ya fita, na koreshi, kuliyar Goggo Hajja cefa.
Cikin tsananin tsoro da rawar jiki cike da gigita,
Ta fito cikin ɗakin Hajja Nana ta nufi gidan Baffa Jauro tana cigaba da faɗin.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n
Ya Allah na tuba ka yafe min”.
Yayin da gaba ɗaya ilahirin jikinta ke rawa na tsananin tsoratan da tayi.
Jin shiganta Aruɗe yasa Goggo Nanne fitowa daga ɗaki wato Mahaifiyar Dije.
Matsawa kusa da Khausar tayi ta riƙe Hannunta tace.
“Lafiya”.
Asanyaye Dije tace.
“Kuliya take tsoro taga kuliyar Goggo
Hajjs ce take haka”.
Cike da tausayinta Goggo Nanne tace.
“Ayyah Subhanallah ki kwantar da hankalinki nan babu kuliya kar ki damu Khausar ki kwantar da hankalinki ki nutsu kinji?”.
Kasa furta komai Khausar tayi sai Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n da take yi aƙasan ranta.
Addu'a Goggo Nanne tashiga tofa mata kafin ta samu hankalinta ya dawo jikinta.
Jauro daya fito daga banɗaki yana alwala yace.
“Yau kuliya ce haka kamar wanda taga kura haka?”.
Ya faɗa yana kallon yanda tsananin razana ya bayyana afuskarta.
Juyawa yayi yana kallon Goggo Nanne yace.
“Lalle wannan baƙunta akwai saɓani a cikinsa. Ita Addah Hajja ba zata iya rayuwa babu kuliya ba ita kuma wannan ga tsoron kuliya”.
Tana sakin ajiyar zuciya tace.
“Nide bazan sake shiga ɗakinta ba shegen ɗaki ga tarukuce ga duhu sannan ga kuliya wannan ɗakin har macizai za asamu acikinsa bazan sake shiga ɗakinta ba”.