Sashe 44
Sakayyah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Aunty Ruƙayya dake bedroom ta fito fuskarta ɗauke da murmushi tace.
“Khausar kece sannu da zuwa, shigo ciki”.
Da sauri tace.
“A'a Aunty sauri nakeyi ai”.
Cikin kulawa tace.
“Yo yasu Mommy ki?”.
Murmushi Khausar tayi tace.
“Wallahi Aunty Ruƙayya Mommy ce ke asibiti bata da lafiya, shine nace bari nazo na faɗa miki, Ni yanzu ma zan wuce ko za muje tare?”.
Cike da tausayawa Aunty Ruƙayya tace.
“Ayyah Allah ya bata lafiya zanje bari ina zuwa mu tafi tare”.
Kai Khausar ta gyaɗa da faɗin.
“Toh”.
Aunty Ruƙayya kuwa bedroom ta shiga tare kiran mijinta a waya, bayan ya bata izinine, ta ɗauko key mota da mayafinta suka fita,
suka shiga mota,
jingina kai Khausar tayi da jikin motar kalaman Hajiya Bunayya nayi mata suwwa akunne.
Juyawa Aunty Ruƙayya tayi ganin yanda Khausar ta zurfafa cikin tunani yasa tace.
“Ki riƙa yi mata addu'a”.
Kai kawai Khausar ta iya gyaɗa mata.
Cikin Mintuna kaɗan suka isa Asibitin bakinsu ɗauke da Sallama suka shiga ɗakin da aka kwantar da Mommy saboda Hajiya Bunayya ta faɗa mata.
Kwance akan gado suka tarar da ita yayin da Lamiɗo ke gefenta akan kujera hannunsa riƙe da kofin tea yana miƙa mata da faɗin.
“Ki tashi kisha”.
Yana jin Sallamar Khausar ya juya yana kallonta har ta isa kusa dashi.
Cike da kulawa yace.
“Khausar har kun dawo?”.
Kai ta gyaɗa kana tace.
“Eh Abba ya jikin Mommy!?”.
Sai da ya ɗan kalli Mommy dake jingine da pillow sai kuma ya mayar da Kallonsa kan Khausar yace.
“Da sauƙi”.
Sai asannan ya lura da Hajiya Rukayya ya ɗan yi murmushi da faɗin.
“Hajiya Ruƙayya sannu da zuwa”.
Zama tayi akujeran dake kusa da ita tana cewa.
“Yawwa ya Hajiya Aysha da jikin kuma?”.
Ɗan Murmushi yayi kana yace.
“Da sauƙi”.
Tana kallon Mommy tace.
“Ubangiji Allah ya ƙara sauki”.
Ya amsa da.
“Ameen ya hayyu ya ƙayyum”.
Khausar kuwa bakin gadon ta ƙarasa ta riƙe hannun Mommy acikin nata.
Cikin raunin murya tare da tausayawa mahaifiyar tata tace.
“Sannu Mommy ya Jikin?”.
Lumshe idanu Mommy tayi kana ta buɗe su a hankali tace.
“Da sauƙi Khausar bana jin komai in dan ta nice ma, da su sallame ni in koma gida mu kwana tare, dan bana jin ciwon cikin yayi sauƙi babu inda yake min ciwo!”.
Ajiyar zuciya Khausar ta sauƙe tare da faɗin.
“Masha Allah Mommy Allah yaƙara sauƙi Ubangiji ya ƙara tsarewa ya kare”.
A ranta kuwa cewa tace.
Ayyah da ace duk addu'o'in da takeyiwa Mommynta tun randa taci ferfesun da ace tana haɗa addu'ar da yaron cikin wata ƙil da bai zube ba.
Shafa kanta Mommy tayi cike da ƙaunar ta tace.
“Ameen Khausar ki kwantar da hankalin ki ba najin Komai”.
Ta faɗi hakan ganin yanda Khausar tayi zuru-zuru da ita.
Hajiya Ruƙayyance ta kalli Mommy kana tace.
“Hajiya Aysha ya ƙarfin jikin!?”
Murmushi Mommy tayi kana tace.
“Dasauƙi Hajiya Ruƙayya ya ‘Yar taki ya kuma rigima a makaranta!?".
Kallon Khausar Hajiya Ruƙayya tayi kana tace.
“A'a yanzu ai ta daina ta fara girma!”.
Jin haka yasa Khausar tayi murmushi.
Lamiɗo kuwa miƙewa yayi idanunsa akan Mommy yace.
“Toh shikenan bari na tafi dama ganin babu kowa ne yasa nake zaune bari na samu naje nayi wanka dan tunda muka zo ban samu na koma gida ba”.
Hajiya Ruƙayya tace.
“Ayyah ai babu komai Alhaji kaje”.
Jinjina kai Mommy tayi tace.
“Allah ya tsare”.
Ya Amsa da.
“Ameen”sannan ya juya ya fice.
Tafiyar Lamiɗo babu daɗewa Hajiya Bunayya da Hajiya Lami suka zo Raudat na riƙe da hannunta.
Suna shiga Hajiya Bunayya ta zauna daga gefen gadon tare da kallon Mommy tace.
“Sannu ƙanwata ya ƙarfin jikin?”.
Murmushi Mommy tayi kana tace.
“Ai naji sauki Yaya”.
Jinjina kai Hajiya Bunayya tayi cikin yanayin tausayawa tace.
“Allah ya baki lafiya”.
Hajiya Ruƙayya kuwa kallo ɗaya tayi wa Hajiya Bunayya da Hajiya Lami taji sam basu kwanta mata arai ba musanman ma Hajiya Bunayya dake wani shish-shugewa Mommy.
Ta dai daure tace.
“Sannunku da zuwa”.
Hajiya Bunayya da Hajiya Lami suka haɗa baki wajen cewa.
“Yawwa ya mai jikin”.
Ataƙaice Hajiya Ruƙayya tace.
“Da sauƙi”.
Hajiya Lami kuwa jikin gadon ta matasa Idanunta akan Mommy tace.
“Ayyah Sannu Hajiya Aysha Ashe ga abinda ya faru kuma? Amma wannan abu yayi yawa ai gwara Alhj yayi ƙoƙari ya fitar dake waje wannan matsalar ko yaushe da ansamu ciki ya zube ai babu daɗi!”.
Kafin Mommy tayi magana Hajiya Bunayya tayi saurin cewa.
“Kede bari Hajiya Lami abin nan yana damun mu, gaba ɗaya mun kasa gane menene ainihin matsalar, amma hankalinmu na tashi kullum cikin yanayin nan, abin babu daɗi yanzu ciki takwas kenan yana zubewa abin ai babu daɗi!”.
Taɓe baki Khausar da Hajiya Rukayya sukayi alokaci ɗaya.
Ahankali Mommy ta gyara matashin data kishingiɗa akai kana tace.
“Uyummm ya za'ayi da abinda Allah ya tsara, amma ni inaga nin ba wani matsala bane, tun da gashi na haihu bayan haihuwar Haiydar ma haka nata fama da ɓare-ɓaren nan, kuma daga baya da Allah ya kawo Ramadan da Raudat an haifesu ba komai ai”.
Cike da kirsa Hajiya Bunayya tayi yaƙe kana tace.
“Hakane kam, toh Allah ya kawo masu albarka”.
Hajiya Lami kuwa harara ta gallawa Mommy tare da taɓe baki aranta tace shegiya me iyayin jaraba keda haihuwa sai dai kiga anayi.
Idanun Hajiya Ruƙayya da Khausar na kan Hajiya Lami alokacin data taɓe baki ta harari Mommy,
Juyawa Hajiya Ruƙayya tayi ta kalli Khausar tare da jinjina kai itama Khausar kai ta jinjina.
Miƙewa Hajiya Ruƙayya tayi tare da kallon Mommy tace.
“Toh Hajiya Aysha Ubangiji Allah ya ƙara sauki sannan Allah ya tsareki daga sharrin abin ƙi ni zan wuce!”.
A hankali Mommy ta ɗan yunƙura tare da lumshe Idanunta kana tace.
“Ameen ya hayyu ya ƙayyum Hajiya Ruƙayya Nagode”.
Hajiya Lami da Hajiya Bunayya kuwa baki suka saki suna kallon Hajiya Ruƙayya da Mamaki aransu suka ce kaji shegiyar mata da iyayi uban wa takewa wannan addu'ar.
Miƙewa Raudat tayi tare da riƙe hannun Hajiya Ruƙayya tace.
“Aunty Ruƙayya ni zan biki gidanki, Inje in kwana dasu Salman tun da gobe babu makarata”.
Da sauri Khausar ta kalli Raudat dake riƙe da hannun Aunty Ruƙayya tace.
“Ayyah Raudat am baza mu kwana ba?”.
Girgiza kai Raudat tayi tare da langwaɓar da kai kana tace.
“ Ni dai Ina tsoro ni bazan zauna ba”.
Kai Khausar ta gyaɗa da faɗin.
“Shikenan kibi Aunty Ruƙayya”.
Murmushi Aunty Ruƙayya tayi tare da jan hannun Khausar dake cikin nata
Har sun kai ƙofa Hajiya Bunayya ta ƙirƙiri murmushi tana kallon bayan Raudat tace.
“Oohhh Raudat ba zaki bini mu tafi gida ba?”.
Kafaɗa Raudat ta maƙale tace.
“A'a ni zanbi Aunty Ruƙayya”.
Aunyty Ruƙayya kuwa jan hannun Raudat tayi suka fice batare data sake jiran jin Abinda Hajiya Bunayya zata ceba.
Bayan tafiyar Aunty Ruƙayya babu da ɗewa Hajiya Bunayya ta miƙe tare da kallon Mommy tace.
“Toh ƙanwata zamu wuce Allah yaƙara sauƙi”.
Murmushi Mommy tayi da faɗin.
“Nagode Yaya ahuta gajiya”.
Hajiya Lami tace.
“Babu Gajiya”.
Sannan suka fice Khausar kuwa jinginar da kai tayi kamar mai bacci.
Da daddare Khausar ta miƙe daga kan dogon kujeran asibitin da take kwance ta dubi Mommy da bacci ya fara fisgarta tace.
“Mommy”.
Buɗe idanu Mommy tayi tare da kallon Khausar tace.
“Na'am Khausar ya akayi?”.
Ajiyar zuciya Khausar ta saki tana wasa da yatsun hannunta tace.
“Mommy baki zargi perpesoup ɗin nan da kika ci azubewar cikin nan ba!?”.
Sosai Mommy ta tsira mata ido na second uku zuwa biyar sai kuma ta miƙe daga kwanciyar da take Atake fara'ar dake fuskanta ya gushe cikin ɗaure fuska cikin kakkausan Murya tace.
“Khausar!, Khausar!!, Khausar!!!, Ki cigaba Nagode da abinda kike min Khausar, duk irin tarbiyyan da nake baki fatali kike dashi ko, kina ɗaukar rashin yarda kina ɗaurawa mutane ki sani Manzon Allah (S.A.W) Yace.
:Azzana zambu walau kana haƙƙun”.
Khausar kuwa ƙasa da kai tayi hawaye masu zafi suka cika Idanunta shin sai yaushe mahaifiyarta zata amince da gaskiyar da take so ta sani akan Hajiya Bunayya basa ƙaunarta cutar da ita suke sonyi.
Cikin sanyi murya tare da rauni gami da ban haƙuri tace.
“Shikenan Mommy kiyi haƙuri Allah ya huci zuciyarki”.
Mommy bata tanka taba ta juya ta gyara kwanciyar, ta itama Khausar juyawa tayi ta kwanta zuciyarta babu daɗi.
Washe gari Alhamis Da safe Dr ya shiga ya basu sallama dan jikinta yayi sauƙi Sosai Lamiɗo da kansa yaje ya maido su gida.
Suna dawowa Hajiya Bunayya ta shigo hannunta riƙe da babban Warmers da tayi Perpesoup ɗin Kaji ta shigo dashi.
Zama tayi akan 2sitter tace.
“Sannu ƙanwata ya ƙarfin jikin?”.
Mommy tayi yar dariya tare da faɗin.
“Jiki yayi sauƙi Yaya sai faman hidima kike dani kamar wacce tayi haihuwar farko?”.
Dariya Hajiya Bunayya tayi da faɗin.
“Ai mai ɓari yafi son akula dashi fiye da mai haihuwa”.
Khausar dake tsaye duk takaici ya gama cikita gashi babu dama ta faɗawa mahaifiyarta gaskiya sai ta hau kanta da faɗa bayan da ta iya daga ƙarshe ma Saboda takaici kawai sai ta koma Bedroom ɗin ta ta fara karatu.
Wunin ranan haka Hajiya Bunayya ta yini tare da Mommy ta cigaba da kulawa da ita.
Washe gari juma'a dai-dai lokacin da maza suka tafi Juma'a dai-dai lokacin da kowa ya tafi Sallar juma'a Akuma lokacin ne Hajiya Bunayya da Hajiya Lami suka tafi gidan Boka Kar'uzu.
Khausar da Mommy ne zaune suna hira sosai jikin Mommy yayi ƙarfi abinka da mai juriya ga kuma kulawa da take samu.
Sallamar Aunty Ruƙayya ya katse musu hirar da suke.
Khausar ta faɗaɗa fara'ar fuskarta kana tace.
“Aunty Ruƙayya sannu da zuwa ina Affan?”.
Murmushi Aunty Ruƙayya tayi tana zama tace.
“Affan yana lafiya bacci ma yake ya mai jikin”.
Khausar tace.
“Jiki da sauƙi”.
Aunty Ruƙayya tace.
“Masha Allah Ubangiji ya ƙara sauki”.
Cikin sakin fuska Mommy ta gyara zaman hular dake kanta tace.
“Hajiya Ruƙayya sannu da zuwa ya gajiyarki?”.
“Hajiya Ruƙayya tayi murmushi da faɗin.
“Babu gajiya ya jikin naki?”.
“Jiki yayi sauƙi ya yara?”.
Alhamdulillah ta bata amsa.
“Khausar kece sannu da zuwa, shigo ciki”.
Da sauri tace.
“A'a Aunty sauri nakeyi ai”.
Cikin kulawa tace.
“Yo yasu Mommy ki?”.
Murmushi Khausar tayi tace.
“Wallahi Aunty Ruƙayya Mommy ce ke asibiti bata da lafiya, shine nace bari nazo na faɗa miki, Ni yanzu ma zan wuce ko za muje tare?”.
Cike da tausayawa Aunty Ruƙayya tace.
“Ayyah Allah ya bata lafiya zanje bari ina zuwa mu tafi tare”.
Kai Khausar ta gyaɗa da faɗin.
“Toh”.
Aunty Ruƙayya kuwa bedroom ta shiga tare kiran mijinta a waya, bayan ya bata izinine, ta ɗauko key mota da mayafinta suka fita,
suka shiga mota,
jingina kai Khausar tayi da jikin motar kalaman Hajiya Bunayya nayi mata suwwa akunne.
Juyawa Aunty Ruƙayya tayi ganin yanda Khausar ta zurfafa cikin tunani yasa tace.
“Ki riƙa yi mata addu'a”.
Kai kawai Khausar ta iya gyaɗa mata.
Cikin Mintuna kaɗan suka isa Asibitin bakinsu ɗauke da Sallama suka shiga ɗakin da aka kwantar da Mommy saboda Hajiya Bunayya ta faɗa mata.
Kwance akan gado suka tarar da ita yayin da Lamiɗo ke gefenta akan kujera hannunsa riƙe da kofin tea yana miƙa mata da faɗin.
“Ki tashi kisha”.
Yana jin Sallamar Khausar ya juya yana kallonta har ta isa kusa dashi.
Cike da kulawa yace.
“Khausar har kun dawo?”.
Kai ta gyaɗa kana tace.
“Eh Abba ya jikin Mommy!?”.
Sai da ya ɗan kalli Mommy dake jingine da pillow sai kuma ya mayar da Kallonsa kan Khausar yace.
“Da sauƙi”.
Sai asannan ya lura da Hajiya Rukayya ya ɗan yi murmushi da faɗin.
“Hajiya Ruƙayya sannu da zuwa”.
Zama tayi akujeran dake kusa da ita tana cewa.
“Yawwa ya Hajiya Aysha da jikin kuma?”.
Ɗan Murmushi yayi kana yace.
“Da sauƙi”.
Tana kallon Mommy tace.
“Ubangiji Allah ya ƙara sauki”.
Ya amsa da.
“Ameen ya hayyu ya ƙayyum”.
Khausar kuwa bakin gadon ta ƙarasa ta riƙe hannun Mommy acikin nata.
Cikin raunin murya tare da tausayawa mahaifiyar tata tace.
“Sannu Mommy ya Jikin?”.
Lumshe idanu Mommy tayi kana ta buɗe su a hankali tace.
“Da sauƙi Khausar bana jin komai in dan ta nice ma, da su sallame ni in koma gida mu kwana tare, dan bana jin ciwon cikin yayi sauƙi babu inda yake min ciwo!”.
Ajiyar zuciya Khausar ta sauƙe tare da faɗin.
“Masha Allah Mommy Allah yaƙara sauƙi Ubangiji ya ƙara tsarewa ya kare”.
A ranta kuwa cewa tace.
Ayyah da ace duk addu'o'in da takeyiwa Mommynta tun randa taci ferfesun da ace tana haɗa addu'ar da yaron cikin wata ƙil da bai zube ba.
Shafa kanta Mommy tayi cike da ƙaunar ta tace.
“Ameen Khausar ki kwantar da hankalin ki ba najin Komai”.
Ta faɗi hakan ganin yanda Khausar tayi zuru-zuru da ita.
Hajiya Ruƙayyance ta kalli Mommy kana tace.
“Hajiya Aysha ya ƙarfin jikin!?”
Murmushi Mommy tayi kana tace.
“Dasauƙi Hajiya Ruƙayya ya ‘Yar taki ya kuma rigima a makaranta!?".
Kallon Khausar Hajiya Ruƙayya tayi kana tace.
“A'a yanzu ai ta daina ta fara girma!”.
Jin haka yasa Khausar tayi murmushi.
Lamiɗo kuwa miƙewa yayi idanunsa akan Mommy yace.
“Toh shikenan bari na tafi dama ganin babu kowa ne yasa nake zaune bari na samu naje nayi wanka dan tunda muka zo ban samu na koma gida ba”.
Hajiya Ruƙayya tace.
“Ayyah ai babu komai Alhaji kaje”.
Jinjina kai Mommy tayi tace.
“Allah ya tsare”.
Ya Amsa da.
“Ameen”sannan ya juya ya fice.
Tafiyar Lamiɗo babu daɗewa Hajiya Bunayya da Hajiya Lami suka zo Raudat na riƙe da hannunta.
Suna shiga Hajiya Bunayya ta zauna daga gefen gadon tare da kallon Mommy tace.
“Sannu ƙanwata ya ƙarfin jikin?”.
Murmushi Mommy tayi kana tace.
“Ai naji sauki Yaya”.
Jinjina kai Hajiya Bunayya tayi cikin yanayin tausayawa tace.
“Allah ya baki lafiya”.
Hajiya Ruƙayya kuwa kallo ɗaya tayi wa Hajiya Bunayya da Hajiya Lami taji sam basu kwanta mata arai ba musanman ma Hajiya Bunayya dake wani shish-shugewa Mommy.
Ta dai daure tace.
“Sannunku da zuwa”.
Hajiya Bunayya da Hajiya Lami suka haɗa baki wajen cewa.
“Yawwa ya mai jikin”.
Ataƙaice Hajiya Ruƙayya tace.
“Da sauƙi”.
Hajiya Lami kuwa jikin gadon ta matasa Idanunta akan Mommy tace.
“Ayyah Sannu Hajiya Aysha Ashe ga abinda ya faru kuma? Amma wannan abu yayi yawa ai gwara Alhj yayi ƙoƙari ya fitar dake waje wannan matsalar ko yaushe da ansamu ciki ya zube ai babu daɗi!”.
Kafin Mommy tayi magana Hajiya Bunayya tayi saurin cewa.
“Kede bari Hajiya Lami abin nan yana damun mu, gaba ɗaya mun kasa gane menene ainihin matsalar, amma hankalinmu na tashi kullum cikin yanayin nan, abin babu daɗi yanzu ciki takwas kenan yana zubewa abin ai babu daɗi!”.
Taɓe baki Khausar da Hajiya Rukayya sukayi alokaci ɗaya.
Ahankali Mommy ta gyara matashin data kishingiɗa akai kana tace.
“Uyummm ya za'ayi da abinda Allah ya tsara, amma ni inaga nin ba wani matsala bane, tun da gashi na haihu bayan haihuwar Haiydar ma haka nata fama da ɓare-ɓaren nan, kuma daga baya da Allah ya kawo Ramadan da Raudat an haifesu ba komai ai”.
Cike da kirsa Hajiya Bunayya tayi yaƙe kana tace.
“Hakane kam, toh Allah ya kawo masu albarka”.
Hajiya Lami kuwa harara ta gallawa Mommy tare da taɓe baki aranta tace shegiya me iyayin jaraba keda haihuwa sai dai kiga anayi.
Idanun Hajiya Ruƙayya da Khausar na kan Hajiya Lami alokacin data taɓe baki ta harari Mommy,
Juyawa Hajiya Ruƙayya tayi ta kalli Khausar tare da jinjina kai itama Khausar kai ta jinjina.
Miƙewa Hajiya Ruƙayya tayi tare da kallon Mommy tace.
“Toh Hajiya Aysha Ubangiji Allah ya ƙara sauki sannan Allah ya tsareki daga sharrin abin ƙi ni zan wuce!”.
A hankali Mommy ta ɗan yunƙura tare da lumshe Idanunta kana tace.
“Ameen ya hayyu ya ƙayyum Hajiya Ruƙayya Nagode”.
Hajiya Lami da Hajiya Bunayya kuwa baki suka saki suna kallon Hajiya Ruƙayya da Mamaki aransu suka ce kaji shegiyar mata da iyayi uban wa takewa wannan addu'ar.
Miƙewa Raudat tayi tare da riƙe hannun Hajiya Ruƙayya tace.
“Aunty Ruƙayya ni zan biki gidanki, Inje in kwana dasu Salman tun da gobe babu makarata”.
Da sauri Khausar ta kalli Raudat dake riƙe da hannun Aunty Ruƙayya tace.
“Ayyah Raudat am baza mu kwana ba?”.
Girgiza kai Raudat tayi tare da langwaɓar da kai kana tace.
“ Ni dai Ina tsoro ni bazan zauna ba”.
Kai Khausar ta gyaɗa da faɗin.
“Shikenan kibi Aunty Ruƙayya”.
Murmushi Aunty Ruƙayya tayi tare da jan hannun Khausar dake cikin nata
Har sun kai ƙofa Hajiya Bunayya ta ƙirƙiri murmushi tana kallon bayan Raudat tace.
“Oohhh Raudat ba zaki bini mu tafi gida ba?”.
Kafaɗa Raudat ta maƙale tace.
“A'a ni zanbi Aunty Ruƙayya”.
Aunyty Ruƙayya kuwa jan hannun Raudat tayi suka fice batare data sake jiran jin Abinda Hajiya Bunayya zata ceba.
Bayan tafiyar Aunty Ruƙayya babu da ɗewa Hajiya Bunayya ta miƙe tare da kallon Mommy tace.
“Toh ƙanwata zamu wuce Allah yaƙara sauƙi”.
Murmushi Mommy tayi da faɗin.
“Nagode Yaya ahuta gajiya”.
Hajiya Lami tace.
“Babu Gajiya”.
Sannan suka fice Khausar kuwa jinginar da kai tayi kamar mai bacci.
Da daddare Khausar ta miƙe daga kan dogon kujeran asibitin da take kwance ta dubi Mommy da bacci ya fara fisgarta tace.
“Mommy”.
Buɗe idanu Mommy tayi tare da kallon Khausar tace.
“Na'am Khausar ya akayi?”.
Ajiyar zuciya Khausar ta saki tana wasa da yatsun hannunta tace.
“Mommy baki zargi perpesoup ɗin nan da kika ci azubewar cikin nan ba!?”.
Sosai Mommy ta tsira mata ido na second uku zuwa biyar sai kuma ta miƙe daga kwanciyar da take Atake fara'ar dake fuskanta ya gushe cikin ɗaure fuska cikin kakkausan Murya tace.
“Khausar!, Khausar!!, Khausar!!!, Ki cigaba Nagode da abinda kike min Khausar, duk irin tarbiyyan da nake baki fatali kike dashi ko, kina ɗaukar rashin yarda kina ɗaurawa mutane ki sani Manzon Allah (S.A.W) Yace.
:Azzana zambu walau kana haƙƙun”.
Khausar kuwa ƙasa da kai tayi hawaye masu zafi suka cika Idanunta shin sai yaushe mahaifiyarta zata amince da gaskiyar da take so ta sani akan Hajiya Bunayya basa ƙaunarta cutar da ita suke sonyi.
Cikin sanyi murya tare da rauni gami da ban haƙuri tace.
“Shikenan Mommy kiyi haƙuri Allah ya huci zuciyarki”.
Mommy bata tanka taba ta juya ta gyara kwanciyar, ta itama Khausar juyawa tayi ta kwanta zuciyarta babu daɗi.
Washe gari Alhamis Da safe Dr ya shiga ya basu sallama dan jikinta yayi sauƙi Sosai Lamiɗo da kansa yaje ya maido su gida.
Suna dawowa Hajiya Bunayya ta shigo hannunta riƙe da babban Warmers da tayi Perpesoup ɗin Kaji ta shigo dashi.
Zama tayi akan 2sitter tace.
“Sannu ƙanwata ya ƙarfin jikin?”.
Mommy tayi yar dariya tare da faɗin.
“Jiki yayi sauƙi Yaya sai faman hidima kike dani kamar wacce tayi haihuwar farko?”.
Dariya Hajiya Bunayya tayi da faɗin.
“Ai mai ɓari yafi son akula dashi fiye da mai haihuwa”.
Khausar dake tsaye duk takaici ya gama cikita gashi babu dama ta faɗawa mahaifiyarta gaskiya sai ta hau kanta da faɗa bayan da ta iya daga ƙarshe ma Saboda takaici kawai sai ta koma Bedroom ɗin ta ta fara karatu.
Wunin ranan haka Hajiya Bunayya ta yini tare da Mommy ta cigaba da kulawa da ita.
Washe gari juma'a dai-dai lokacin da maza suka tafi Juma'a dai-dai lokacin da kowa ya tafi Sallar juma'a Akuma lokacin ne Hajiya Bunayya da Hajiya Lami suka tafi gidan Boka Kar'uzu.
Khausar da Mommy ne zaune suna hira sosai jikin Mommy yayi ƙarfi abinka da mai juriya ga kuma kulawa da take samu.
Sallamar Aunty Ruƙayya ya katse musu hirar da suke.
Khausar ta faɗaɗa fara'ar fuskarta kana tace.
“Aunty Ruƙayya sannu da zuwa ina Affan?”.
Murmushi Aunty Ruƙayya tayi tana zama tace.
“Affan yana lafiya bacci ma yake ya mai jikin”.
Khausar tace.
“Jiki da sauƙi”.
Aunty Ruƙayya tace.
“Masha Allah Ubangiji ya ƙara sauki”.
Cikin sakin fuska Mommy ta gyara zaman hular dake kanta tace.
“Hajiya Ruƙayya sannu da zuwa ya gajiyarki?”.
“Hajiya Ruƙayya tayi murmushi da faɗin.
“Babu gajiya ya jikin naki?”.
“Jiki yayi sauƙi ya yara?”.
Alhamdulillah ta bata amsa.