Sashe 7
Sakayyah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wani irin mayataccen kallo Samira ke bin lips ɗin Moddibo dashi, tana mai kallon dukkan yadda yake motsasu, da yadda tattausan sajensa ke zuba ƙyalli ƙawarta Ikilima Ibrahim ce ta ɗan taɓata da kafa alamun wannan wanne irin kallo ne.
Yayinda gefen damansu kuwa, wata madaidaciyar macece, Hadiza Muhammad Yahaya, wacce take cikin sabbin dalibai.
Kallon da Samira Sani keyiwa Moddibo ne ke bata mamaki.
Shi kuwa Moddibo a hankali yaci gaba da cewa.
Kuma daga Ukbatu Ibn Amir Allah ya yarda dashi yace:
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi.
Ya fito alhalin muna cikin rumfa sai yace:
(Wannene daga cikinku zai so ya fita kullum da safe zuwa ƙoramar Buɗhan ko Aƙiƙ ya dawo da taguwa biyu masu manyan tozuna ba tare da yayi wani laifi ba ko yanke zumunta ba?
Mukace masa muna son haka.
Yace:
(Ɗayanku yaje Masallaci ya nemi sani, ko ko ya karanta ayoyi biyu daga cikin littafin Allah, mabuwayi mai ɗaukana, yafi masa taguwa uku ayoyi huɗu sun fi masa taguwa huɗu da kwatankwacin adadinsu na raƙuma.)
Kunga ashe muna ɓarar da damarmakinmu riƙe da waya ba tare da mun samu mun ribaci ilimin da iyayenmu da malanmu suka bamu ba.
Kuma mai tsira da Amincin Allah yace:
(Wanda ya zauna a wani waje, bai ambaci Allah a wajenba, wannan zai zamanto masa abin bibiya a wajen Allah, wanda ya kwanta a makwanci bai ambaci Allah a wajenba shima zai zamanto masa abin bibiya a wajen ALLAH.
Kuma mai tsira da amincin Allah yace:
(Babu wasu mutane da zasu zauna a majalisi da basu ambaci Allah a cikinsa ba, kuma basu yi salati ga annabinsu ba, face ya zamo musu abin bibiya, in Allah yaso yayi musu azaba, in yaso kuma sai ya gafarta musu.”
Jujjuya idanunsa yayi fuskarsa cike da shauƙin son Mahaikin Allah Muhammadu Rasulullah, da sahabbansa,
Wani irin sassayan numfashi ya fesar tare da lumshe idanunsa, wanda yakan shiga wannan yanayi a duk lokacin da yakeyiwa ɗalibansa nuni da al'khairan dake cikin ammaton Allah da bin sunnar manzonmu abinkoyinmu abinsonmu da sahabbansa masu daraja.
Ita kuwa Khausar ƙasa tai da idanunta.
Sai kuma ta ɗan ɗago ta kalleshi jin tattausar muryarsa yaci gaba da cewa.
“Kuma mai tsira da amincin Allah yace:
Babu wasu mutane da zasu tashi daga wani majalisi da basu ambaci Allah a cikinsa ba, face sun zama kamar sun tashi daga kan *mushen jaki ne* kuma zai zamanto musu abin dana sani)”....
Ya ƙare mgnar da haɗe kan yatsunsa duka, kana sai ya buɗasu a tare da ware tafin hannunsa kamar ya sake abu,
alamun ya dasa babbab ɗamba, ya gama da wannan yankin.
Gaba ɗaya hankalinsu tunaninsu duk yana kansa, domin suna matuƙar jin dadin yadda wasu lokutan idan ya shiga aji yake tunasar dasu mahimman abubuwan da suka cancanci musulmi ya lizamcesu.
Yayinda wasu kuwa da sam baya shiga ajujuwansu cike da son salon sa suke sauraronsa, kasan cewar makarantar nada yalwar malamai kuma shi aiyuka sun mai yawa shisa ba dukkan class da suke dashi yake shigaba.
Shi kuwa Moddibo cikin alamun gajiya da yawan motsa lips nasa da yayi yaci gaba da cewa a gaggauce.
“Mu farka mu ribaci wannan shekarar dukanta kada muce dan wannan wata na Ramadan daya shuɗe, zamu bar wasu ayyukan ibada, mu jure mu zamo dasu ɗabi'armu a kullum domin shi ubangiji ka gafartawa bayinsa, a duk sanda yaso ya ainta wasu daga azaba zuwa rahmarsa madaumiya, mu wasar da wayoyin nan mu ruggumi Alqur'ani mai girma da tasbihai ya zama dai ita wayar nan sai time to time zamu riƙe ya ke mai karatu dake nake."
Ya faɗi hakan yana nuna gefensu Samira dake buɗe da littafi a gabansu.
Sai kuma ya ɗan gyara saƙale Lapel Microphone din a wuyar jallabiyar jikinsa dan yaji muryarsa tana ƙasa sosai alum yadan zame kaɗan, da ɗan sauri yace.
“Zaku iya duba Muslim (1/554) Abu Dawud (4/264) da waninsa duba Sahihul Jam'i, (5/342). Tirmizi duba Sahihul Tirmizi (3/140) Abu Dawud (4/264) da Ahmad (2/389) duba Sahihul Jami (5/176) Allah shine mafi sani... Abinda nace dai-dai Allah ya haɗamu a mizanin ladan abinda nai kuskure Allah ya gafartamin.”
Ya rufe mgnar da addu'a tare da juyawa ya fita.
Sukuwa gaba ɗaya numfashi suka sassauƙe, yana fitowa Malam Jamil na isowa wurin, dan shi zai shiga ya shaida musu kwanakin da aka ƙara.
Kai Modibbo ya kauda gefe, jin Aminin nashi na cewa.
“Fattanah maza yi gudu ki shiga aji kada in rigagi, shiga, dan in na rigaki nima yau gadin aji zansa kiyi mana”.
Da sauri Khausar din ta juyo tare da kallon shi cikin alamun yanai musu barkwanci tace.
“Malam ko ta window ma zan shiga”.
Murmushin yayi tare da cewa.
“Har yanzu baki girmi shiga ta window ba FATTANAH”.
Da sauri tace.
“Toh ai banyi jikiba, ka gani”.
Kawai sai ta kama jikin window alamun zata zauna ta wajen sai ta juya ta ciki.
Cikin yamutsa fuska Moddibo yace.
“Ke bar nan,”.
Ai da sauri ta diro tare, da nufar ƙofa, tana tura baki.
Shi kuwa Malam Jamil cikin tsananin son yarinyar sabida ƙwazonta da jan da kwanyarta keyi kana da ƙawancenta da ƙanwarsa Asma'u Ahmad ya bita da ido.
Rungume Moddibo yayi tare da yin mgn murya can ƙasa.
“Tuba mukeyi Moddibo ai mana tsawan a hankali ka mance baka cire Lapel Microphone ɗinba, har nima tsawar ta razanani”.
Wani irin nannauyan numfashin Moddibo ya sauƙe tare lumshe idanunsa.
Shi kuwa M Jamil murmushin yayi kana kuma ya sake shi yace.
“Lokaci na tafiya sai na fito na sallami maza kam”.
Kai Moddibo ya gyaɗa tare da sauƙa ƙasa.
Goma dai-dai aka tashi islamiyan gaba ɗaya duk ɗaliban suka koma gida bayan M Jamil ya musu bayanin dalilin ƙarin hutun, wanda kuma suma sunga hakan.
Ƙarfe ɗaya dai-dai suka tashi daga taron tattaunawa da malaman nasu baki ɗaya.
Bayan sunyi sallan azahar ne, kana duk suka tafi, ma'aikata sukaci gaba da aikinsu.
A gidansu Khausar kuwa.
Khausar ce kwance bisa 3 str daga ita sai yar doguwar rigar material mai taushi a jikinta, Pink collor, sai hular sanyi data sa a kanta, yayinda himilin gashinta yayi tub-tub a ciki.
Da alamun bacci take sonyi.
Cikin sanyi ta buɗe ido ta tare da juyowa ta kalli Momynta dake fitowa daga kitchen ɗinta, hannunta riƙe da plate da yankakkun fruits a ciki masu sanyi, gefen ta ta zauna bisa 1 str ta ɗaura plate ɗin kan cinyarta tare kallon Khausar ɗin data miƙa mata hannu alamun ta bata.
“Tashi kije ki ɗebo Uniform ɗin ku, nasan yanzu ya bushe kizo ki goge muku kafin a kira magriba”.
Numfashi mai ɗan sanyi Khausar ɗin ta fesar tare da miƙewa zaune, ita kuwa Momy tafin sawun ɗiyar Tata take kallo cike da ganin kamannin sawunta dana ahlinta.
Hannu tasa ta ɗauki inabi guda uku. Kana ta miƙe tsaye tare da juyawa ta fita.
Ita kuwa Momy da idanu ta rakata.
Tana fita a barandar ta tsaya tare da ɗan sa hannunta na dama ta riƙe ƙugunta.
Amina ce ta fito daga side din Gimbiya Bunayya, mahaifiyarsu kenan, uwar gidan Lamido,
Wacce daga itana sai Maman su Khausar wacce itace amaryarsa.
Wani irin kallo Amina tayiwa Khausar tare da cewa.
“Hamshaƙiya, cin abu a tsaye ba koyarwar musulunci bane”.
Fuska Khausar ɗin ta ɗan yamutsa tare da cewa.
“Ngd”. Sai kuma ta miƙawa Aminu ƙanin Amina wanda yake gefenta.
Da sauri Amina ta kwaɓe hannun yaron da bazai gaza shekara goma sha ɗaya ba tare da cewa.
“Makwaɗaicin baza, in zakaci akwai a fridge kaje a baka”.
Ido Khausar ɗin ta zuba mata, sai kuma ta sauƙe numfashi dan batayi mmkin hakanba, cikin alamun kasalan da baccin da takeji ya sakar mata, ta nufi wurin shanyan nasu, a hankali take tafiya, dan ganin shanyan nasu yana can har bayan Part ɗin Hajia Bunayya Umma.
“Wannan daga gani ma aikin Ramadan ne, shine zai zo yayi mana shanya har nan, zaice waɗan can igiyoyin tsawonsa bazai kaiba”.
Ta ƙare mgnar tana nufar can.
A hankali ta fara janye shanyan, har ta isa dai-dai window Hajia Bunayya, cikin mamaki ta ɗan tsaya jin yadda Umman ke mgn da faɗa-faɗa.
“Kada in damufa kake cewa.
Kasan kuwa irin tashin hankali da nake ciki duk sanda na buɗi idanuna na kalli Haiydar a matsayin ɗan Lamido Yariman Gembila kuwa, ko ka mance shine ɗan sa na miji babba, shin baka ganin iyakata da mulki sai dai gani sai hange tunda shine ɗa babba akan Aminu na.
Kai bakaga yadda komai zai juye min ba a gaba, ina gani sarauta zata koma ɗakin Aysha ƴaƴanta ne zasu mulki masarautarmun”.
Sai kuma tayi shiru alamun tana sauraron abin da ake cewa a ɗaya sashin.
Ita kuwa Khausar cike da tsoron halin irin na Umma, gashi dai abinda taji, amman koda zata kwana gayawa mahaifiyarsu bazata taɓa yardaba, domin Umma bata taɓa nuna kishinta a kanta, shiyasa ta ɗauki dukkan yarda ta bata.
Cikin tsananin tsoro Khausar ɗin ta zaro ido ta tare dasa tafin hannunta ta dafe ƙahon zuciyarta, jin Hajia Bunayya na cewa.
“Wallahi tallahi billahil azeem zanyi komai dan ganin bayan Aysha da yaranta, zanyi duk abinda ya kama domin in kauda Haiydar a matsayin yarima mai jiran gado, dan wlh Allah zan iya kasheshi kowama ya huta!...”.
Cikin tsananin kaɗuwa Khausar ta juya da sassarfa ta koma sade ɗin Maminta, tana isa kawai sai ta watsar da kayan bisa kujera.
Da sauri ta kamo hannun mahaifiyar tata tare da cewa.
“Momy! Momy dan Allah ki biyoni zo kiji wani abu”.
Ta ƙare mgnar a matuƙar kiɗime, wanda hakan yasa dole Hajia Aysha ta bita a baya.
Ita kuwa da sauri take jenta, har zuwa bayan window Hajia Bunayya.
Cirko-cirko suka tsaya,
Ita kam Khausar cike da firfito da ido waje take sauraron abinda Hajia Bunayya ke faɗi.
Momy kuwa wani irin...!
Yayinda gefen damansu kuwa, wata madaidaciyar macece, Hadiza Muhammad Yahaya, wacce take cikin sabbin dalibai.
Kallon da Samira Sani keyiwa Moddibo ne ke bata mamaki.
Shi kuwa Moddibo a hankali yaci gaba da cewa.
Kuma daga Ukbatu Ibn Amir Allah ya yarda dashi yace:
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi.
Ya fito alhalin muna cikin rumfa sai yace:
(Wannene daga cikinku zai so ya fita kullum da safe zuwa ƙoramar Buɗhan ko Aƙiƙ ya dawo da taguwa biyu masu manyan tozuna ba tare da yayi wani laifi ba ko yanke zumunta ba?
Mukace masa muna son haka.
Yace:
(Ɗayanku yaje Masallaci ya nemi sani, ko ko ya karanta ayoyi biyu daga cikin littafin Allah, mabuwayi mai ɗaukana, yafi masa taguwa uku ayoyi huɗu sun fi masa taguwa huɗu da kwatankwacin adadinsu na raƙuma.)
Kunga ashe muna ɓarar da damarmakinmu riƙe da waya ba tare da mun samu mun ribaci ilimin da iyayenmu da malanmu suka bamu ba.
Kuma mai tsira da Amincin Allah yace:
(Wanda ya zauna a wani waje, bai ambaci Allah a wajenba, wannan zai zamanto masa abin bibiya a wajen Allah, wanda ya kwanta a makwanci bai ambaci Allah a wajenba shima zai zamanto masa abin bibiya a wajen ALLAH.
Kuma mai tsira da amincin Allah yace:
(Babu wasu mutane da zasu zauna a majalisi da basu ambaci Allah a cikinsa ba, kuma basu yi salati ga annabinsu ba, face ya zamo musu abin bibiya, in Allah yaso yayi musu azaba, in yaso kuma sai ya gafarta musu.”
Jujjuya idanunsa yayi fuskarsa cike da shauƙin son Mahaikin Allah Muhammadu Rasulullah, da sahabbansa,
Wani irin sassayan numfashi ya fesar tare da lumshe idanunsa, wanda yakan shiga wannan yanayi a duk lokacin da yakeyiwa ɗalibansa nuni da al'khairan dake cikin ammaton Allah da bin sunnar manzonmu abinkoyinmu abinsonmu da sahabbansa masu daraja.
Ita kuwa Khausar ƙasa tai da idanunta.
Sai kuma ta ɗan ɗago ta kalleshi jin tattausar muryarsa yaci gaba da cewa.
“Kuma mai tsira da amincin Allah yace:
Babu wasu mutane da zasu tashi daga wani majalisi da basu ambaci Allah a cikinsa ba, face sun zama kamar sun tashi daga kan *mushen jaki ne* kuma zai zamanto musu abin dana sani)”....
Ya ƙare mgnar da haɗe kan yatsunsa duka, kana sai ya buɗasu a tare da ware tafin hannunsa kamar ya sake abu,
alamun ya dasa babbab ɗamba, ya gama da wannan yankin.
Gaba ɗaya hankalinsu tunaninsu duk yana kansa, domin suna matuƙar jin dadin yadda wasu lokutan idan ya shiga aji yake tunasar dasu mahimman abubuwan da suka cancanci musulmi ya lizamcesu.
Yayinda wasu kuwa da sam baya shiga ajujuwansu cike da son salon sa suke sauraronsa, kasan cewar makarantar nada yalwar malamai kuma shi aiyuka sun mai yawa shisa ba dukkan class da suke dashi yake shigaba.
Shi kuwa Moddibo cikin alamun gajiya da yawan motsa lips nasa da yayi yaci gaba da cewa a gaggauce.
“Mu farka mu ribaci wannan shekarar dukanta kada muce dan wannan wata na Ramadan daya shuɗe, zamu bar wasu ayyukan ibada, mu jure mu zamo dasu ɗabi'armu a kullum domin shi ubangiji ka gafartawa bayinsa, a duk sanda yaso ya ainta wasu daga azaba zuwa rahmarsa madaumiya, mu wasar da wayoyin nan mu ruggumi Alqur'ani mai girma da tasbihai ya zama dai ita wayar nan sai time to time zamu riƙe ya ke mai karatu dake nake."
Ya faɗi hakan yana nuna gefensu Samira dake buɗe da littafi a gabansu.
Sai kuma ya ɗan gyara saƙale Lapel Microphone din a wuyar jallabiyar jikinsa dan yaji muryarsa tana ƙasa sosai alum yadan zame kaɗan, da ɗan sauri yace.
“Zaku iya duba Muslim (1/554) Abu Dawud (4/264) da waninsa duba Sahihul Jam'i, (5/342). Tirmizi duba Sahihul Tirmizi (3/140) Abu Dawud (4/264) da Ahmad (2/389) duba Sahihul Jami (5/176) Allah shine mafi sani... Abinda nace dai-dai Allah ya haɗamu a mizanin ladan abinda nai kuskure Allah ya gafartamin.”
Ya rufe mgnar da addu'a tare da juyawa ya fita.
Sukuwa gaba ɗaya numfashi suka sassauƙe, yana fitowa Malam Jamil na isowa wurin, dan shi zai shiga ya shaida musu kwanakin da aka ƙara.
Kai Modibbo ya kauda gefe, jin Aminin nashi na cewa.
“Fattanah maza yi gudu ki shiga aji kada in rigagi, shiga, dan in na rigaki nima yau gadin aji zansa kiyi mana”.
Da sauri Khausar din ta juyo tare da kallon shi cikin alamun yanai musu barkwanci tace.
“Malam ko ta window ma zan shiga”.
Murmushin yayi tare da cewa.
“Har yanzu baki girmi shiga ta window ba FATTANAH”.
Da sauri tace.
“Toh ai banyi jikiba, ka gani”.
Kawai sai ta kama jikin window alamun zata zauna ta wajen sai ta juya ta ciki.
Cikin yamutsa fuska Moddibo yace.
“Ke bar nan,”.
Ai da sauri ta diro tare, da nufar ƙofa, tana tura baki.
Shi kuwa Malam Jamil cikin tsananin son yarinyar sabida ƙwazonta da jan da kwanyarta keyi kana da ƙawancenta da ƙanwarsa Asma'u Ahmad ya bita da ido.
Rungume Moddibo yayi tare da yin mgn murya can ƙasa.
“Tuba mukeyi Moddibo ai mana tsawan a hankali ka mance baka cire Lapel Microphone ɗinba, har nima tsawar ta razanani”.
Wani irin nannauyan numfashin Moddibo ya sauƙe tare lumshe idanunsa.
Shi kuwa M Jamil murmushin yayi kana kuma ya sake shi yace.
“Lokaci na tafiya sai na fito na sallami maza kam”.
Kai Moddibo ya gyaɗa tare da sauƙa ƙasa.
Goma dai-dai aka tashi islamiyan gaba ɗaya duk ɗaliban suka koma gida bayan M Jamil ya musu bayanin dalilin ƙarin hutun, wanda kuma suma sunga hakan.
Ƙarfe ɗaya dai-dai suka tashi daga taron tattaunawa da malaman nasu baki ɗaya.
Bayan sunyi sallan azahar ne, kana duk suka tafi, ma'aikata sukaci gaba da aikinsu.
A gidansu Khausar kuwa.
Khausar ce kwance bisa 3 str daga ita sai yar doguwar rigar material mai taushi a jikinta, Pink collor, sai hular sanyi data sa a kanta, yayinda himilin gashinta yayi tub-tub a ciki.
Da alamun bacci take sonyi.
Cikin sanyi ta buɗe ido ta tare da juyowa ta kalli Momynta dake fitowa daga kitchen ɗinta, hannunta riƙe da plate da yankakkun fruits a ciki masu sanyi, gefen ta ta zauna bisa 1 str ta ɗaura plate ɗin kan cinyarta tare kallon Khausar ɗin data miƙa mata hannu alamun ta bata.
“Tashi kije ki ɗebo Uniform ɗin ku, nasan yanzu ya bushe kizo ki goge muku kafin a kira magriba”.
Numfashi mai ɗan sanyi Khausar ɗin ta fesar tare da miƙewa zaune, ita kuwa Momy tafin sawun ɗiyar Tata take kallo cike da ganin kamannin sawunta dana ahlinta.
Hannu tasa ta ɗauki inabi guda uku. Kana ta miƙe tsaye tare da juyawa ta fita.
Ita kuwa Momy da idanu ta rakata.
Tana fita a barandar ta tsaya tare da ɗan sa hannunta na dama ta riƙe ƙugunta.
Amina ce ta fito daga side din Gimbiya Bunayya, mahaifiyarsu kenan, uwar gidan Lamido,
Wacce daga itana sai Maman su Khausar wacce itace amaryarsa.
Wani irin kallo Amina tayiwa Khausar tare da cewa.
“Hamshaƙiya, cin abu a tsaye ba koyarwar musulunci bane”.
Fuska Khausar ɗin ta ɗan yamutsa tare da cewa.
“Ngd”. Sai kuma ta miƙawa Aminu ƙanin Amina wanda yake gefenta.
Da sauri Amina ta kwaɓe hannun yaron da bazai gaza shekara goma sha ɗaya ba tare da cewa.
“Makwaɗaicin baza, in zakaci akwai a fridge kaje a baka”.
Ido Khausar ɗin ta zuba mata, sai kuma ta sauƙe numfashi dan batayi mmkin hakanba, cikin alamun kasalan da baccin da takeji ya sakar mata, ta nufi wurin shanyan nasu, a hankali take tafiya, dan ganin shanyan nasu yana can har bayan Part ɗin Hajia Bunayya Umma.
“Wannan daga gani ma aikin Ramadan ne, shine zai zo yayi mana shanya har nan, zaice waɗan can igiyoyin tsawonsa bazai kaiba”.
Ta ƙare mgnar tana nufar can.
A hankali ta fara janye shanyan, har ta isa dai-dai window Hajia Bunayya, cikin mamaki ta ɗan tsaya jin yadda Umman ke mgn da faɗa-faɗa.
“Kada in damufa kake cewa.
Kasan kuwa irin tashin hankali da nake ciki duk sanda na buɗi idanuna na kalli Haiydar a matsayin ɗan Lamido Yariman Gembila kuwa, ko ka mance shine ɗan sa na miji babba, shin baka ganin iyakata da mulki sai dai gani sai hange tunda shine ɗa babba akan Aminu na.
Kai bakaga yadda komai zai juye min ba a gaba, ina gani sarauta zata koma ɗakin Aysha ƴaƴanta ne zasu mulki masarautarmun”.
Sai kuma tayi shiru alamun tana sauraron abin da ake cewa a ɗaya sashin.
Ita kuwa Khausar cike da tsoron halin irin na Umma, gashi dai abinda taji, amman koda zata kwana gayawa mahaifiyarsu bazata taɓa yardaba, domin Umma bata taɓa nuna kishinta a kanta, shiyasa ta ɗauki dukkan yarda ta bata.
Cikin tsananin tsoro Khausar ɗin ta zaro ido ta tare dasa tafin hannunta ta dafe ƙahon zuciyarta, jin Hajia Bunayya na cewa.
“Wallahi tallahi billahil azeem zanyi komai dan ganin bayan Aysha da yaranta, zanyi duk abinda ya kama domin in kauda Haiydar a matsayin yarima mai jiran gado, dan wlh Allah zan iya kasheshi kowama ya huta!...”.
Cikin tsananin kaɗuwa Khausar ta juya da sassarfa ta koma sade ɗin Maminta, tana isa kawai sai ta watsar da kayan bisa kujera.
Da sauri ta kamo hannun mahaifiyar tata tare da cewa.
“Momy! Momy dan Allah ki biyoni zo kiji wani abu”.
Ta ƙare mgnar a matuƙar kiɗime, wanda hakan yasa dole Hajia Aysha ta bita a baya.
Ita kuwa da sauri take jenta, har zuwa bayan window Hajia Bunayya.
Cirko-cirko suka tsaya,
Ita kam Khausar cike da firfito da ido waje take sauraron abinda Hajia Bunayya ke faɗi.
Momy kuwa wani irin...!