Sashe 90
Sakayyah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Aɓangaren Abban M Jameel kuwa tsaye yake ajikin window falonsa ya tsirawa harabar gidan Ido tun bayan fitar Motar M Jameel ya kasa motsa wa daga wajen.
Hajiya Karima data fito daga Bedroom ɗin sa ta dubesa cike da kulawa tace.
“Ya dai Alhj tun tuni kana tsaye ana ka gaza motsa sama da awa biyu kenan tun bayan fitar motar Jameel kake tsaye lafiya kuwa?”.
Cikin wani irin yanayi ya lumshe idonsa.
Haka nan yaji ruwan hawaye na tsats-tsafo masa a hankali ya sauƙe ajiyar zuciya tare da furzar da iska kana yace.
“Haka nan dai narasa me nake tunawa awajen nan”.
Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da dafa bayansa kana tace.
“Toh kazo ka zauna mana”.
Girgiza kai yayi tare da fesar da numfashi kana cikin sanyi murya yace.
“Ina ga ko dan garin dana gani da alamun hadari ne ko yaya ne ban sani ba”.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Toh kadawo ka zauna dan Allah tsayuwar tayi yawa”.
Kai ya gyaɗa lokaci ɗaya yaji wani irin masifaffen rauni mai haɗe da bugun zuciya ya rufe sa Atake yaji Idanunsa na tsats-tsafo da ruwan hawaye masu ɗumi yayin da zuciyarsa ya cigaba da tsinkewa jikinsa na mutuwa tamkar ana zare masa laka cikin sanyi jiki yaja ƙafafunsa da yaji sunyi masa mugun nauyi ya zauna akan kujera tare da kwanciya akan 3sitter kana ya lumshe Idanunsa.
Cike da kulawa tace.
“Ya dai lafiya kuwa kashiga ciki mana?”.
Girgiza kai yayi still zuciyarsa na cigaba da bugawa yayinda muryarsa ke ɗauke da rauni yace.
“Please Karima ki barni in kwanta inaji kamar kaina na ciwo”.
Cikin sauri tace.
“Alhj kad dai BP kane?”.
Girgiza kai yayi still Idanunsa na lumshe yace.
“A'a ba BP na bane bari dai mu gani”.
Zama tayi daga hannun kujeran kana tace.
“Toh kasha maganin ka kuwa?”.
Kai ya gyaɗa tare da cewa.
“Eh sosai ma yan zun nan kafin Jameelu ya fita ya bani nasha”.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Eh ƙwarai kuwa hakane toh Allah ya sawwaƙa”.
Ahankali yace.
“Ameen”, Miƙewa tayi tare da shiga Bedroom ɗin sa ta kwanta.
Ɓangaren Moddibo kuwa har Misalin sha biyu da kwata yana zaune dafe da ƙirjinsa dake cigaba da bugawa ahankali ya ɗago kansa tare da shafa gefen wayarsa haske ya bayyana tare da nuna masa ƙarfe 12:15 afili ya furta.
“Har yanzu J bai zoba”.
Yayi mgnar tare da shiga Call log yayi dearling number M Jameel amma ga mamakinsa sai yaji Swich off.
Cikin yanayin damuwa ya dafe kansa tare da cewa.
“Ikon Allah lafiya kuwa wayar J arufe?”.
Kallonsa ya mayar kan babbar wayarsa tare da ɗauka kana ya fito da ɗaya number M Jameel ya kira Shima still Swich off.
Miƙewa tsaye yayi ido a lumshe yace.
“Ha'a ya wayar J akashe kuma dai J baya kashe wayarsa, to amma mai yafaru yau wayarsa akashe toh me yake faruwa bayan ya faɗa min yau zai dawo!?”,l.
Yayi maganar cikin zulumi
“Ya ilahi ya mujabat da'awati, to kuma ko kafin J ya fito sai da ya kirni yace zaije wajen Abba ya sallame sa sannan yazo amma kuma har yanzu bai zoba”.
Atake wata zuciyar tace kasani ko yazo suna tare da Innayi suna can suna ƙus-ƙus atake ya amince da abinda zuciyarsa ya raya masa cikin mutuwar jiki ya nufi ƙofan falonsa tare da buɗewa.
Wani sanyayyan iska ya hurasa ahankali ya ɗaga kansa sama gani yayi hadari ya fara haduwa sai walƙiya dake haskawa can ƙasa alamun yanzu hadarin ya fara, garin ya danyu duhu sakamakon rashin wuta ga kuma hadarin,
ahankali yabi sararin samaniyar da kallo ganin yanda hadarin yayiwa garin zobe kana aƙasan ransa yace to kodai wannan hadarin ne ya hana J zuwa sai kuma yace to kodai yana ɗakin Innayi ya faɗa yana taka step ɗin ahankali.
Cikin sauri Innayi ta haske masa ido da touch light mai masifar haske cikin han zari ya Janye hannuunsa dake danne da J ɗinsa ya tare Idanunsa dashi saboda hasken touchlight daya haska masa ido.
Cike da kulawa Innayi tace.
“Moddibo ya dai lafiya ina zuwa Atsakiyar adaren nan?”.
Ahankali ya sake sakƙowa daga kan step ɗin tare da jingina bayansa da jikin filan barandarsa, kana hannunsa na dama na kan flowes dake gefe yace.
“Kece fa kike ganinsa tsakiyar dare ne, dudu shabiyu da rabi ne fa yanzu”.
Kallonsa tayi tare da cewa.
“Tsakiyar dare ne mana Moddibo yanzu fa ƙarfe shabiyu harda rabi ai tsakiyar dare ne, to amma me kafito yi lafiya dai ko?”.
Cikin sanyin murya yace.
“J ne har yanzu bai zo ba kuma ya fito akan zai zo ma ya kirani awaya kan cewa yanzu zai shiga wajen Abbansa ya masa saida safe ya fito, kuma har yanzu bai iso ba sannan nata kiran layukan sa basa shiga”.
Ya ida maganar akasalance.
Ajiyar zuciya Innayi ta sauƙe tare da cewa.
“Toh dan bai zoba Moddibo ai ba abin tashin hankali bane, kaga yanayin wannan hadarin daya haɗu zai iya hanasa zuwa wataƙil daya shiga wajen Abban nasa zaice dare yayi kuma ga hadari ya bari sai gobe”.
Da sauri ya katseta da cewa.
“To ai Innayi wayarsa bata shiga fa”.
Saurin Kallonsa Innayi tayi tare da cewa.
“Ka kira layinsa duka?”.
Kai ya jinjina mata.
“Eh na kira layukansa duka fa basa shiga”.
Cikin yanayin bacci ta kalli Moddibo tare da sakin hamma kana ta aro Jarumtaka tare da cewa.
“To ko dai network ne?”.
Lumshe Idanunsa yayi tare da Girgiza mata kai kana yace.
“A'a ba network bane cemin akeyi akashe kuma fa Innayi J baya kashe wayarsa, ko zai kwanta komai yaya kuma nasan wayar J baya rasa caji”.
A hankali Innayi ta rufe idonta jin kamar tsinkewar zuciya ya ziyarci ta.
Amma sai ta daure kana tace.
“To amma kaga jiya ma kace min wajen Umminsa ya kwana to ko dai yauma yaje canne ne ya kashe wayarsa dan kada kayi ta kiransa?”.
Jinjina kai yayi tare da faɗin.
“Ok ba mamaki fa bari na kira Ummi”.
Cikin sauri Innayi ta kallesa tare da cewa.
“Aƙarfe ɗaya saura zaka kirasu?”
Kai ya gyaɗa kana yace.
“Eh Innayi in dai har wurin Ummi yake nasan yanzu zasu ganshi kamar takwas na dare ne, saboda nasan yanzu suna hira ba suyi bacci ba.
Kai Innayi ta gyaɗa tare da gyara tsayuwar ta kana tace.
“Toh shikenan ka kira”.
Dearling number Ummi yayu.
Acan ɓangaren Ummi kuwa kwance take yayin da idanunta ke lumshe cikin tsananin tsinkewar zuciya da kasala jin rurin wayarta yasa ta miƙe firgice cikin yanayi sanyi sanya hannunta na dama ta janyo wayar tare da ƙurawa screen ɗin Ido sunan Moddibo ke yawo.
Cikin sauri tare da rawan jiki tayi Picking call ɗin tare da kaiwa Kunnenta batare data amsa Sallamar daya mata ba tace.
“Babana Lafiya?”.
Cikin ƙoƙarin danne damuwarsa yace.
“Ummi lafiya ya naji kamar kin razana?”.
Ahankali ta koma ta jingina bayanta da jikin kushin ɗin tare da lumshe idanunta kana cikin wata raunan'niyar murya mai cike da kasala da tsoro ta fesar da numfashi tare da cewa.
“Gaba ɗaya ma ai. Arazanen nake Babana”.
Moddibo kuwa cikin kasala da mutuwar jiki ya yaja numfashi tare da fesar wa kana yace.
“To Ummi me yafaru?”.
Buɗe Idanunta dake lumshe tayi tare da dafe ƙirjinta da still yake bugawa kana tace.
“Ban saniba amma gaba ɗaya ina jina wani irin gani nan dai kamar mara lfy, kuma ba zance ga abinda yake damuna kai tsaye ba”.
Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe kana yace.
“Toh amma Ummi lafiyar ki lau?”.
Kai ta gyaɗa masa kamar yana gabanta kana tace.
“Lafiya ta ƙalau,Amma Babana lafiya ka kira yanzu?”.
Numfashi ya sauke tare da lumshe idanunsa kana ya sake jingina bayansa da jikin step ɗin tare da cewa.
“Eh lafiya lau babu komai dama zan tambayeki ne ko dai J yazo yana wurinki ne munyi dashi tun ɗazu akan zai zo har yace min gashi ya fito amma zai sallami Abbansa ne kawai ya taho”.
Sai kuma ya lumshe idanunsa tare da cijan lip ɗin sa na ƙasa kana yace.
“Amma har yanzu be taho ba, inata jiran sa ko ƙofar gida bamu rufe ba, shiyasa nace bari na kira koya biya wajenki, da yake jiya ma nan ya kwana!?”.
Rumtse ida nunta tayi da masifar ƙarfi k cikin wani azabebben tsinkewar zuciya da faɗuwar gaba ta buga hannunta na dama aƙirji tare da cewa.
_“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n. Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan min_
bai zo ba kuma yace maka zai zo?
Abbansa kaɗai zai Sallama?”.
Gyaɗa kai Moddibo yayi tamkar yana gabanta kana cikin raunan'niyar murya mai cike da sanyi yace.
“Eh Ummi”.
Cikin wani irin yanayi na taraddadin zuciya da rauni Ummi tace.
“Ya Ubangiji Allah ka dubeni da Idon Rahma. Ya Allah ka tsare wannan bawan naka, aduk inda yake Alfarman Annabi da Alkur'ani”.
Jin salatin da kuma yanayin da Ummi tayi Magana cikin firgici ya farkar da Asma'u, Bashir da Malam Ahmad Aruɗe Asma'u ta miƙe tare da dafe kanta da taji yayi masifar sarawa ta sauƙa daga kan gadon.
Acan ɗakin Bashir kuwa Hasbunallahu wani'imal wakin ya furta tare da sauƙa ƙasa kusan atare suka fito falon ko wannensu zuciyarsa na bugawa da kaso tamanin cikin ɗari.
Moddibo kuwa cikin sanyu da ruɗu yace.
“Ameen ya Allah Ummi ameen ya rabbil Izzati”.
Cikin zulumi Ummi ta runtse Idanunta kana tace.
“Amma Babana ka kira Abbansa mana”.
Numfashi Moddibo ya fesar tare da kallon Innayi data tsaresa da ido cikin yanayin razani yace.
“Eh Ummi nayi tunanin kiran Abbansa amma sai nace bari na fara kiranki tunda jiya yazo na, sannan Ummi nasan J baya kashe wayarsa rashin shigar wayarsa nema yafi damuna!”.
Girgiza kai Ummi tayi yayinda ruwan hawaye masu masifar ɗumi suka cika kwarmin Idanunta kana cikin raunan'niyar murya tace.
“Tabbas baya kashewa ka kira Abbansa kaji”.
Kai ya gyaɗa kana yace.
“Eh dama zan kirasa amma Innayi tace ko Abbansa ne ya hanasa zuwa ganin hadari”.
A hankali tace.
“Anya?,Ka kira sa dai”.
“Amma yanzu dare baiyi ba Ummi”.
Cikin sauri tace.
“A'a ka kira Babana ka kira Abbansa ɗin duk yanda kukayi ka kirani ka sanar min”.
“Toh”.
Moddibo yace kana ya katse kiran.
Hajiya Karima data fito daga Bedroom ɗin sa ta dubesa cike da kulawa tace.
“Ya dai Alhj tun tuni kana tsaye ana ka gaza motsa sama da awa biyu kenan tun bayan fitar motar Jameel kake tsaye lafiya kuwa?”.
Cikin wani irin yanayi ya lumshe idonsa.
Haka nan yaji ruwan hawaye na tsats-tsafo masa a hankali ya sauƙe ajiyar zuciya tare da furzar da iska kana yace.
“Haka nan dai narasa me nake tunawa awajen nan”.
Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da dafa bayansa kana tace.
“Toh kazo ka zauna mana”.
Girgiza kai yayi tare da fesar da numfashi kana cikin sanyi murya yace.
“Ina ga ko dan garin dana gani da alamun hadari ne ko yaya ne ban sani ba”.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Toh kadawo ka zauna dan Allah tsayuwar tayi yawa”.
Kai ya gyaɗa lokaci ɗaya yaji wani irin masifaffen rauni mai haɗe da bugun zuciya ya rufe sa Atake yaji Idanunsa na tsats-tsafo da ruwan hawaye masu ɗumi yayin da zuciyarsa ya cigaba da tsinkewa jikinsa na mutuwa tamkar ana zare masa laka cikin sanyi jiki yaja ƙafafunsa da yaji sunyi masa mugun nauyi ya zauna akan kujera tare da kwanciya akan 3sitter kana ya lumshe Idanunsa.
Cike da kulawa tace.
“Ya dai lafiya kuwa kashiga ciki mana?”.
Girgiza kai yayi still zuciyarsa na cigaba da bugawa yayinda muryarsa ke ɗauke da rauni yace.
“Please Karima ki barni in kwanta inaji kamar kaina na ciwo”.
Cikin sauri tace.
“Alhj kad dai BP kane?”.
Girgiza kai yayi still Idanunsa na lumshe yace.
“A'a ba BP na bane bari dai mu gani”.
Zama tayi daga hannun kujeran kana tace.
“Toh kasha maganin ka kuwa?”.
Kai ya gyaɗa tare da cewa.
“Eh sosai ma yan zun nan kafin Jameelu ya fita ya bani nasha”.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Eh ƙwarai kuwa hakane toh Allah ya sawwaƙa”.
Ahankali yace.
“Ameen”, Miƙewa tayi tare da shiga Bedroom ɗin sa ta kwanta.
Ɓangaren Moddibo kuwa har Misalin sha biyu da kwata yana zaune dafe da ƙirjinsa dake cigaba da bugawa ahankali ya ɗago kansa tare da shafa gefen wayarsa haske ya bayyana tare da nuna masa ƙarfe 12:15 afili ya furta.
“Har yanzu J bai zoba”.
Yayi mgnar tare da shiga Call log yayi dearling number M Jameel amma ga mamakinsa sai yaji Swich off.
Cikin yanayin damuwa ya dafe kansa tare da cewa.
“Ikon Allah lafiya kuwa wayar J arufe?”.
Kallonsa ya mayar kan babbar wayarsa tare da ɗauka kana ya fito da ɗaya number M Jameel ya kira Shima still Swich off.
Miƙewa tsaye yayi ido a lumshe yace.
“Ha'a ya wayar J akashe kuma dai J baya kashe wayarsa, to amma mai yafaru yau wayarsa akashe toh me yake faruwa bayan ya faɗa min yau zai dawo!?”,l.
Yayi maganar cikin zulumi
“Ya ilahi ya mujabat da'awati, to kuma ko kafin J ya fito sai da ya kirni yace zaije wajen Abba ya sallame sa sannan yazo amma kuma har yanzu bai zoba”.
Atake wata zuciyar tace kasani ko yazo suna tare da Innayi suna can suna ƙus-ƙus atake ya amince da abinda zuciyarsa ya raya masa cikin mutuwar jiki ya nufi ƙofan falonsa tare da buɗewa.
Wani sanyayyan iska ya hurasa ahankali ya ɗaga kansa sama gani yayi hadari ya fara haduwa sai walƙiya dake haskawa can ƙasa alamun yanzu hadarin ya fara, garin ya danyu duhu sakamakon rashin wuta ga kuma hadarin,
ahankali yabi sararin samaniyar da kallo ganin yanda hadarin yayiwa garin zobe kana aƙasan ransa yace to kodai wannan hadarin ne ya hana J zuwa sai kuma yace to kodai yana ɗakin Innayi ya faɗa yana taka step ɗin ahankali.
Cikin sauri Innayi ta haske masa ido da touch light mai masifar haske cikin han zari ya Janye hannuunsa dake danne da J ɗinsa ya tare Idanunsa dashi saboda hasken touchlight daya haska masa ido.
Cike da kulawa Innayi tace.
“Moddibo ya dai lafiya ina zuwa Atsakiyar adaren nan?”.
Ahankali ya sake sakƙowa daga kan step ɗin tare da jingina bayansa da jikin filan barandarsa, kana hannunsa na dama na kan flowes dake gefe yace.
“Kece fa kike ganinsa tsakiyar dare ne, dudu shabiyu da rabi ne fa yanzu”.
Kallonsa tayi tare da cewa.
“Tsakiyar dare ne mana Moddibo yanzu fa ƙarfe shabiyu harda rabi ai tsakiyar dare ne, to amma me kafito yi lafiya dai ko?”.
Cikin sanyin murya yace.
“J ne har yanzu bai zo ba kuma ya fito akan zai zo ma ya kirani awaya kan cewa yanzu zai shiga wajen Abbansa ya masa saida safe ya fito, kuma har yanzu bai iso ba sannan nata kiran layukan sa basa shiga”.
Ya ida maganar akasalance.
Ajiyar zuciya Innayi ta sauƙe tare da cewa.
“Toh dan bai zoba Moddibo ai ba abin tashin hankali bane, kaga yanayin wannan hadarin daya haɗu zai iya hanasa zuwa wataƙil daya shiga wajen Abban nasa zaice dare yayi kuma ga hadari ya bari sai gobe”.
Da sauri ya katseta da cewa.
“To ai Innayi wayarsa bata shiga fa”.
Saurin Kallonsa Innayi tayi tare da cewa.
“Ka kira layinsa duka?”.
Kai ya jinjina mata.
“Eh na kira layukansa duka fa basa shiga”.
Cikin yanayin bacci ta kalli Moddibo tare da sakin hamma kana ta aro Jarumtaka tare da cewa.
“To ko dai network ne?”.
Lumshe Idanunsa yayi tare da Girgiza mata kai kana yace.
“A'a ba network bane cemin akeyi akashe kuma fa Innayi J baya kashe wayarsa, ko zai kwanta komai yaya kuma nasan wayar J baya rasa caji”.
A hankali Innayi ta rufe idonta jin kamar tsinkewar zuciya ya ziyarci ta.
Amma sai ta daure kana tace.
“To amma kaga jiya ma kace min wajen Umminsa ya kwana to ko dai yauma yaje canne ne ya kashe wayarsa dan kada kayi ta kiransa?”.
Jinjina kai yayi tare da faɗin.
“Ok ba mamaki fa bari na kira Ummi”.
Cikin sauri Innayi ta kallesa tare da cewa.
“Aƙarfe ɗaya saura zaka kirasu?”
Kai ya gyaɗa kana yace.
“Eh Innayi in dai har wurin Ummi yake nasan yanzu zasu ganshi kamar takwas na dare ne, saboda nasan yanzu suna hira ba suyi bacci ba.
Kai Innayi ta gyaɗa tare da gyara tsayuwar ta kana tace.
“Toh shikenan ka kira”.
Dearling number Ummi yayu.
Acan ɓangaren Ummi kuwa kwance take yayin da idanunta ke lumshe cikin tsananin tsinkewar zuciya da kasala jin rurin wayarta yasa ta miƙe firgice cikin yanayi sanyi sanya hannunta na dama ta janyo wayar tare da ƙurawa screen ɗin Ido sunan Moddibo ke yawo.
Cikin sauri tare da rawan jiki tayi Picking call ɗin tare da kaiwa Kunnenta batare data amsa Sallamar daya mata ba tace.
“Babana Lafiya?”.
Cikin ƙoƙarin danne damuwarsa yace.
“Ummi lafiya ya naji kamar kin razana?”.
Ahankali ta koma ta jingina bayanta da jikin kushin ɗin tare da lumshe idanunta kana cikin wata raunan'niyar murya mai cike da kasala da tsoro ta fesar da numfashi tare da cewa.
“Gaba ɗaya ma ai. Arazanen nake Babana”.
Moddibo kuwa cikin kasala da mutuwar jiki ya yaja numfashi tare da fesar wa kana yace.
“To Ummi me yafaru?”.
Buɗe Idanunta dake lumshe tayi tare da dafe ƙirjinta da still yake bugawa kana tace.
“Ban saniba amma gaba ɗaya ina jina wani irin gani nan dai kamar mara lfy, kuma ba zance ga abinda yake damuna kai tsaye ba”.
Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe kana yace.
“Toh amma Ummi lafiyar ki lau?”.
Kai ta gyaɗa masa kamar yana gabanta kana tace.
“Lafiya ta ƙalau,Amma Babana lafiya ka kira yanzu?”.
Numfashi ya sauke tare da lumshe idanunsa kana ya sake jingina bayansa da jikin step ɗin tare da cewa.
“Eh lafiya lau babu komai dama zan tambayeki ne ko dai J yazo yana wurinki ne munyi dashi tun ɗazu akan zai zo har yace min gashi ya fito amma zai sallami Abbansa ne kawai ya taho”.
Sai kuma ya lumshe idanunsa tare da cijan lip ɗin sa na ƙasa kana yace.
“Amma har yanzu be taho ba, inata jiran sa ko ƙofar gida bamu rufe ba, shiyasa nace bari na kira koya biya wajenki, da yake jiya ma nan ya kwana!?”.
Rumtse ida nunta tayi da masifar ƙarfi k cikin wani azabebben tsinkewar zuciya da faɗuwar gaba ta buga hannunta na dama aƙirji tare da cewa.
_“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n. Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan min_
bai zo ba kuma yace maka zai zo?
Abbansa kaɗai zai Sallama?”.
Gyaɗa kai Moddibo yayi tamkar yana gabanta kana cikin raunan'niyar murya mai cike da sanyi yace.
“Eh Ummi”.
Cikin wani irin yanayi na taraddadin zuciya da rauni Ummi tace.
“Ya Ubangiji Allah ka dubeni da Idon Rahma. Ya Allah ka tsare wannan bawan naka, aduk inda yake Alfarman Annabi da Alkur'ani”.
Jin salatin da kuma yanayin da Ummi tayi Magana cikin firgici ya farkar da Asma'u, Bashir da Malam Ahmad Aruɗe Asma'u ta miƙe tare da dafe kanta da taji yayi masifar sarawa ta sauƙa daga kan gadon.
Acan ɗakin Bashir kuwa Hasbunallahu wani'imal wakin ya furta tare da sauƙa ƙasa kusan atare suka fito falon ko wannensu zuciyarsa na bugawa da kaso tamanin cikin ɗari.
Moddibo kuwa cikin sanyu da ruɗu yace.
“Ameen ya Allah Ummi ameen ya rabbil Izzati”.
Cikin zulumi Ummi ta runtse Idanunta kana tace.
“Amma Babana ka kira Abbansa mana”.
Numfashi Moddibo ya fesar tare da kallon Innayi data tsaresa da ido cikin yanayin razani yace.
“Eh Ummi nayi tunanin kiran Abbansa amma sai nace bari na fara kiranki tunda jiya yazo na, sannan Ummi nasan J baya kashe wayarsa rashin shigar wayarsa nema yafi damuna!”.
Girgiza kai Ummi tayi yayinda ruwan hawaye masu masifar ɗumi suka cika kwarmin Idanunta kana cikin raunan'niyar murya tace.
“Tabbas baya kashewa ka kira Abbansa kaji”.
Kai ya gyaɗa kana yace.
“Eh dama zan kirasa amma Innayi tace ko Abbansa ne ya hanasa zuwa ganin hadari”.
A hankali tace.
“Anya?,Ka kira sa dai”.
“Amma yanzu dare baiyi ba Ummi”.
Cikin sauri tace.
“A'a ka kira Babana ka kira Abbansa ɗin duk yanda kukayi ka kirani ka sanar min”.
“Toh”.
Moddibo yace kana ya katse kiran.