← Book details Sakayyah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 49 OF 114

Sashe 49

Sakayyah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Hararanta Hajja Nana tayi da faɗin.
“Dama kece mai taya ta aikin ina masu taya ta aikin?”.
Zare ido Khausar tayi kana tace.
“Tayi cikin shege ankoreta ta koma ƙauyensu.
Mai gadin muma ana canza shi saboda shi ya mata ciki”.
Da mamaki Hajja Nana tace.
“Ash'sha Subhanallahi ashe gidan naku babu tsaro kenan, ashe ku gidan bayan maita hadda rashin tsaro a'a maza-maza shirya mu tafi”.
Dai-dai lokacin da Mommy ta fito girgiza kai tayi tace.
“Kai Khausar bakyajin magana maza ki ɗauka wa Dije abinci ku wuce ɗakin ki”.

Kai Khausar ta gyaɗa tare da wucewa kichen ta daukawa Dije abincin sannan suka wuce Bedroom ɗin.
Mommy kuwa zama tayi agefen Hajja Nana tare da ajiye mata tiren abinci cikin sanyin murya tace.
“Hajja Nana kiyi haƙuri da halin Khausar zaku tafi idan hakan kike so”.
Kai Hajja Nana ta gyaɗa kana tace.
“Toh babu damuwa amma tace min baki da lafiya da gaske ne?”.

Kai Mommy ta Jinjina kana tace.
“Eh wallahi kwanakin nan duka ban cika jin daɗi ba bansan meke damuna ba!”.
Jinjina kai Hajja Nana tayi kana tace.
“Subhanallah Allah ya sawwaƙa Allah ya yaye.
Kuma da gaske ne mai aikin ku ta haihu cikin shege?".

Dai-dai lokacin Hajiya Bunayya da Amina suka shigo falon.
Ɗaga kai Mommy tayi tare da kallon Hajiya Bunayya data zauna tace.
“Hajiya ga Kakar Khausar”.
Murmushi Hajiya Bunayya tayi Idanunta akan Khausar tace.
“Ai na ganeta Hajja Nana sannu da zuwa ina yini ya gajiya kunzo lafiya?”.

Ita kuwa Amina batare data ƙarasa shiga falon ba ta ɗaga sautin Muryanta da faɗin.
“Khausar!, Khausar!! Khausar!!!,”.
Daga ciki Khausar tace.
“Me?".
Afusace Amina tace.
“Bana son rashin kunya ni zaki yiwa rashin kunya? ina kiranki kina jina ba zaki fito ba aikin san dai tunda na kira ki ina da ɓuƙatar ki!”.
Jin surutan da take yasa Khausar ta fito tare da tsayawa daga bakin ƙofa ta riƙe ƙugunta kana tace.
“To ai tunda ke kike da ɓuƙatata kinsan inda dakina yake sai ki shiga ki sameni”.

Cike da kirsa Hajiya Bunayya tayi dariya tana kallon Khausar tace.
“Kudai in Kun hadu bakwa rabuwa da faɗa kamar wasu ƙananun yara Allah dai ya kawo muku sauƙi kuna na kamar wuta da Auduga”.
Juyawa Hajja Nana tayi ta kalli Khausar da Amina kana ta taɓe baki tare da cewa.
“To ai kinsan haka al'amarin yake, mu zuriyarmu bama gani mu ƙyale sannan bama ji muyi shiru, sannan su kuma mayu haka suke basason mai baki shiyasa baza'ayi shiri ba”.
Hajiya Bunayya tayi saurin cewa.
“Hmmm Hajiya ai tsatsonne na mayu su basu tsotsaba dan mu atsarkake muke”.
Kallon mamaki Mommy tayi mata kana tace.
“Hajiya har ke kin yarda da kalmar kenan?”.
Hajiya Bunayya ta taɓe baki kana tace.
“Ha'a abinda ake faɗa musu acikin gari mun isa mu hana ne?”.
Atake fara'ar dake fuskar Mommy ya gushe cikin rashin jin daɗin abinda Hajiya Bunayya ta faɗa tace.
“Wallahi sukam ba Mayu bane har dake ki yarda kefa komin yaya, ita Uwa ce agareki kuma kakar ’ya'yanki kuma Inde har za'ace suna ciki to mijinki ma yana ciki”.

Hajiya Bunayya kuwa cikin sauri tace.
“A'a mijina atsarkake yake.
Uwarsa kuwa ba zan musan ta mata ba yawwa a duniya idan kaji an cewa mutum maye ba zaka musanta masa ba kawai dai abinda na sani mijina ba yayi nima banayi kuma 'ya'yana na basayi.
Hajja Nana gaskiya kika faɗa taje can ta ƙarata da baƙin halinta inma tanayi can mata inma ba tayi can mata amma abinda gari dai ake faɗa tana yi, kuma mutum bashida hujjar da zaiyi musu akan hakan, gwara ma hujjar da mutum zai ɗabbaga tunda ga alamu ke yanzu ko cikin ki dake yawa zubewa bakya ta Allah ƙashi da ita!?”.

Cikin sauri tare da ɗaure fuska Mommy tace.
“A'a nikam Allah ne ya ƙaddara min zubewar ciki babu wani wanda ya zubar min da ciki”.
Murmushi Hajiya Bunayya tayi aƙasan ranta tace can miki ƙidahuma.

Khausar kuwa kallon mamaki tabi Hajiya Bunayya dashi kana aƙasan ranta tace lalle Hausawa sunyi gaskiya da suka ce iya ruwa fidda kai”.
Amina dake tsaye ta watsa Khausar Harara kana tace.
“Abbah ke kiranki kizo kakar taki tazo da wasu maza suna waje sai kije ku gaisa”.
Ta ida maganar tare da juyawa ta fice.

Ita kuwa khausar cike da farin ciki ta juya ta fice ta nufi coumpund kasa ɓoye fara'ar fuskarta tayi ganin Yaya Aliyu tsaye yaron Baffanta na Adamawa tare da Yaya Abba cikin jin dadi ta ware manyan Idanunta cike da farin ciki tace.
“Yaya Aliyu sannu da zuwa ku ƙara so”.
Ta faɗa tana yin gaba zuwa Falon Lamiɗo dake saukan baki.
Bayan sun shiga falon sun zauna ta dubi Aliyu still Fuskarta da murmushi tace.
“Yaya Aliyu yaushe kazo?".
Gyara zamansa yayi yana fuskantar ta kana fuskarsa ɗauke da murmushi yace.
“Baffanki ne ya tasoni wai sai na kawowa tsohuwar sa kayan azumi shine kuma yanzu Hajja Nana tace sai munzo”.
Khausar kuwa murmushi tayi kana tace.
“Hajja Nana rigima"
Sai kuma ta maida kallonta kan Yaya Abba dake latsa waya tace.
“Yaya Abba ya karatu?”.
Ahankali ya ɗago kansa da murmushi afuskarsa yace.
“Karatu ya ƙare yanzu wannan karon tare zamu tafi da Aliyu can Adamawa idan Allah ya nufa idan munje zan samu aiki Insha Allah tunda kinga Baffan Jimeta yana da hanya da manyan mutane Insha Allah za'a samu”.

aSaki murmushi tayi kana tace.
“Masha Allah abu yayi kyau”.
Lamiɗo ya shigo suka gaisa bayan sun gama gaisawa ya fita, Khausar kuwa Anutse ta miƙe tace.
“Ina zuwa”.
sannan ta fice.
Kai tsaye kichen ɗin su ta nufa ta ɗauko Babban Warmers da faranti ta fita.
Hajja Nana ta bita da kallo baki sake ganin Uban kula me kyau da tsari da tafita dashi.
Ba daɗewa Khausar ta dawo ta sake ɗaukan Flaks da kofuna.

Har takai ƙofa Hajja Nana data kasa haƙuri tace.
“Kede akwai Jaira mara kirki tunda nazo kike wani shan ƙamshi kamar baki so zuwa na ba, ko arzikin gaisuwa ban samu ba bare insa rai da ruwan sha, amma wa'annan saboda 'yan uwanki ne jiki na rawa kin wani kinkimi Uban kula kin fita yanzu kin dawo kin ɗauki Flaks”.
Kallonta Khausar tayi tare da taɓe baki tace.
“Kinga sai anjima Ni sauri nake”.
Tana gama fadar haka ta fice bakinta ɗauke da Sallama tashiga falon.
Amsawa sukayi tare da kallonta.
Zama tayi tare da buɗe Warmers din ta ɗauki babban Plate ta zuba musu shin kafa da miyar da yaji naman kaza sai kuma haɗin coslow kana ta zuba musu shayi dake tururi.
Yaya Abba yayi Murmushi yace.
“Da'alama wannan girkin kine saboda wannan ƙamshi”.
Murmushi tayi amma batace Komai ba.

Acan ɗaki kuwa bayan ankira sallan Azahar Mommy takai Hajja Nana har toilet ɗin ta tayi alwala kana ta fito ta gabatar da Sallah bayan ta idar tayi adduo'i.
Ta juya ta kalli Mommy dake riƙe da carbi ahannunta tace.
“Aisha”.
Cike da girmamawa Mommy tayi ƙasa da kanta kana tace.
“Na'am”
Hajja Nana kuwa gyara zamanta tayi tare da tattara duk kan nutsuwarta zuwa kan Mommy tare da cewa.
“Magana ce mai muhimmanci ta kawoni”.
Cikin girmamawa Mommy da kanta ke ƙasa tace.
“Toh ina sauraronki Hajja Nana”.

Hajja Nana kuwa Ajiyar zuciya ta sauƙe kana tace.
“Magana ce akan Khausar da kuma ɗan Baffanta wato Aliyu”.

Jinjina kai Mommy tayi cike da ladabi tace.
“Toh Hajja Nana ina jinki”.
Hajja Nana ta gyara zamanta tare da cewa.
“Toh zuwa yanzu dai inaga Khausar ta girma, sannan inaga ta gama karatun ta yanzu idan ma bata gama ba to ta kusa”.
Jinjina kai Mommy tayi kana tace.
“Eh ta kusa Insha Allah yanzu kam Shekara ɗaya yarage bayan sallah Insha Allah zata tafi ajin ƙarshe na gama makarantar gaba da primary”.

Cikin jinjina kai Hajja Nana tace.
“Masha Allah Ubangiji ya taimaka”.
Mommy ta amsa da.
“Ameen ya hayyu ya ƙayyum”.
Hajja Nana kuwa duk kan nutsuwarta ta tattara tare da cewa.
“To ai yanzu dai ta samu ta kori jahilci ta yaƙesa, yanzu batun aurenta za'ayi.
Ga kuma Yayanta kuma ɗan Uwanta za'a aura Matashi magana ya ƙare sannan kuma idan karatun take so ta cigaba idan sunyi aure zata yi acan jahar Adamawa tunda suna da makarantu manya-manya acan dan haka yanzu batun aure ne ya kawo mu nazo dashi za'a haɗa bayan sallah in Allah ya yarda”.
Akuma dai-dai lokacin Khausar ta shigo ɗakin, cike ka ɗuwa Idanunta na kan Hajja Nana cikin sauri tace.
“Wai me naji kina cewa?”.
Cikin isa, gadara, Hajja Nana ta wurga mata Harara kana tace.
“Batun Aurenki nakeyi”.
Arazane Khausar ta zare ido kana tace.
“Wa.....!

*GARKUWAR* taku ce dai MA'AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son k’amshi kece raini, da gyaran da zaike maimaita muku dararen forkon kuruciya*

Ko kunsan Jikinmu na da sinadaran hormones da suke taimakawa dan’adam akan komai musamman lokacin da mace take mu’amalar aure da mijinta. Mafi akasari wannan hormones din ne ke samun matsala ko su yi sanyi koma su daina aiki kwata-kwata shi ne dalilin da zai sa mace tace bata jin sha’awa ko bata san dadin aure ba. Albishirinku ina da kayan da ke taimakawa wannan sinadaran du dawo aiki tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara.

Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida.
Chapter 49 · 0% Book details