Sashe 57
Sakayyah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Suna ida shiga gidan suka samu wajen suka zauna Ummi ta miƙe tare da ɗaukar Flaks da kofina ta haɗa musu tea mai kauri yana tururi kana ta zuba musu soyeyyen dankali da ƙwai.
Anutse suka fara ci kaɗan Moddibo yaci ya janye hannunsa daga ciki.
Kallonsa Ummi tayi kana tace.
“Ya dai Babana kaci mana”.
Murmushi Moddibo yayi tare da ɗaura hannunsa na dama akan shafefen cikinsa ya shafa kana yace.
“Ummi na ƙoshi”.
Girgiza kai Ummi tayi tare da cewa.
“Kai Babana me ma kuka ci?”.
Ɗan kwaɓe fuska yayi kana cikin sanyin murya mai kama da shagwaɓa ya lumshe idanunsa tare da cewa.
“Ummi kar muje muna sallah abinci yan fitowa ta hancin mu”.
Kallonsa Ummi tayi tare da murmushi kana tace.
“A'a Babana me ma kuka ci da zai zazzago ta hancinku?”.
Murmushi yayi tare da shafa sajensa zuwa gemunsa kana yace.
“Allah Ummi mun ƙoshi ko ba haka ba J?”.
Kai M Jameel ya gyaɗa tare da Hararan Moddibo ya cire hannunsa a Plate din dan kalin.
Hira suka sake taɓawa kana Moddibo ya miƙe tare da kallon Ummi kana yace.
“Ummi zamu tafi”.
Jinjina kai Ummi tayi tare da cewa.
“Idan kunyi sallah Isha'i zaku dawo ta nan?”.
Girgiza kai Moddibo yayi kana yace.
“A'a Ummi sai wani lokaci”.
Gyaɗa kai tayi tare da cewa.
“Toh ku tafi da kunun nan”.
Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da gyara tsayuwar sa kana yace.
“Toh Ummi ina son kunun abamu zan tafi dashi”.
M Jameel ya juya ya kalli Ummi tare da langwaɓar da kai kana yace.
“Ummi Ni dai ba abani abinda nake so ba”.
Cike da kulawa da kuma so ta juya ta kallesa kana tace.
“Me kake so?”.
Murmushi yayi kana yace.
“Inabin za'a bani in tafi dashi”.
Saurin Kallonsa Moddibo yayi sai kuma ya juya ya kalli Ummi tare da cewa.
“Ummi kar ki basa yasha muna dashi agida”.
Tura baki M Jameel Yayi kana yace.
“Iyeee to na haƙura tunda ba aso ayimin kyautar”.
Ummi Kam murmushi take Cike da ƙaunar su, ji takeyi tamkar su duka biyu a cikinta ta rainesu ta haifesu.
Sallama suka mata kana suka fice suka shiga mota Moddibo ke mazaunin Driver yayin da M Jameel ke gefen mai zaman banza kai tsaye Masallacin da suke limancin na ƙofar gidan Sarki suka nufa sunyi tafiya mai ɗan tsayi kafin suka isa lokacin da suka isa ankira sallar Isha'i suka shiga Moddibo ne yayi limanci suka idar da Isha'i kana sukayi Asham bayan an watse kana suka fito suka shiga mota wannan karon M Jameel ke driving Kai tsaye gidan Innayi suka wuce.
Ƙarfe takwas da rabi suka isa gidan bayan sunyi parking sun fito kai tsaye sashen Innayi suka shiga bakinsu ɗauke da sallama a farfajiyar gidan suka tarar da Innayi da Asma'u zaune Innayi dake gashin nama akan mangal da tarin gawayi agefenta ta daga kanta tare da Kallonsu kana ta amsa Sallamar su.
Ƙara sawa kusa da ita sukayi M Jameel yaja kujera ya Zauna kana ya Kalli Innayi tare da cewa.
“Innayi ya dai mai ake gasa wasa ne?”.
Murmushi Innayi tayi kana tace.
“Nama nake dan gasawa nasanku da cin nama kamar kuraye!”.
Dariya M Jameel Yayi kana yace.
“Aikam Innayi kin kyauta gashi asalin gashi na gargajiya kike yi”.
Kai ta gyaɗa tana ɗaukar Plate tace.
“Eh ai nasanku”.
Ta ida maganar tare da miƙa musu naman data yayyanka ta zuba a Plate tare dasa musu yaji agefe sannan ta yaryara ɗa musu man shanu.
Kallon Asma'u dake yi musu sannu da zuwa tayi kana tace.
“Asms'u ɗauko musu capet su zauna”.
Cikin murza kai gefen dama da hagu Modibbo yace.
“Uhmm Innayi kin dai sanshi shi J ɗinki da son nama kamar kura”.
Murmushi M Jameel yayi dan yasan tabbas Modibbo bai cika damuwa da namaba, asalima in dai gasheshene ko soyayya in dai yaci yanka huɗu zuwa biyar zaice muƙa-muƙinsa sun gaji da taunawa, in kuma dafaffene wani lokaci da haƙorin gaba zai ɗan tattauna in yaji ya gaji sai ya tura masa naman gabansa.
Shi kuwa M Jameel Allah ya sani yana masifar son nama, shi kuwa Moddibo yafi bawa ƴaƴan itatuwa mahimmanci.
Cikin murmushin yace.
“Yoh in ban so namaba me zanso A.J Namafa shine maƙurar daɗi”.
“A wurinka ba, gashi kuma kana son koyamin”.
Cewar Moddibon,
Asma'u kuwa ganin Innayi na kallonta cikin mamakin tace.
“A'a Asma'u ɗauko musu abin zama mana”.
Kai Asma'u ta gyaɗa kana ta miƙe ta shiga falon ta ɗauko capet ɗin ta shimfiɗa musu awajen da yake agyare tass babu alamar ƙazanta.
Zama sukayi akai, Innayi ta sake kallon Asma'u tare da cewa.
“Haɗa musu Tea sannan kisa musu zuma yaji”.
Kai Asma'u ta gyaɗa kana ta miƙe ta zuba musu shayi tare da zuba wadataccen zuma aciki ta kawo musu.
M Jameel kuwa Anutse ya kai yankan naman bakinsa lokaci ɗaya ya lumshe idanunsa tare da buɗe su akan Innayi kana yace.
“Kai gaskiya gashin nan yayi daɗi sosai”.
Murmushi Innayi tayi tare da kallon Moddibo dake cin naman kamar ko yaushe kamar dai dole, yana ɗan taunawa kaɗan-kaɗan cikin kula tace.
“Kai kuma fa Moddibo?”.
Ɗago kansa yayi ya kalleta kana yace.
“Uhm yayi”.
Girgiza kai tayi kana tace.
“Wato kai dai baza ka iya Yabawa ba kenan?”.
Kansa ya sake ɗagowa tare da kallonta kana yace.
“Ai gashinan J ya yaba kuma danɗanon harshen mu ɗaya ne ai”.
Murmushi M Jameel da Asma'u sukayi.
Innayi kuwa baki ta taɓe M Jameel da Moddibo suka cigaba daci Ahankali Moddibo ya ɗago hannunsa tare da kallon tsadedden agogonsa kana ya mayar da Kallonsa kan M Jameel tare da cewa.
“Sai munyi sauri lokaci ya kusa J”.
Kai M Jameel ya gyaɗa tare da cire hannunsa a Plate din kana yace.
“Toh shikenan mu tafi”.
Miƙewa Moddibo yayi tare da kallon Innayi kana yace.
“Bari naje na canza kaya”.
Daga haka ya juya ya nufi sashen sa, shima M Jameel bayansa yabi.
Moddibo nashiga Bedroom ya sauya kayansa zuwa Jallabiya Coffee color tare da ɗaura farin hirami irin na samarin larabawa kana ya feshe jikinsa da turarukansa masu daɗin ƙamshi.
Anutse ya fito falo ya samu M Jameel da shima ya canza kayansa buɗe fridge M Jameel Yayi ya ɗauki goran faro mai sanyi sannan suka jera tare da Moddibo suka sauƙa.
Kai tsaye sashen su Innayi suka koma batare da sun shiga farfajiyar gidan ba .
“Toh Innayi mun tafi”.
Cewar M Jameel
Tana rufe roban yajin da suka ci nama dashi ta ajiye kana tace.
“Toh Allah ya tsare muma yanzu muna bayanku”.
M Jameel na gyara ɗaurin agogon dake tsintsiyar hannunsa ya kalleta kana yace.
“Toh idan za kuje kuzo mu tafi mana sai mu sauƙe ku”.
Girgiza kai tayi tare da cewa.
“Ai akwai Napep zamu hau”.
M Jameel kuwa kai ya Girgiza kana yace.
“A'a ai abin baiyi ba bayan tanan muke tafiya kuma kuce zaki shiga Napep kawai kuzo mutafi”.
Jinjina kai Innayi ta gyaɗa kana tace.
“To bari mu tattara da sauri sai mu tafi”.
“Toh”,M Jameel yace Shi kuwa Moddibo bai ce komai ba sai harɗe hannunsa da yayi aƙirji.
Cikin sauri Innayi da Asma'u suka tattare wajen sannan suka sanya hijabansu kana suka rufe kichen da gidan suka fice abayan Mota suka zauna ita da Asma'u yayin da M Jameel da Moddibo ke gaba.
Suna isa babban masallacin M Jameel yayi Parking Innayi da Asma'u suka fita suka nufi sashen mata su kuma suka shiga cikin masallacin daya cika sosai da al'umma.
Bayan sun zauna Kamar ko yaushe M jameel ya buɗe musu da addu'o'in kana Moddibo ya gyara system ɗin sa tare da ƙara rage girms Idanunsa kana yasa lallausan tafin hannunsa ya gyara zaman microphone din dake gabansa tare dayin gyaran murya cikin sanyayyar sautin muryansa ya fara kamar haka:
_“Auzubillahi Minal Shaiɗanir Rajim, Bismillahir Rahmanir Rahim.
(10) Innalazina ya'akuluna, Amwalal yatama zhulman innama ya'akuluna fiy buɗunihim naraa,wasayaslauna sa'irah”._
Jama'ar dake wajen masallacin cikin sassarfa suka ƙaraso cikin masallacin dan basa so koda harafi ɗaya ne su rasa daga cikin karatun Moddibo saboda baiwar muryarsa.
Moddibo kuwa sanyayyar numfashi ya fesar tare da jingina bayansa da kujeran kana ya cigaba kamar haka:
_“(11)Yusikumullahu fii auladikum,Lilzikri mislu hazzil unsaynan.Fa'in kunna Nisa'a fauƙasnatayni falahunna sulusa ma tarak,Wa'in kanat wahidatan falahannisf,Wali abwayhi likulli wahidin Minhumassudusu,Mimma taraka inkana lahuu waladun,Fa'in lam yakun lahu waladu wawarisahuuu abwahu fali ummihi sulus.Fa'in kana lahu Ikhwatun fali ummihi sudus min ba'adi wasiyyatin yusi biha audayn,abaukum wa'abna ukum latadruna ayyuhum aƙrabuna lakum naf',a,Faridatan Minallah,Innalaha kana aliman hakima”._
Ya dire ayar tare da jan numfashin sa da ya riƙe.
Jinjina kai M Jameel Yayi yayinda ayoyin ke ratsa sa cikin yanayin sakewa ya lumshe idanu kana yace.
“Aya ta gaba”.
Jinjina kai Moddibo yayi kana cikin zazzaƙan muryansa mai sanyi da ratsa jiki kana da nutsuwa ya cigaba da jan ayoyin saida ya kai aya ta Ashirin kana ya tsaya.
Shi kuwa M Jameel Cike da tsantsar ƙwarewa da nutsuwa kana da sanin makaman tafsir ya fara fassara ayoyin tare da cikekken kaddima da kowa amintattun haɗisai da suka da munasaba da ayoyin harma da sababul nuzur na ayoyi, lokacin ɗaya cikin masallacin ya sake samun nutsuwa tafsirin na ratsa su.
Ƙarfe goma dai-dai suka tashi tafsir ɗin mata suka fara fita ta ɓangarensu kafin maza suka fita acikin mota Asma'u da Innayi suka jira M Jameel da Moddibo goma da kwata dai-dai suka fito suka tafi.
Acan ɓangaren Khausar kuwa yauma kamar kullum taje tafsiri ita kaɗai ta dawo duk da masallacin a ƙofar gidansu yake bakinta ɗauke da Sallama tashiga cikin falonsu Anutse ta cire hijabinta tare da nufar kichen inda take jiyo motsin Mommyta kasancewar yau itace da girki yasa ko tafsir bata jeba.
Anutse suka fara ci kaɗan Moddibo yaci ya janye hannunsa daga ciki.
Kallonsa Ummi tayi kana tace.
“Ya dai Babana kaci mana”.
Murmushi Moddibo yayi tare da ɗaura hannunsa na dama akan shafefen cikinsa ya shafa kana yace.
“Ummi na ƙoshi”.
Girgiza kai Ummi tayi tare da cewa.
“Kai Babana me ma kuka ci?”.
Ɗan kwaɓe fuska yayi kana cikin sanyin murya mai kama da shagwaɓa ya lumshe idanunsa tare da cewa.
“Ummi kar muje muna sallah abinci yan fitowa ta hancin mu”.
Kallonsa Ummi tayi tare da murmushi kana tace.
“A'a Babana me ma kuka ci da zai zazzago ta hancinku?”.
Murmushi yayi tare da shafa sajensa zuwa gemunsa kana yace.
“Allah Ummi mun ƙoshi ko ba haka ba J?”.
Kai M Jameel ya gyaɗa tare da Hararan Moddibo ya cire hannunsa a Plate din dan kalin.
Hira suka sake taɓawa kana Moddibo ya miƙe tare da kallon Ummi kana yace.
“Ummi zamu tafi”.
Jinjina kai Ummi tayi tare da cewa.
“Idan kunyi sallah Isha'i zaku dawo ta nan?”.
Girgiza kai Moddibo yayi kana yace.
“A'a Ummi sai wani lokaci”.
Gyaɗa kai tayi tare da cewa.
“Toh ku tafi da kunun nan”.
Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da gyara tsayuwar sa kana yace.
“Toh Ummi ina son kunun abamu zan tafi dashi”.
M Jameel ya juya ya kalli Ummi tare da langwaɓar da kai kana yace.
“Ummi Ni dai ba abani abinda nake so ba”.
Cike da kulawa da kuma so ta juya ta kallesa kana tace.
“Me kake so?”.
Murmushi yayi kana yace.
“Inabin za'a bani in tafi dashi”.
Saurin Kallonsa Moddibo yayi sai kuma ya juya ya kalli Ummi tare da cewa.
“Ummi kar ki basa yasha muna dashi agida”.
Tura baki M Jameel Yayi kana yace.
“Iyeee to na haƙura tunda ba aso ayimin kyautar”.
Ummi Kam murmushi take Cike da ƙaunar su, ji takeyi tamkar su duka biyu a cikinta ta rainesu ta haifesu.
Sallama suka mata kana suka fice suka shiga mota Moddibo ke mazaunin Driver yayin da M Jameel ke gefen mai zaman banza kai tsaye Masallacin da suke limancin na ƙofar gidan Sarki suka nufa sunyi tafiya mai ɗan tsayi kafin suka isa lokacin da suka isa ankira sallar Isha'i suka shiga Moddibo ne yayi limanci suka idar da Isha'i kana sukayi Asham bayan an watse kana suka fito suka shiga mota wannan karon M Jameel ke driving Kai tsaye gidan Innayi suka wuce.
Ƙarfe takwas da rabi suka isa gidan bayan sunyi parking sun fito kai tsaye sashen Innayi suka shiga bakinsu ɗauke da sallama a farfajiyar gidan suka tarar da Innayi da Asma'u zaune Innayi dake gashin nama akan mangal da tarin gawayi agefenta ta daga kanta tare da Kallonsu kana ta amsa Sallamar su.
Ƙara sawa kusa da ita sukayi M Jameel yaja kujera ya Zauna kana ya Kalli Innayi tare da cewa.
“Innayi ya dai mai ake gasa wasa ne?”.
Murmushi Innayi tayi kana tace.
“Nama nake dan gasawa nasanku da cin nama kamar kuraye!”.
Dariya M Jameel Yayi kana yace.
“Aikam Innayi kin kyauta gashi asalin gashi na gargajiya kike yi”.
Kai ta gyaɗa tana ɗaukar Plate tace.
“Eh ai nasanku”.
Ta ida maganar tare da miƙa musu naman data yayyanka ta zuba a Plate tare dasa musu yaji agefe sannan ta yaryara ɗa musu man shanu.
Kallon Asma'u dake yi musu sannu da zuwa tayi kana tace.
“Asms'u ɗauko musu capet su zauna”.
Cikin murza kai gefen dama da hagu Modibbo yace.
“Uhmm Innayi kin dai sanshi shi J ɗinki da son nama kamar kura”.
Murmushi M Jameel yayi dan yasan tabbas Modibbo bai cika damuwa da namaba, asalima in dai gasheshene ko soyayya in dai yaci yanka huɗu zuwa biyar zaice muƙa-muƙinsa sun gaji da taunawa, in kuma dafaffene wani lokaci da haƙorin gaba zai ɗan tattauna in yaji ya gaji sai ya tura masa naman gabansa.
Shi kuwa M Jameel Allah ya sani yana masifar son nama, shi kuwa Moddibo yafi bawa ƴaƴan itatuwa mahimmanci.
Cikin murmushin yace.
“Yoh in ban so namaba me zanso A.J Namafa shine maƙurar daɗi”.
“A wurinka ba, gashi kuma kana son koyamin”.
Cewar Moddibon,
Asma'u kuwa ganin Innayi na kallonta cikin mamakin tace.
“A'a Asma'u ɗauko musu abin zama mana”.
Kai Asma'u ta gyaɗa kana ta miƙe ta shiga falon ta ɗauko capet ɗin ta shimfiɗa musu awajen da yake agyare tass babu alamar ƙazanta.
Zama sukayi akai, Innayi ta sake kallon Asma'u tare da cewa.
“Haɗa musu Tea sannan kisa musu zuma yaji”.
Kai Asma'u ta gyaɗa kana ta miƙe ta zuba musu shayi tare da zuba wadataccen zuma aciki ta kawo musu.
M Jameel kuwa Anutse ya kai yankan naman bakinsa lokaci ɗaya ya lumshe idanunsa tare da buɗe su akan Innayi kana yace.
“Kai gaskiya gashin nan yayi daɗi sosai”.
Murmushi Innayi tayi tare da kallon Moddibo dake cin naman kamar ko yaushe kamar dai dole, yana ɗan taunawa kaɗan-kaɗan cikin kula tace.
“Kai kuma fa Moddibo?”.
Ɗago kansa yayi ya kalleta kana yace.
“Uhm yayi”.
Girgiza kai tayi kana tace.
“Wato kai dai baza ka iya Yabawa ba kenan?”.
Kansa ya sake ɗagowa tare da kallonta kana yace.
“Ai gashinan J ya yaba kuma danɗanon harshen mu ɗaya ne ai”.
Murmushi M Jameel da Asma'u sukayi.
Innayi kuwa baki ta taɓe M Jameel da Moddibo suka cigaba daci Ahankali Moddibo ya ɗago hannunsa tare da kallon tsadedden agogonsa kana ya mayar da Kallonsa kan M Jameel tare da cewa.
“Sai munyi sauri lokaci ya kusa J”.
Kai M Jameel ya gyaɗa tare da cire hannunsa a Plate din kana yace.
“Toh shikenan mu tafi”.
Miƙewa Moddibo yayi tare da kallon Innayi kana yace.
“Bari naje na canza kaya”.
Daga haka ya juya ya nufi sashen sa, shima M Jameel bayansa yabi.
Moddibo nashiga Bedroom ya sauya kayansa zuwa Jallabiya Coffee color tare da ɗaura farin hirami irin na samarin larabawa kana ya feshe jikinsa da turarukansa masu daɗin ƙamshi.
Anutse ya fito falo ya samu M Jameel da shima ya canza kayansa buɗe fridge M Jameel Yayi ya ɗauki goran faro mai sanyi sannan suka jera tare da Moddibo suka sauƙa.
Kai tsaye sashen su Innayi suka koma batare da sun shiga farfajiyar gidan ba .
“Toh Innayi mun tafi”.
Cewar M Jameel
Tana rufe roban yajin da suka ci nama dashi ta ajiye kana tace.
“Toh Allah ya tsare muma yanzu muna bayanku”.
M Jameel na gyara ɗaurin agogon dake tsintsiyar hannunsa ya kalleta kana yace.
“Toh idan za kuje kuzo mu tafi mana sai mu sauƙe ku”.
Girgiza kai tayi tare da cewa.
“Ai akwai Napep zamu hau”.
M Jameel kuwa kai ya Girgiza kana yace.
“A'a ai abin baiyi ba bayan tanan muke tafiya kuma kuce zaki shiga Napep kawai kuzo mutafi”.
Jinjina kai Innayi ta gyaɗa kana tace.
“To bari mu tattara da sauri sai mu tafi”.
“Toh”,M Jameel yace Shi kuwa Moddibo bai ce komai ba sai harɗe hannunsa da yayi aƙirji.
Cikin sauri Innayi da Asma'u suka tattare wajen sannan suka sanya hijabansu kana suka rufe kichen da gidan suka fice abayan Mota suka zauna ita da Asma'u yayin da M Jameel da Moddibo ke gaba.
Suna isa babban masallacin M Jameel yayi Parking Innayi da Asma'u suka fita suka nufi sashen mata su kuma suka shiga cikin masallacin daya cika sosai da al'umma.
Bayan sun zauna Kamar ko yaushe M jameel ya buɗe musu da addu'o'in kana Moddibo ya gyara system ɗin sa tare da ƙara rage girms Idanunsa kana yasa lallausan tafin hannunsa ya gyara zaman microphone din dake gabansa tare dayin gyaran murya cikin sanyayyar sautin muryansa ya fara kamar haka:
_“Auzubillahi Minal Shaiɗanir Rajim, Bismillahir Rahmanir Rahim.
(10) Innalazina ya'akuluna, Amwalal yatama zhulman innama ya'akuluna fiy buɗunihim naraa,wasayaslauna sa'irah”._
Jama'ar dake wajen masallacin cikin sassarfa suka ƙaraso cikin masallacin dan basa so koda harafi ɗaya ne su rasa daga cikin karatun Moddibo saboda baiwar muryarsa.
Moddibo kuwa sanyayyar numfashi ya fesar tare da jingina bayansa da kujeran kana ya cigaba kamar haka:
_“(11)Yusikumullahu fii auladikum,Lilzikri mislu hazzil unsaynan.Fa'in kunna Nisa'a fauƙasnatayni falahunna sulusa ma tarak,Wa'in kanat wahidatan falahannisf,Wali abwayhi likulli wahidin Minhumassudusu,Mimma taraka inkana lahuu waladun,Fa'in lam yakun lahu waladu wawarisahuuu abwahu fali ummihi sulus.Fa'in kana lahu Ikhwatun fali ummihi sudus min ba'adi wasiyyatin yusi biha audayn,abaukum wa'abna ukum latadruna ayyuhum aƙrabuna lakum naf',a,Faridatan Minallah,Innalaha kana aliman hakima”._
Ya dire ayar tare da jan numfashin sa da ya riƙe.
Jinjina kai M Jameel Yayi yayinda ayoyin ke ratsa sa cikin yanayin sakewa ya lumshe idanu kana yace.
“Aya ta gaba”.
Jinjina kai Moddibo yayi kana cikin zazzaƙan muryansa mai sanyi da ratsa jiki kana da nutsuwa ya cigaba da jan ayoyin saida ya kai aya ta Ashirin kana ya tsaya.
Shi kuwa M Jameel Cike da tsantsar ƙwarewa da nutsuwa kana da sanin makaman tafsir ya fara fassara ayoyin tare da cikekken kaddima da kowa amintattun haɗisai da suka da munasaba da ayoyin harma da sababul nuzur na ayoyi, lokacin ɗaya cikin masallacin ya sake samun nutsuwa tafsirin na ratsa su.
Ƙarfe goma dai-dai suka tashi tafsir ɗin mata suka fara fita ta ɓangarensu kafin maza suka fita acikin mota Asma'u da Innayi suka jira M Jameel da Moddibo goma da kwata dai-dai suka fito suka tafi.
Acan ɓangaren Khausar kuwa yauma kamar kullum taje tafsiri ita kaɗai ta dawo duk da masallacin a ƙofar gidansu yake bakinta ɗauke da Sallama tashiga cikin falonsu Anutse ta cire hijabinta tare da nufar kichen inda take jiyo motsin Mommyta kasancewar yau itace da girki yasa ko tafsir bata jeba.