Sashe 31
Sakayyah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kai Moddibo ya jujjuya tare da yar kwaffa hana yace.
“Toh ba matsala ai ka'ida iyayen yara.
Yau kuma mai yasami motar ta lalace ne? Ko kuma sa maine bazaka iya ba”.
Yana mai laluben aljihunsa yace.
“Duka biyu, ta lalacen kuma yau du-du-du da naira ashirin da biyar na tashi”.
Kai Moddibo ya sunkuyar yana mai kallon wayarshi yace.
“Kuma har ina Rugar Jauro Yaya yake da nisa ne!?”.
Da sauri Malam Arɗo Yace.
“Koma da nisa kai zaka kaini dan badan ka matsa min akan gyaran makarantar nan ba da wataƙil in canza mota kuma da ko ban canza a ai bazan rasa kuɗin da mai ba”.
Murmushi Moddibo yayi kana yace.
“Dama wataƙil ne Malam koba ayi gyaran makaranta ba da wuya ka canza wannan motar.
Dariya Hajiya Zainabu tayi tace.
“Aikam Moddibo ka faɗi gaskiya”.
Anutse Moddibo yace.
“Koma dai menene dan Allah Malam ayi ƙoƙari asa musu kujeru dubi fa ba laida ba Capet ba kujere ba tiles sai siminti kawai dan Allah ka daure kasamu tiles da kujeru”.
Murmushi Hajiya Zainabu tayi tare da yiwa Moddibo alamar jinjina da hannu kana tace.
“Allah ya maka albarka”.
Tayi maganar yanda Malam Arɗo ba zai jiba.
Kai Malam Arɗo ya gyaɗa da faɗin.
“Naji wuce muje".
Taɓe baki Moddibo yayi kana suka fita.
Ɗakin Uwar gidan Malam Arɗo suka shiga mai suna Hajiya Ramatu,
Kwance suka same ta akan faranda ta shimfiɗa ta burma.
Gefenta Moddibo ya ɗan zauna bisa dakalin dake mazaunin Mlma Arɗo cikin mutuntaka yace.
“Ina kwana Hajiya ya jikin?”.
“Da sauƙi Moddibo ya ƙoƙari?”.
Tace tana mai kallonsa, kauda kansa yayi tare da cewa.
“Alhamdulillah”. yana miƙewa.
Yace.
“Ai dole ma sanyi yata kamaku ba Capet ba kujeru asanyin garin nan kam dan Allah Malam asamu kujeru inba haka ba zasu ta cutuwa sanyi zaita kamasu sannan ya batun fitar da ita wajen?”.
Tsaresa da Ido Malam Arɗo yayi kafin yace.
“Moddibo! Moddibo!! Moddibo Kafita idona baka iya lissafin komai ba sai lissafin yanda za'a cinye min kuɗina ko”.
Shi kuwa Moddibo kai ya karya kana cikin sanyi yace.
“Ai gaskiya ne Malam ita lafiyar nan dole aneme ta”.
Harara ya galla masa tare da faɗin.
“Ai mun gama magana da Basiru na basa kuɗin da zai isa".
Shi kuwa Moddibo kai ya jinjina yace.
Malam munyi magana da Basheer kuɗin ba zai isa ba Malam fita waje fa ba abune mai sauƙi ba”.
Saurin Kallonsa Malam Arɗo yayi yace.
“Na fahimta wato har ƙarana suke kaiwa wajenka to kaiɗin Ubana ne da zaka sani inyi!?”.
Murmushin gefen baki Moddibo yayi wanda ke ƙarawa fuskarsa kyau yace.
“A'a Malam niba Babanka bane ai shawara ce dai”.
Shi kuwa Malam Arɗo kai ya gyaɗa yace.
“Toh shikenan naji zanyi”.
Sallama Moddibo yayi wa Hajiya Ramatu sannan suka wuce ɗakin Malam Arɗo.
Kallon Moddibo Malam Arɗo yayi yace.
“Ya batun ƙara school fees ɗin yaran nan?”.
Shi ma Moddibo Kallonsa yayi kafin yace.
“Malam duk gyaran makarantar nan da akayi a asusun makaranta akayi school fees ɗin yaran yayi dan angyara makaranta baya nufin sai anƙarawa ɗalibai school fees zaka kashe makarantar ida kuɗin yayi yawa”.
Baki Malam Arɗo ya cuna har Moddibo ya ida magana sai kuma yace.
“In kashe makaranta fa kace?
Bayan na gyara makaranta sannan kuma ga lafiyayyun malamai masu ilimi yara suna samun wadataccen ilimi ko za'a samu ilimi abanza ne? zan ƙara school fees Tabbas zan ƙara”.
Murmushi Moddibo yayi yace.
“Toh shikenan kamar nawa za'a ƙara?".
Sai asannan Malam Arɗo yayi Murmushi yace.
“Za'a ƙarawa ko wani ɗalibi dubu Ashirin”.
Wara ido Moddibo yayi yace.
“Innalillahi gaskiya Malam yayi yawa inma za'a ƙara ya kama dole to bazai wuce aƙara dubu biyar biyar za'a ƙara shima saboda za’a ƙara sabbin malamai ne da kuma sabbin tsare-tsare”.
Kai Malam Arɗo ya jinjina yace.
“Toh shikenan tunda ka matsa zan barshi ahaka”.
Zama Moddibo ya gyara yace.
“Akwai kuma maganar tafiya musabaƙa na gasar hadda da za'ayi za'aje Noka”.
Kai Malam Arɗo ya gyaɗa da faɗin.
“Wannan ba matsala ashirya komai”.
Murmushin gefen baki Moddibo ya kumayi idanunsa akan Malam Arɗo yace.
“Eh badamuwa Malam wato tunda kasan wannan iyayen yarane zasu biya kuɗin motar da sungulla da komai”.
Dariya Malam Arɗo yayi yace.
“Atoh ainima dai ina ƙoƙari tunda motoci makarantar nanne ake tafiya dasu ko”.
Kai Moddibo ya jinjina yace.
“Ai Malam, Ƙarfe nawa zamu tafi can jauro yayan sannan mai zakaje yi?”.
Cikin sanyi yace.
“Wata Rugar Fulani ce amma gaskiya akwai tafiya zamu tafi da yanzu tun da kaga ƙarfe tara zuwa sha ɗaya zamu isa Insha Allah,Yawanci ina zuwa karatu can wajen wani Malam Aliyu limamin Rugar tasu sannan kuma anyi masa rasuwa shine nakeso Inje inyi masa ta'aziyya to kaga motata ta samu matsala”.
Jinjina kai Moddibo yayi da faɗin.
“Allah yajiƙan musulmi toh ba matsala muje tunda dama yanzu babu abinda nake yi, amma dai zamu dawo da wuri ko tunda kasan akwai ‘yan hadda?”.
Kai Malam Arɗo ya gyaɗa yace.
Toh ba matsala Allah dai ya kaimu lafiya”.
“Amin”. Yace
Sannan ya miƙe suka shiga mota suka fice kasancewar Ashirye suke.
Moddibo kuwa ƙira'ar Sheykh Jabeer ya kunna suna tafiya yana saurara tare da bin bakinsa tafiya mai ɗan nisa sukayi a haka.
Malam Arɗo ne ya katse shirun da faɗin.
“Gaskiya wannan tsarin ginin Makarantar yayi kyau Moddibo kayi ƙoƙari”.
Murmushi Moddibo yayi yace.
“Uhum Masha Allah”.
Haka suka cigaba da tafiya suna taɓa hira jefi-jefi wanda mafi yawan hiran Malam Arɗo keyi shi dai Moddibo daga Uhm sai um-um. Koko yace Masha Allah ko Alhamdulillah.
Suna dosan Rugar Moddibo yaga wajen kamar Rafi hayaƙi na tasowa lokaci ɗaya wani irin sanyi mai ratsa jiki ya ratsa gaba ɗaya ilahirin jikinsa Atake ya lumshe idanunsa tare da cije laɓɓansa na ƙasa.
Ahankali ya juya ya kalli malam Arɗo yace.
“Kai Malam garin nan akwai sanyi”.
Murmushi malam Arɗo yayi yace.
“Sosai ma kuwa garin akwai sanyi”.
Kai ya jinjina tare da jan numfashi kana ya fesar da huci mai ɗan karen ɗumi.
Dai-dai lokacin yayi parking a ƙofar gidan malam liman kana yana motsa laɓɓansa alamar Tasbihi yake.
“Subahanallahi”. Ya furta a hankali sabida tsarin garin yayi matuƙar ratsa shi.
Yaya Abba da shigowarsa kenan ya isa garesu tare da miƙawa Moddibo hannu sukayi musabaha kana yace.
“Sannun ku da zuwa fatan kunzo lafiya?”
Kai Moddibo ya gyaɗa da faɗin.
“Alhamdulillah".
Kallon Malam Arɗo Yaya Abba yayi yace.
“Tsoho mai ran ƙarfe”.
Murmushi Malam Arɗo yayi da faɗin.
“Ya akayi ɗan saurayi”.
Cikin alamun sanayya yayi musu jagora, har cikin ɗakin Malam Liman.
Cike da mutuntaka daddataku Malam Liman yake musu marhabin da zuwa.
“A'a Malam Arɗo kaine tafe, sannu da zuwa, on laleko mon njabɓa ma mon laleko bagare”.
Sai kuma ya juyo ya kalli
Yaya Abba kana yace.
“Jeka kawo musu abin taɓa wa”.
Kai yaya Abba ya gyaɗa sannan ya miƙe ya shiga cikin gida.
Ba jimawa ya dawo hannunsa riƙe da Akwashi guda biyu akan faranti sannan ya koma ya sake ɗauko kofi guda biyu ya buɗe akwashin daya fi girma Gashesh-shen naman ragone da aka masa gashin ruwa ruwa yayin da ɗaya akwashin ke ɗauke da madaran shanu mai ɗumi Yaya Abba yace.
“Bismilla kuci”.
Bai jira jin mai zasu ceba ya miƙe yabar wajen.
Shi kuwa Moddibo lumshe idanunsa yayi sakamakon ƙamahin naman daya ratsa hancinsa da kuma yanda gashin yayi kyau a ido da farko baiyi niyyan ciba amma ganin yanda gidan yake atsaftace da kuma masu gidan ga wani irin ƙamshi dake tashi yasa ya fara cin naman cikin nutsuwa tare da zuba madaran sosai yaci dan baƙaramin daɗi naman yayi ba, gashi dama baiyi breakfast ba.
Malam Arɗo ma sosai yaci sannan yasha madaran wanda shi kuwa kirtansa ke hamada ci sai yazo nan yake kashe tsatsan haƙoransa shiyasa ba cika fashin zuwa duk wata yana zuwa sai biyu.
Bayan sun kammala ne Malam Liman yashigo ya zauna daga gefen Malam Arɗo ya bashi hannu sukayi musabaha.
Malam Arɗo yace.
“Fatan mun same ku lafiya ya kuma muka ji da ƙarin haƙuri?”.
Kai Malam Liman gyaɗa tare da faɗin.
“Hakuri mungode Allah”.
Malam Arɗo yace.
“Allah ya jiƙansa da rahma da kuma dukkan musulman da suka rigamu gidan gaskiya”.
“Ameen ya hayyu ya ƙayyum”.
ya amsa.
Shima Moddibo cike da girmamawa yace.
“Malam ya mukaji da haƙuri Ubangiji Allah ya jikansa da Rahman Allah ya haskaka makwancinsa”.
Malam Liman ya amsa da.
“Ameen”.
Baffa Liman ya kalli Malam Arɗo yace.
“Muje ka gaida Babbar Addarmu wacce take madadin mahaifiyarmu”.
Kai Malam Arɗo ya gyaɗa kana yace.
“Toh ba matsala muje”.
Ya ida Maganar suna miƙewa.
Baffa Liman da malam Arɗo na gaba yayin da Moddibo da yaya Abba ke bayansu Moddibo na ƙarewa yanayin garin kallon sosai garin ya burgesa ko ina ka duba tsaf-tsaf babu alamar ƙazanta ko datti.
Bakinsu ɗauke da Sallama suka shiga gidan Hajja Nana lokacin tana zaune atsakar gidan kan ta burma.
Baffa Liman ya kalli Hajja Nana yace.
“Ga Yayana kuma ɗalibina yazo zai gaisheki”.
Tace.
“Ayyah sannunku da zuwa”.
Sannan ta miƙe ta shimfiɗa musu darduma dake tsaf dashi babu alamar datti ajiki komai na gidanta tsaf babu datti duk da stufanta amma komai nata tsaf yake.
Sosai garin da mutanen garin suka burge Moddibo komai na garin akimtse.
Gaisawa sukayi da Hajja Nana sannan suka yi mata ta'aziyya madara mai ɗumi tasa aka kawo musu. Koda sukace Alhamdulillah fir tace dolefa susha ita baƙo baya zuwa wurinta ya fita baici komaiba.
Madarar kawai Moddibo yasha kasancewar ya ƙoshi agidan malam Liman Aransa kuwa sai yaba karamci da dattakon mutanen yake.
Aɓangaren Khausar kuwa tana can rafi tare da Dije da Sadik sunje ɗiban ƙwan Zabbi da kuma kayan lambu dake hannun Khausar bayan sun gama suka fito kallon Sadik da Dije Khausar tayi tace.
“Tunda wayar yaya Abba na hannu na zanje Bishiyar ƙare zancenka in Kira Mommy na”.
Kai suka gyaɗa mata da faɗin.
“Muje toh”.
“Toh ba matsala ai ka'ida iyayen yara.
Yau kuma mai yasami motar ta lalace ne? Ko kuma sa maine bazaka iya ba”.
Yana mai laluben aljihunsa yace.
“Duka biyu, ta lalacen kuma yau du-du-du da naira ashirin da biyar na tashi”.
Kai Moddibo ya sunkuyar yana mai kallon wayarshi yace.
“Kuma har ina Rugar Jauro Yaya yake da nisa ne!?”.
Da sauri Malam Arɗo Yace.
“Koma da nisa kai zaka kaini dan badan ka matsa min akan gyaran makarantar nan ba da wataƙil in canza mota kuma da ko ban canza a ai bazan rasa kuɗin da mai ba”.
Murmushi Moddibo yayi kana yace.
“Dama wataƙil ne Malam koba ayi gyaran makaranta ba da wuya ka canza wannan motar.
Dariya Hajiya Zainabu tayi tace.
“Aikam Moddibo ka faɗi gaskiya”.
Anutse Moddibo yace.
“Koma dai menene dan Allah Malam ayi ƙoƙari asa musu kujeru dubi fa ba laida ba Capet ba kujere ba tiles sai siminti kawai dan Allah ka daure kasamu tiles da kujeru”.
Murmushi Hajiya Zainabu tayi tare da yiwa Moddibo alamar jinjina da hannu kana tace.
“Allah ya maka albarka”.
Tayi maganar yanda Malam Arɗo ba zai jiba.
Kai Malam Arɗo ya gyaɗa da faɗin.
“Naji wuce muje".
Taɓe baki Moddibo yayi kana suka fita.
Ɗakin Uwar gidan Malam Arɗo suka shiga mai suna Hajiya Ramatu,
Kwance suka same ta akan faranda ta shimfiɗa ta burma.
Gefenta Moddibo ya ɗan zauna bisa dakalin dake mazaunin Mlma Arɗo cikin mutuntaka yace.
“Ina kwana Hajiya ya jikin?”.
“Da sauƙi Moddibo ya ƙoƙari?”.
Tace tana mai kallonsa, kauda kansa yayi tare da cewa.
“Alhamdulillah”. yana miƙewa.
Yace.
“Ai dole ma sanyi yata kamaku ba Capet ba kujeru asanyin garin nan kam dan Allah Malam asamu kujeru inba haka ba zasu ta cutuwa sanyi zaita kamasu sannan ya batun fitar da ita wajen?”.
Tsaresa da Ido Malam Arɗo yayi kafin yace.
“Moddibo! Moddibo!! Moddibo Kafita idona baka iya lissafin komai ba sai lissafin yanda za'a cinye min kuɗina ko”.
Shi kuwa Moddibo kai ya karya kana cikin sanyi yace.
“Ai gaskiya ne Malam ita lafiyar nan dole aneme ta”.
Harara ya galla masa tare da faɗin.
“Ai mun gama magana da Basiru na basa kuɗin da zai isa".
Shi kuwa Moddibo kai ya jinjina yace.
Malam munyi magana da Basheer kuɗin ba zai isa ba Malam fita waje fa ba abune mai sauƙi ba”.
Saurin Kallonsa Malam Arɗo yayi yace.
“Na fahimta wato har ƙarana suke kaiwa wajenka to kaiɗin Ubana ne da zaka sani inyi!?”.
Murmushin gefen baki Moddibo yayi wanda ke ƙarawa fuskarsa kyau yace.
“A'a Malam niba Babanka bane ai shawara ce dai”.
Shi kuwa Malam Arɗo kai ya gyaɗa yace.
“Toh shikenan naji zanyi”.
Sallama Moddibo yayi wa Hajiya Ramatu sannan suka wuce ɗakin Malam Arɗo.
Kallon Moddibo Malam Arɗo yayi yace.
“Ya batun ƙara school fees ɗin yaran nan?”.
Shi ma Moddibo Kallonsa yayi kafin yace.
“Malam duk gyaran makarantar nan da akayi a asusun makaranta akayi school fees ɗin yaran yayi dan angyara makaranta baya nufin sai anƙarawa ɗalibai school fees zaka kashe makarantar ida kuɗin yayi yawa”.
Baki Malam Arɗo ya cuna har Moddibo ya ida magana sai kuma yace.
“In kashe makaranta fa kace?
Bayan na gyara makaranta sannan kuma ga lafiyayyun malamai masu ilimi yara suna samun wadataccen ilimi ko za'a samu ilimi abanza ne? zan ƙara school fees Tabbas zan ƙara”.
Murmushi Moddibo yayi yace.
“Toh shikenan kamar nawa za'a ƙara?".
Sai asannan Malam Arɗo yayi Murmushi yace.
“Za'a ƙarawa ko wani ɗalibi dubu Ashirin”.
Wara ido Moddibo yayi yace.
“Innalillahi gaskiya Malam yayi yawa inma za'a ƙara ya kama dole to bazai wuce aƙara dubu biyar biyar za'a ƙara shima saboda za’a ƙara sabbin malamai ne da kuma sabbin tsare-tsare”.
Kai Malam Arɗo ya jinjina yace.
“Toh shikenan tunda ka matsa zan barshi ahaka”.
Zama Moddibo ya gyara yace.
“Akwai kuma maganar tafiya musabaƙa na gasar hadda da za'ayi za'aje Noka”.
Kai Malam Arɗo ya gyaɗa da faɗin.
“Wannan ba matsala ashirya komai”.
Murmushin gefen baki Moddibo ya kumayi idanunsa akan Malam Arɗo yace.
“Eh badamuwa Malam wato tunda kasan wannan iyayen yarane zasu biya kuɗin motar da sungulla da komai”.
Dariya Malam Arɗo yayi yace.
“Atoh ainima dai ina ƙoƙari tunda motoci makarantar nanne ake tafiya dasu ko”.
Kai Moddibo ya jinjina yace.
“Ai Malam, Ƙarfe nawa zamu tafi can jauro yayan sannan mai zakaje yi?”.
Cikin sanyi yace.
“Wata Rugar Fulani ce amma gaskiya akwai tafiya zamu tafi da yanzu tun da kaga ƙarfe tara zuwa sha ɗaya zamu isa Insha Allah,Yawanci ina zuwa karatu can wajen wani Malam Aliyu limamin Rugar tasu sannan kuma anyi masa rasuwa shine nakeso Inje inyi masa ta'aziyya to kaga motata ta samu matsala”.
Jinjina kai Moddibo yayi da faɗin.
“Allah yajiƙan musulmi toh ba matsala muje tunda dama yanzu babu abinda nake yi, amma dai zamu dawo da wuri ko tunda kasan akwai ‘yan hadda?”.
Kai Malam Arɗo ya gyaɗa yace.
Toh ba matsala Allah dai ya kaimu lafiya”.
“Amin”. Yace
Sannan ya miƙe suka shiga mota suka fice kasancewar Ashirye suke.
Moddibo kuwa ƙira'ar Sheykh Jabeer ya kunna suna tafiya yana saurara tare da bin bakinsa tafiya mai ɗan nisa sukayi a haka.
Malam Arɗo ne ya katse shirun da faɗin.
“Gaskiya wannan tsarin ginin Makarantar yayi kyau Moddibo kayi ƙoƙari”.
Murmushi Moddibo yayi yace.
“Uhum Masha Allah”.
Haka suka cigaba da tafiya suna taɓa hira jefi-jefi wanda mafi yawan hiran Malam Arɗo keyi shi dai Moddibo daga Uhm sai um-um. Koko yace Masha Allah ko Alhamdulillah.
Suna dosan Rugar Moddibo yaga wajen kamar Rafi hayaƙi na tasowa lokaci ɗaya wani irin sanyi mai ratsa jiki ya ratsa gaba ɗaya ilahirin jikinsa Atake ya lumshe idanunsa tare da cije laɓɓansa na ƙasa.
Ahankali ya juya ya kalli malam Arɗo yace.
“Kai Malam garin nan akwai sanyi”.
Murmushi malam Arɗo yayi yace.
“Sosai ma kuwa garin akwai sanyi”.
Kai ya jinjina tare da jan numfashi kana ya fesar da huci mai ɗan karen ɗumi.
Dai-dai lokacin yayi parking a ƙofar gidan malam liman kana yana motsa laɓɓansa alamar Tasbihi yake.
“Subahanallahi”. Ya furta a hankali sabida tsarin garin yayi matuƙar ratsa shi.
Yaya Abba da shigowarsa kenan ya isa garesu tare da miƙawa Moddibo hannu sukayi musabaha kana yace.
“Sannun ku da zuwa fatan kunzo lafiya?”
Kai Moddibo ya gyaɗa da faɗin.
“Alhamdulillah".
Kallon Malam Arɗo Yaya Abba yayi yace.
“Tsoho mai ran ƙarfe”.
Murmushi Malam Arɗo yayi da faɗin.
“Ya akayi ɗan saurayi”.
Cikin alamun sanayya yayi musu jagora, har cikin ɗakin Malam Liman.
Cike da mutuntaka daddataku Malam Liman yake musu marhabin da zuwa.
“A'a Malam Arɗo kaine tafe, sannu da zuwa, on laleko mon njabɓa ma mon laleko bagare”.
Sai kuma ya juyo ya kalli
Yaya Abba kana yace.
“Jeka kawo musu abin taɓa wa”.
Kai yaya Abba ya gyaɗa sannan ya miƙe ya shiga cikin gida.
Ba jimawa ya dawo hannunsa riƙe da Akwashi guda biyu akan faranti sannan ya koma ya sake ɗauko kofi guda biyu ya buɗe akwashin daya fi girma Gashesh-shen naman ragone da aka masa gashin ruwa ruwa yayin da ɗaya akwashin ke ɗauke da madaran shanu mai ɗumi Yaya Abba yace.
“Bismilla kuci”.
Bai jira jin mai zasu ceba ya miƙe yabar wajen.
Shi kuwa Moddibo lumshe idanunsa yayi sakamakon ƙamahin naman daya ratsa hancinsa da kuma yanda gashin yayi kyau a ido da farko baiyi niyyan ciba amma ganin yanda gidan yake atsaftace da kuma masu gidan ga wani irin ƙamshi dake tashi yasa ya fara cin naman cikin nutsuwa tare da zuba madaran sosai yaci dan baƙaramin daɗi naman yayi ba, gashi dama baiyi breakfast ba.
Malam Arɗo ma sosai yaci sannan yasha madaran wanda shi kuwa kirtansa ke hamada ci sai yazo nan yake kashe tsatsan haƙoransa shiyasa ba cika fashin zuwa duk wata yana zuwa sai biyu.
Bayan sun kammala ne Malam Liman yashigo ya zauna daga gefen Malam Arɗo ya bashi hannu sukayi musabaha.
Malam Arɗo yace.
“Fatan mun same ku lafiya ya kuma muka ji da ƙarin haƙuri?”.
Kai Malam Liman gyaɗa tare da faɗin.
“Hakuri mungode Allah”.
Malam Arɗo yace.
“Allah ya jiƙansa da rahma da kuma dukkan musulman da suka rigamu gidan gaskiya”.
“Ameen ya hayyu ya ƙayyum”.
ya amsa.
Shima Moddibo cike da girmamawa yace.
“Malam ya mukaji da haƙuri Ubangiji Allah ya jikansa da Rahman Allah ya haskaka makwancinsa”.
Malam Liman ya amsa da.
“Ameen”.
Baffa Liman ya kalli Malam Arɗo yace.
“Muje ka gaida Babbar Addarmu wacce take madadin mahaifiyarmu”.
Kai Malam Arɗo ya gyaɗa kana yace.
“Toh ba matsala muje”.
Ya ida Maganar suna miƙewa.
Baffa Liman da malam Arɗo na gaba yayin da Moddibo da yaya Abba ke bayansu Moddibo na ƙarewa yanayin garin kallon sosai garin ya burgesa ko ina ka duba tsaf-tsaf babu alamar ƙazanta ko datti.
Bakinsu ɗauke da Sallama suka shiga gidan Hajja Nana lokacin tana zaune atsakar gidan kan ta burma.
Baffa Liman ya kalli Hajja Nana yace.
“Ga Yayana kuma ɗalibina yazo zai gaisheki”.
Tace.
“Ayyah sannunku da zuwa”.
Sannan ta miƙe ta shimfiɗa musu darduma dake tsaf dashi babu alamar datti ajiki komai na gidanta tsaf babu datti duk da stufanta amma komai nata tsaf yake.
Sosai garin da mutanen garin suka burge Moddibo komai na garin akimtse.
Gaisawa sukayi da Hajja Nana sannan suka yi mata ta'aziyya madara mai ɗumi tasa aka kawo musu. Koda sukace Alhamdulillah fir tace dolefa susha ita baƙo baya zuwa wurinta ya fita baici komaiba.
Madarar kawai Moddibo yasha kasancewar ya ƙoshi agidan malam Liman Aransa kuwa sai yaba karamci da dattakon mutanen yake.
Aɓangaren Khausar kuwa tana can rafi tare da Dije da Sadik sunje ɗiban ƙwan Zabbi da kuma kayan lambu dake hannun Khausar bayan sun gama suka fito kallon Sadik da Dije Khausar tayi tace.
“Tunda wayar yaya Abba na hannu na zanje Bishiyar ƙare zancenka in Kira Mommy na”.
Kai suka gyaɗa mata da faɗin.
“Muje toh”.