Sashe 46
Sakayyah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ita kuwa Khausar mazari uwar rawa, ƙugunta da ƙirjinta take motsawa a slowly tana mai ci gaba da cewa.
“Kai zaka zauna adamana, kuma ka bani gurin kwana, wannan shine fassarar mafarkin da nake kullum cikin baccina”.
Wani irin yar-yar Moddibo yaji tsikar jikinsa na tashi domin suna jinta ras kasan cewar Glass ɗin bayan motar a suna ƙasa kaɗan.
Ita kuwa Khausar
ida baitin tayi tana mai nuna Moddibo dake kwance jikin kujeran Idanunsa alumshe da yatsan hannunta tana murmushin dake ƙarawa fuskarta kyau.
Shi kuwa Moddibo Cikin fushi ya fuzge hannunsa daga riƙon da M Jameel yayi masa tare da sanya tattauaan tafin hannunsa da niyyan buɗe motar.
Shi kuwa M Jameel cikin sauri ya riƙe tafukan hannunsa da ƙarfi tare da girgiza masa kai alamar ya bari suga iya gudun ruwanta.
Ƙwafa Moddibo yayi tare da jingina bayansa da jikin kujeran ya cigaba da kallonta.
Ita kuwa rawanta ta cigaba dayi tana Girgiza jikinta ganin abin nata ba mai ƙare wa bane yasa Moddibo buɗe motar cike da tsananin fusata.
Kamar walƙiya ko wanda ya diro daga sama haka taga Moddibo a gabanta,
Cikin tsoro, mamaki, da kiɗima kalli fuskarsa cikin zare ido ta tayi ƙasa da kanta,
domin bata tsammaci da mutum aciki ba.
Shikuwa Moddibo cikin nutsuwarsa da kuma kamala ya fito daga motar tare da tsaida idanunsa akanta yana mai ƙara tsananta suƙe fuskarta da ya ƙara razanata.
Ita kuwa cikin tsananin ruɗu da tashin hankali mara misaltuwa ta ɗaura hannunta akai.
tare da zubewa akan gwiwoyinta tana mai girgiza kanta gaba ɗaya ta gaza cewa komai.
M Jameel kuwa gefen Driver ya buɗe tare da fitowa yana dariya mai sassayan sauti,
dai-dai lokacin da Ummi da Asma'u suka fito daga cikin gidan zuwa harabar gidan.
Idanu Ummi ne suka sauƙa akan Moddibo da M Jameel kafin kuma ta maida ganinta kan Khausar dake durƙushe ta kama kai da hannunta duka biyu,
cike da mamaki asaman fuskarta Ummu tace.
“A'a ikon Allah Khausar lafiya ya dai haka!?”.
Kasa cewa komai Khausar tayi, still hannunta na kanta haka zalika ta kasa ɗago kanta banda bugawa da ƙarfi babu abinda zuciyarta keyi da ƙarfi.
Ganin Ummi da tambayar da take yiwa Khausar yasa Moddibo basarwa kamar baisan da ruwan ɗigon Khausar dake tsugunne gabansa ba,
cike da nutsuwa da kuma takun ƙasaita ya janye ƙafarsa da ya ɗaga da niyar zaiyi wasan ƙollo da Khausar ɗin yana mai maida fushinsa ya haɗiye ya juya ya nufi gaban Ummi.
Murmushi Ummi tayi Idanunta akan Moddibo tace.
“Sannun ku da zuwa Babana, dama yanzu nake shirin zuwa unguwa zanje duba jikin Maman Khausar”.
Ta ida mgnar ta maida kallonta kan Khausar da har zuwa yanzu take durƙushe sai dib dab dib dab da sautin zuciyarta ke badawa, cikin kula tace.
“A'a Khausar yaushe kika zo? ya jikin Mommyn ki?”
Ita dai Khausar bata ɗago ba bare kuma ta motsa, gani take aduk lokacin da tayi kuskuren ɗaga kanta Moddibo zai iya kifeta da azabebben marinsan nan mai sa mutum ganin taurari masu wutsiya.
Cikin kula Ummi ta juya ta kalli Moddibo dake tsaye hannunsa na acikin aljihu murmushi tayi kana tace.
“Allah yayi zaku zo ku sameni, kuzo mushiga daga ciki”.
Kai suka jinjina tare da wuceta, ita kuwa Ummi juyawa tayi zuwa gaban Khausar ɗan tsugunna tayi tare da riƙo hannun Khausar tace.
“Duk cikin gaishe da Malama ne har haka Khausar? to taso mu tafi”.
Sai asannan Khausar ta ɗago kanta tare da sakin wani nan-nauyan ajiyar zuciya, ganin Moddibo bai nan cikin mutuwar jiki tabi Ummi falon.
Suna shiga Khausar tayi saurin janye hannunta daga cikin na Ummi, kana ta kama na Asma'u suka nufi Bedroom ɗinta”.
Suna shiga Bedroom ɗin Khausar ta janye hannunta daga na Asma'u ta zauna agefen gadon Idanunta cike da ruwan hawaye ta dafe ƙirjinta tare da cewa.
“Asma'u nashiga ukuna!nikam yau naga ta kaina, Allah yana jarabtana ta hanyar haɗani da Moddibo a bauɗaɗɗen yanayi,
zuwa na kenan naji wata waƙa tamin daɗi na tsaya ina bi uwa zabiya.
Kuma kin sanima fa ni ban fiye jin waƙa ba, sannan bai dameni ba amma kawai ɗazu naji wata waƙa MP din Haiydar Wai ita Buga da Lamba kuma wallahi nasan Haiydar ne ya haxa min da bai bani aron MP ɗinsa ba ai da banjita ba bare inji yamin daɗi, kawai na kama rawa tamkar yar gala,
ashe Moddibo na kallona nikam bansan irin hukuncin da zai minba gobe amakaranta, ƙilan ma ya sake sakani kaɗe ɗan kwali nikam nashiga Ukuna! Laifi kan laifi gashi gyale na yafa ga uban turaren dana zumbuɗa ga rawa dajin waƙa Wayyo ni Batula Faɗimatuzzahara naga ta kaina!”.
Ta gumi Asma'u tayi tare da kallon, Khausar da tayi narai-narai da ido kana tace.
“Ke kam dai Khausar kamar saɓani Allah yake haɗaki dashi”.
Narai-narai tayi da ido tare da dafe kuncinta da hannun biyu kana tace.
“Mummunan saɓani ma kuwa, na sharri ma ya Allah kashiga tsakanin na gari da mugu, Allah kara bani dashi ya Allah kada ka bashi ikon zalunta na, tun da dai arashin sani nayi kuma babu wanda yafi ƙarfin kuskure ai seya min uzuri ko?”.
Janye mata tagumin Asma'u tayi tana dariya tace.
“Kece Khausar wani zubin sai ahankali, kawai daga zuwa saiki hau rawa kamar mazari da anyi magana ki wani ce Allah yashiga tsakanin na gari da mugu sannan da kike maganar uzuri a'a ba'asi za amiki ba uzuri ba kuma waye mugun waye na garin”.
Sheƙeƙe Khausar ta ɗago kai tare da tsirawa Asma'u Idanu kana tace.
“Nifa na lura dake tun ba yanzu ba, kinfi ƙaunar Moddibo dani wato har kina goyon bayan sa akan ni kin zaɓe sa kin barni? Yoh shine mugu mana ni ta gari”.
Ware idanu Asma'u tayi tare da langwaɓar da kai tana dariya tace.
“Haba ƙawar arziƙi matsayinki yafi haka, dan Allah kada ki sake faɗan hakan aise kisa ayimina dariya”.
Taɓe baki Khausar tayi tare da faɗin.
“Kinsan gwara in gane matsayina ai tun wurima,
idan kinfi ƙaunar Moddibo insan matsayina”.
Dariya mai sauti Asma'u tayi da faɗin.
“Maida wuƙar ranki shi daɗe Fattanah”.
Murmushi Khausar tayi tare da kishingiɗa akan gadon.
Acan falo kuwa bayan Moddibo da M Jameel sun sake gaisawa da Ummi ta miƙe tashiga kichen ba daɗewa ta fito hannunta riƙe da babban tray dake ɗauke da Warmers ta ajiye musu.
Murmushi Moddibo yayi yace.
“Sannu da gajiya Ummi”.
Murmushi tayi tace.
“Yawwa Babana”.
M Jameel kuwa miƙewa yayi yashiga kichen ya dauko musu Plate da cups guda biyu kana ya dawo ya zauna.
Kulan ya buɗe, da sauri ya gyara zamansa jin wani ƙamshi mai daɗin ya ratsa hancinsu.
M Jameel ya lumshe ido tare da zuba musu akan Plate.
Moddibo ya matso tare da tsirawa Pride rice ɗin da yaji vegetables da naman kaza amsar spoon ɗin da M Jameel ke miƙa masa yayi, cikin fesar da numfashi Moddibo ya ɗibi abincin ya kai bakinsa, lokaci ɗaya yaji daɗi ya mamaye masa baki, kallon Ummi yayi tare da faɗin.
“Ummi wannan girkin yayi daɗi”.
murmushi tayi tare da tsiyaya musu tea mai ɗumi.
Bayan sun gama ci.
M Jameel ya goge bakinsa da tissue kana yace.
“Ummi ɗazun ina zakije dama?”.
Tana matsar da Flaks ɗin tea tace.
“Wallahi Maman Khausar zanje dubawa, bata da lafiya shekaran jiya a asibiti suka kwana jiya ne aka sallame su da safe”.
Girgiza kai yayu kana yace.
“Ayyah Subhanallah Allah yabata lafiya Allah yasa zakkan jikine”.
Amin Ummu tace.
Yayinda shi kuwa Moddibo Aransa yace. “Uhhhm yarinyar kamar aljana ita da mahaifiyar ta babu lafiya har ankwantar da ita a asibiti jiya-jiya aka sallame su, amma yau har ta gararo yawo, har tana rawa agidan mutane kamar wacce aka yiwa bushara da Aljanna, ita kuwa wannan daɗin me takeji”. sai kuma ya taɓe baki takaicin halayyar yarinya yasa bece musu komai amaganar ba.
Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da faɗin.
“Toh Ummi mu zamu tafi”.
Ummi ta juya ta kallesa da murmushi afuskarta tace.
“Da wuri haka Babana?”.
M Jameel ne yace.
“Ai dama a gaggauce muka zo Ummi, dan kwana biyun nan naga ya maida hankalinsa akan rubutun da yake inagama ya kusan gamawa”.
Ummi kuwa kallonta ta mayar kan Moddibo kana tace.
“Masha Allah Ubangiji Allah ya taimaka, ya kuma baku sa'a ka kusa gama wa kenan?”.
Cike da nitsuwa Moddibo ya amsa da.
“Ameen”,Kana yace.
“Eh Ummi na kusa gamawa, amma waɗan da na tura ƙasar Ɓadamaya ma tukunna wanda na turawa, Sheykh Jabeer ya duba min su har yau basu dawo ba, to inaso kawai na haɗa wa'annan ma dake wancan bugun Hafs ne wannan kuma Warash ne”.
Yai da mgnar tare sauƙe numfashi kana ya cigaba da cewa.
Warash ne nake rubuta wa to inaso idan nagama rubuta wannan ɗin na tura masa, wala Allah ya tuna mishi da duba wancan ɗin.
Nasani abubuwa ne suka masa yawa da yake ya wanci yakin arewacin nan duk wanda ya rubuta Kur'ani shi ya ake turawa sai ya duba yagani toh zanyi ƙoƙari na gama rubuta wannan ɗin sai ahaɗa akai gaba ɗaya ko zan samu ya haɗa min su lokaci ɗaya idan ya duba ingancin su”.
Jinjina kai Ummu tayi cike da yabawa jajurcewarsa da kuma ƙoƙarin sa tace.
“Masha Allah Allah yatemaka Allah ya bada sa'a abu yayi kyau Allah yabar mana irinku Moddibo Allah yayi jagora”.
Moddibo kuwa cikin jin daɗin addu'ar ta yace.
“Ameen Ummi Allah ya amsa Nagode”.
Miƙewa M Jameel yayi idanunsa akan Ummin sa yace.
“Ummi zamu tafi”.
Tana ƙoƙarin kwashe Plate da sukayi amfani dashi tace.
“Toh Nagode Allah ya muku albarka”.
Suka haɗa baki wajen faɗin.
“Ameen”.
kana suka fice.
Bayan sun ɗauki hanya M Jameel ya dubi Moddibo wanda shike Driving ɗin yanzu yace.
“Ni ka sauƙe ni agida”.
Moddibo da still hankalin sa ke kan Driving yace.
“Ba zamu tafi tare ba?”.
Girgiza kai M Jameel yayi kana yace.
“A'a nasan rubuta zaka je kayi sannan Abba ya kirani akan batun yana so naje Ɓadamaye batun Company sa akwai sabbin Injina da aka kawo, za'a saka kaga na daɗe ban jeba, amma wannan karon ko naje baze wuce kwana biyu zanyi in dawo ba”.
“Kai zaka zauna adamana, kuma ka bani gurin kwana, wannan shine fassarar mafarkin da nake kullum cikin baccina”.
Wani irin yar-yar Moddibo yaji tsikar jikinsa na tashi domin suna jinta ras kasan cewar Glass ɗin bayan motar a suna ƙasa kaɗan.
Ita kuwa Khausar
ida baitin tayi tana mai nuna Moddibo dake kwance jikin kujeran Idanunsa alumshe da yatsan hannunta tana murmushin dake ƙarawa fuskarta kyau.
Shi kuwa Moddibo Cikin fushi ya fuzge hannunsa daga riƙon da M Jameel yayi masa tare da sanya tattauaan tafin hannunsa da niyyan buɗe motar.
Shi kuwa M Jameel cikin sauri ya riƙe tafukan hannunsa da ƙarfi tare da girgiza masa kai alamar ya bari suga iya gudun ruwanta.
Ƙwafa Moddibo yayi tare da jingina bayansa da jikin kujeran ya cigaba da kallonta.
Ita kuwa rawanta ta cigaba dayi tana Girgiza jikinta ganin abin nata ba mai ƙare wa bane yasa Moddibo buɗe motar cike da tsananin fusata.
Kamar walƙiya ko wanda ya diro daga sama haka taga Moddibo a gabanta,
Cikin tsoro, mamaki, da kiɗima kalli fuskarsa cikin zare ido ta tayi ƙasa da kanta,
domin bata tsammaci da mutum aciki ba.
Shikuwa Moddibo cikin nutsuwarsa da kuma kamala ya fito daga motar tare da tsaida idanunsa akanta yana mai ƙara tsananta suƙe fuskarta da ya ƙara razanata.
Ita kuwa cikin tsananin ruɗu da tashin hankali mara misaltuwa ta ɗaura hannunta akai.
tare da zubewa akan gwiwoyinta tana mai girgiza kanta gaba ɗaya ta gaza cewa komai.
M Jameel kuwa gefen Driver ya buɗe tare da fitowa yana dariya mai sassayan sauti,
dai-dai lokacin da Ummi da Asma'u suka fito daga cikin gidan zuwa harabar gidan.
Idanu Ummi ne suka sauƙa akan Moddibo da M Jameel kafin kuma ta maida ganinta kan Khausar dake durƙushe ta kama kai da hannunta duka biyu,
cike da mamaki asaman fuskarta Ummu tace.
“A'a ikon Allah Khausar lafiya ya dai haka!?”.
Kasa cewa komai Khausar tayi, still hannunta na kanta haka zalika ta kasa ɗago kanta banda bugawa da ƙarfi babu abinda zuciyarta keyi da ƙarfi.
Ganin Ummi da tambayar da take yiwa Khausar yasa Moddibo basarwa kamar baisan da ruwan ɗigon Khausar dake tsugunne gabansa ba,
cike da nutsuwa da kuma takun ƙasaita ya janye ƙafarsa da ya ɗaga da niyar zaiyi wasan ƙollo da Khausar ɗin yana mai maida fushinsa ya haɗiye ya juya ya nufi gaban Ummi.
Murmushi Ummi tayi Idanunta akan Moddibo tace.
“Sannun ku da zuwa Babana, dama yanzu nake shirin zuwa unguwa zanje duba jikin Maman Khausar”.
Ta ida mgnar ta maida kallonta kan Khausar da har zuwa yanzu take durƙushe sai dib dab dib dab da sautin zuciyarta ke badawa, cikin kula tace.
“A'a Khausar yaushe kika zo? ya jikin Mommyn ki?”
Ita dai Khausar bata ɗago ba bare kuma ta motsa, gani take aduk lokacin da tayi kuskuren ɗaga kanta Moddibo zai iya kifeta da azabebben marinsan nan mai sa mutum ganin taurari masu wutsiya.
Cikin kula Ummi ta juya ta kalli Moddibo dake tsaye hannunsa na acikin aljihu murmushi tayi kana tace.
“Allah yayi zaku zo ku sameni, kuzo mushiga daga ciki”.
Kai suka jinjina tare da wuceta, ita kuwa Ummi juyawa tayi zuwa gaban Khausar ɗan tsugunna tayi tare da riƙo hannun Khausar tace.
“Duk cikin gaishe da Malama ne har haka Khausar? to taso mu tafi”.
Sai asannan Khausar ta ɗago kanta tare da sakin wani nan-nauyan ajiyar zuciya, ganin Moddibo bai nan cikin mutuwar jiki tabi Ummi falon.
Suna shiga Khausar tayi saurin janye hannunta daga cikin na Ummi, kana ta kama na Asma'u suka nufi Bedroom ɗinta”.
Suna shiga Bedroom ɗin Khausar ta janye hannunta daga na Asma'u ta zauna agefen gadon Idanunta cike da ruwan hawaye ta dafe ƙirjinta tare da cewa.
“Asma'u nashiga ukuna!nikam yau naga ta kaina, Allah yana jarabtana ta hanyar haɗani da Moddibo a bauɗaɗɗen yanayi,
zuwa na kenan naji wata waƙa tamin daɗi na tsaya ina bi uwa zabiya.
Kuma kin sanima fa ni ban fiye jin waƙa ba, sannan bai dameni ba amma kawai ɗazu naji wata waƙa MP din Haiydar Wai ita Buga da Lamba kuma wallahi nasan Haiydar ne ya haxa min da bai bani aron MP ɗinsa ba ai da banjita ba bare inji yamin daɗi, kawai na kama rawa tamkar yar gala,
ashe Moddibo na kallona nikam bansan irin hukuncin da zai minba gobe amakaranta, ƙilan ma ya sake sakani kaɗe ɗan kwali nikam nashiga Ukuna! Laifi kan laifi gashi gyale na yafa ga uban turaren dana zumbuɗa ga rawa dajin waƙa Wayyo ni Batula Faɗimatuzzahara naga ta kaina!”.
Ta gumi Asma'u tayi tare da kallon, Khausar da tayi narai-narai da ido kana tace.
“Ke kam dai Khausar kamar saɓani Allah yake haɗaki dashi”.
Narai-narai tayi da ido tare da dafe kuncinta da hannun biyu kana tace.
“Mummunan saɓani ma kuwa, na sharri ma ya Allah kashiga tsakanin na gari da mugu, Allah kara bani dashi ya Allah kada ka bashi ikon zalunta na, tun da dai arashin sani nayi kuma babu wanda yafi ƙarfin kuskure ai seya min uzuri ko?”.
Janye mata tagumin Asma'u tayi tana dariya tace.
“Kece Khausar wani zubin sai ahankali, kawai daga zuwa saiki hau rawa kamar mazari da anyi magana ki wani ce Allah yashiga tsakanin na gari da mugu sannan da kike maganar uzuri a'a ba'asi za amiki ba uzuri ba kuma waye mugun waye na garin”.
Sheƙeƙe Khausar ta ɗago kai tare da tsirawa Asma'u Idanu kana tace.
“Nifa na lura dake tun ba yanzu ba, kinfi ƙaunar Moddibo dani wato har kina goyon bayan sa akan ni kin zaɓe sa kin barni? Yoh shine mugu mana ni ta gari”.
Ware idanu Asma'u tayi tare da langwaɓar da kai tana dariya tace.
“Haba ƙawar arziƙi matsayinki yafi haka, dan Allah kada ki sake faɗan hakan aise kisa ayimina dariya”.
Taɓe baki Khausar tayi tare da faɗin.
“Kinsan gwara in gane matsayina ai tun wurima,
idan kinfi ƙaunar Moddibo insan matsayina”.
Dariya mai sauti Asma'u tayi da faɗin.
“Maida wuƙar ranki shi daɗe Fattanah”.
Murmushi Khausar tayi tare da kishingiɗa akan gadon.
Acan falo kuwa bayan Moddibo da M Jameel sun sake gaisawa da Ummi ta miƙe tashiga kichen ba daɗewa ta fito hannunta riƙe da babban tray dake ɗauke da Warmers ta ajiye musu.
Murmushi Moddibo yayi yace.
“Sannu da gajiya Ummi”.
Murmushi tayi tace.
“Yawwa Babana”.
M Jameel kuwa miƙewa yayi yashiga kichen ya dauko musu Plate da cups guda biyu kana ya dawo ya zauna.
Kulan ya buɗe, da sauri ya gyara zamansa jin wani ƙamshi mai daɗin ya ratsa hancinsu.
M Jameel ya lumshe ido tare da zuba musu akan Plate.
Moddibo ya matso tare da tsirawa Pride rice ɗin da yaji vegetables da naman kaza amsar spoon ɗin da M Jameel ke miƙa masa yayi, cikin fesar da numfashi Moddibo ya ɗibi abincin ya kai bakinsa, lokaci ɗaya yaji daɗi ya mamaye masa baki, kallon Ummi yayi tare da faɗin.
“Ummi wannan girkin yayi daɗi”.
murmushi tayi tare da tsiyaya musu tea mai ɗumi.
Bayan sun gama ci.
M Jameel ya goge bakinsa da tissue kana yace.
“Ummi ɗazun ina zakije dama?”.
Tana matsar da Flaks ɗin tea tace.
“Wallahi Maman Khausar zanje dubawa, bata da lafiya shekaran jiya a asibiti suka kwana jiya ne aka sallame su da safe”.
Girgiza kai yayu kana yace.
“Ayyah Subhanallah Allah yabata lafiya Allah yasa zakkan jikine”.
Amin Ummu tace.
Yayinda shi kuwa Moddibo Aransa yace. “Uhhhm yarinyar kamar aljana ita da mahaifiyar ta babu lafiya har ankwantar da ita a asibiti jiya-jiya aka sallame su, amma yau har ta gararo yawo, har tana rawa agidan mutane kamar wacce aka yiwa bushara da Aljanna, ita kuwa wannan daɗin me takeji”. sai kuma ya taɓe baki takaicin halayyar yarinya yasa bece musu komai amaganar ba.
Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da faɗin.
“Toh Ummi mu zamu tafi”.
Ummi ta juya ta kallesa da murmushi afuskarta tace.
“Da wuri haka Babana?”.
M Jameel ne yace.
“Ai dama a gaggauce muka zo Ummi, dan kwana biyun nan naga ya maida hankalinsa akan rubutun da yake inagama ya kusan gamawa”.
Ummi kuwa kallonta ta mayar kan Moddibo kana tace.
“Masha Allah Ubangiji Allah ya taimaka, ya kuma baku sa'a ka kusa gama wa kenan?”.
Cike da nitsuwa Moddibo ya amsa da.
“Ameen”,Kana yace.
“Eh Ummi na kusa gamawa, amma waɗan da na tura ƙasar Ɓadamaya ma tukunna wanda na turawa, Sheykh Jabeer ya duba min su har yau basu dawo ba, to inaso kawai na haɗa wa'annan ma dake wancan bugun Hafs ne wannan kuma Warash ne”.
Yai da mgnar tare sauƙe numfashi kana ya cigaba da cewa.
Warash ne nake rubuta wa to inaso idan nagama rubuta wannan ɗin na tura masa, wala Allah ya tuna mishi da duba wancan ɗin.
Nasani abubuwa ne suka masa yawa da yake ya wanci yakin arewacin nan duk wanda ya rubuta Kur'ani shi ya ake turawa sai ya duba yagani toh zanyi ƙoƙari na gama rubuta wannan ɗin sai ahaɗa akai gaba ɗaya ko zan samu ya haɗa min su lokaci ɗaya idan ya duba ingancin su”.
Jinjina kai Ummu tayi cike da yabawa jajurcewarsa da kuma ƙoƙarin sa tace.
“Masha Allah Allah yatemaka Allah ya bada sa'a abu yayi kyau Allah yabar mana irinku Moddibo Allah yayi jagora”.
Moddibo kuwa cikin jin daɗin addu'ar ta yace.
“Ameen Ummi Allah ya amsa Nagode”.
Miƙewa M Jameel yayi idanunsa akan Ummin sa yace.
“Ummi zamu tafi”.
Tana ƙoƙarin kwashe Plate da sukayi amfani dashi tace.
“Toh Nagode Allah ya muku albarka”.
Suka haɗa baki wajen faɗin.
“Ameen”.
kana suka fice.
Bayan sun ɗauki hanya M Jameel ya dubi Moddibo wanda shike Driving ɗin yanzu yace.
“Ni ka sauƙe ni agida”.
Moddibo da still hankalin sa ke kan Driving yace.
“Ba zamu tafi tare ba?”.
Girgiza kai M Jameel yayi kana yace.
“A'a nasan rubuta zaka je kayi sannan Abba ya kirani akan batun yana so naje Ɓadamaye batun Company sa akwai sabbin Injina da aka kawo, za'a saka kaga na daɗe ban jeba, amma wannan karon ko naje baze wuce kwana biyu zanyi in dawo ba”.