Sashe 11
Sakayyah Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Cikin nutsuwarsa da kuma sanyinsa kamar koda yaushe yake tuƙa motar, yayin da M Jameel ke gefen hagunsa kamar wanda akace ya dubi madubin dake gefensa se kuma yayi saurin kallon Moddibo dake Driving cike da mamaki yace.
“Kai A.J kaga kamar binmu akeyi fa ko?”.
Kai Moddibo ya jinjina tare da ɗan yamutsa fuska anitse yace.
“Eh binmu akeyi sai munje gidan Ummi zan tsaya”.
Cikin sauri M Jameel ya juyo gareshi tare da ɗan ware idonsa yace.
“Kama san ana binmu kuma shine ka ƙi tsayawa? Idan kuma wanda zasu cutar da mune fa A.J?”.
Kai Moddibo ya girgiza yana mai cigaba da tuƙinsa tare da buɗe lips inshi a sanyaye yace.
“Ai nasan wanda ke binmu fa Alhaji Bashir ne”.
Da sauri M Jameel yace. “Waye Alh Bashir?”.
Ɗan juyow Moddibo yayi tare da ɗan kallonshi kafin yace.
“Babban yaron Malam Arɗo ne”.
Cikin sauƙe Numfashi M Jameel yace.
“Ok to Meyesa ba zaka tsaya ba?”.
Ba tare da ya juyo ba yace.
“Nasan magana ce mai yawa yazo dashi, koda na tsaya ma, ba zamu gama ba kuma kaga agefen titi muke baya ga hakama na masa signal ya fahimta”.
Kai M Jameel ya gyaɗa tare da faɗin.
“Ok shikenan”.
Daga nan sukaci gaba da tafi.
Suna isa ƙofar gidan Ummi M Jameel ya buɗe ƙofa ya fita dai-dai lokacin da Alh Bashir ya ƙara so fuskarsa ɗauke da murmushi ya miƙa wa Alh Bashir hannu sukayi musabaha cikin sakin fuska Alh Bashir yace.
“M Jameel Ko?”.
Kai M Jameel ya gyaɗa mishi tare da cewa.
“Ya gida ya iyalai ya kuma Baba Arɗo?”.
Cikkn sakin fuska Alhj Bashi yace.
“Duk Suna lafiya”.
Murfin motar M Jameel ya buɗewa Alh Bashir tare da cewa.
“Bismillah kashiga”,
Sannan ya zagaya gefen da moddibo yake wanda har zuwa lokacin bai fito ba yace.
"Bari nashiga ciki sai ka shigo”.
Kai Moddibo ya gyaɗa cikin yanayin sanyin magarsa yace.
“Nima Ina Shigowa yanzu”.
“To sai ka shigo”.
Ya fadi tare da juyawa ya nufi cikin gida yashiga bakinsa ɗauke da sallama.
Ba lefi madedecin gida ne mai kyau daga farkon gidan ze iya ɗaukan motoci biyu se tank na ruwa dake can gefe tsakar gidan shimfiɗe yake da interlock sai babban sashe guda ɗaya cikin gidan zagaye yake da fulawa wi masu kyau wanda keda alaƙa da Moddibo dan duk inda yake da dama sai ya ƙawatasa da fulawowi, sabida suna samishi farin ciki.
Tsarin ginin yayi matuƙar kyau duk da cewa ba babba bane amma komai fess dashi haka zalika madedecin falon nasu da befiye girma ba yayi matuƙar kyau falon na ɗauke da manyan setin kujeru kalar ash da baƙi cai Centre table dake tsakiya da kuma ƙaton TV dake maƙale abango daga gabar da TV akwai ƙaton fanka bayan AC dake maƙale da bango daga yamma da TV zagaye yake da wasu flowes masu kyau da ɗaukar hankali sai tattausan carpet mai ɗan kare kyau dake malale a tsakiyar falon...
Cike da so kulawa ƙauna irin ta uwa Ummi ta kalli Jameel dake shigowa tare da sakar masa da murmushin da bata san ya subce mata ba,
bayan ta amsa sallama.
Cike da farin ciki Asma'u ta miƙe tare da gyara wuyan abaya ɗan baby himar dake zage da fuskarta da ɗauke da murmushi cike da jin daɗi ta rungume M Jameel da faɗin.
“Oyoyo Yaya Jameel na Ina yini”.
Kanta ya shafa cike da son yar uwar tasa yace.
“Lafiya lau my blood ya karatu?”.
Cikin murmushin ta amsa da.
“Alhamdulillah”.
kana ta zauna daga ƙasa kusa da ƙafafunsa,
Ummu kuwa miƙewa tayi tana ɗan leƙan bayansa.
Murmushi M Jameel yayi domin ya fahimci Moddibo take leƙawa ganin basu shigo tare ba.
Cikin yanayin fara'arsa yace.
“Kai Ummina ki bari mugaisa kafin ki tambayi 'yan biyun nawa??”.
Ka ta girgiza tare da cewa.
“A'a gwara in tambaya naji, domin shi yace na muku dambun couscous shiya keso kaga kuwa ai bazan ji daɗi ba in ban ganshi ba”.
Murmushi M Jameel yayi yana mai jin daɗin yadda mahaifiyarsa ke nunawa amininsa ƙauna tamkar ita ta haifeshi, yana murmushi jin dadi yace.
“To yana mota”.
Da sauri ta sake dubansa tare da cewa.
“To me yakeyi amota da bai shigo ba?”.
Ashagwaɓe yace.
“To Ummina mu gaisa mana”.
Dawowa tayi ta zauna bisa kujera 2 str,
shi kuwa M Jameel zamewa ƙasa yayi zauna daɓas bisa carpet kana ya ɗaura kansa acinyarta murya a sanyaye yace.
“Ummina daga shigowa ko gaisawa ba muyiba sannan baki samin albarka ba kika tsareni da tambayar Moddibo”.
Hannunta ta ɗauka bisa tsakiyar kasan tare da shafa kansa tana mai cewa.
“Ubangiji Allah ya Albarkanci rayuwarku! Allah ya dafa muku acikin dukkan lamuranku!!
Ubangiji ya tsareku daga sharrin abinƙi tsakanin mutum da aljan!!!
Allah ya baku 'ya'ya masu biyayya tamkar yadda kuke mana kaida Amininka”.
Cike da tsananin jin dadi da sassayan salama yace.
“Ameen thumma Ameen Yah Ummi”.
Hannunta ta ɗan janye daga kansa tare da sake tambayar sa.
“Ina Moddibo?”.
Ƴar dariya mai sauti yayi tare da miƙewa ya zauna akusa da ita kasancewa kujeran 2sitter ne.
gyara zamansa yayi yana fuskantar ta yace.
“Moddibo zai shigo amma ba yanzu ba”.
Da sauri tace.
“Meyasa?”.
Cikin saurin shima yace.
“Bari dai in miki bayani hankalinki ya kwanta.
Muna tahowa ne Alh Bashir babban yaron Malam Arɗo ya biyo mu to suna mota suna tattaunawa.
Nasan bazai wuce ƙorafi ya kawo akan mahaifinsu ba”.
Tsaresa da ido Ummi tayi kana tace.
“ƙorafi akan Babansu kuma?”.
Kai ya jinjina tare da cewa.
"Eh Ummi saboda Malam Arɗo wani irin mutum ne wanda zamuce mai dukiyar lukudi gashi dai Allah ya bashi dukiya na ban mamaki amma babu wanda ya isa yaci wannan kuɗin kamar abin masifa”.
Gyara zama Ummin tayi tare da cewa.
“Ikon Allah to sabi da me?”.
Numfashin M Jameel ya ɗan fesar tare da cewa.
“Tun bayan rasuwar mahaifinsa abubuwan suka ƙazanta.
Domin baya sauraron shawarar kowa koda kuwa ƙannensa ne domin shine babba acikinsu dan haka babu mai tanƙwarashi.
To fa saidai Allah ya ɗaura masa son Moddibo a zuciyarsa duk abinda Moddibo yace ko kuma ya kawo shawara akai to zaiyi koda kuwa ransa baya so.
Duk da wani lokaci zakiji yana yiwa Moddibon ma faɗa akan cewa zaisa shi kashe kuɗi amma koda ya gama surutun daga baya zakiga yayi abin da ya fadan.”
Gyara zama M Jameel yayu tare daci gaba da cewa.
“To fa wannan dalilin ne yasa muddin 'ya'yansa suna buƙatar wani abu saidai su biyo ta hannunsa Moddibo”.
Ka saƙe Ummi tayi tana kallon Jameel din kana cikin sanyin murya tace.
“To kada fa hakan yasa yayi baƙin jini awajen 'ya'yansa kasan ɗan adam”.
Dariya M Jameel yayi kana yace.
“Ummi me Moddibo zai buƙata awajen Malam Arɗo me zeyi da dukiyarsu? Mutumin da baiwa yayansa Bama me zai bawa Moddibo wanda baida shi".
Kai Ummi ta gyaɗa tare fesar da numfashi a sanyaye tace.
“Hakane kam al'amarin Moddibo da Innayi akwai al'ajabi, domin ko nasan baza su taɓa buƙatar wani abu awajensa ba, duk da kuwa anayi musu kallon basu da wani cikekken jigo acikin rayuwarsu.
Amma kuma yanda suke tafiyar da rayuwarsu cikin tsari da hikima da wadata yana bani makaki”.
Kai M Jameel ya gyaɗa tare da cewa.
“Kinga Koda motar da Malam Arɗo ke hawa tsohuwa ce aƙalla zata kai shekaru ashirin da biyar ko ashirin da takwas amma har zuwa yau ya kasa can zawa, anyi-anyi dashi yaƙi duk yanda akayi dashi ya sauya wata yaƙi kuma kullum ciki bashi ciwon kai takeyi.
har kyautar Mota ɗansa Alh Bashir ya bashi amma yaƙi amsa domin atunaninsa daga baya zai fanshe kuɗin sa.
Ko gidansa da kike gani yanzu ga gini dai yayi mai kyau amma ɗakunan matansa kamar zauren haka suke babu kujeru bare wani abu shi Tv.
Yanzu haka kwanan ake gyaran makarantarsa wanda da taimakon Moddibo akeyinsa kuma adalilinsa ne yake biyan Malamai albashi mai tsoka inba haka ba baki ɗaya makarantar ta koɗe sannan babu albashin kirki saboda Moddibo yanzu aka rushe makarantar ake gyarawa yanzu hutun da aka kara ma gani yake kamar za'a yi masa asara shiryasa yace adawo ko ba'a gama gininba to bayan an dawo yanzu dole aka sake komawa hutu saboda ba'a gama gyaranba yanzu ma cewa yayi dole kada a wuce wata ɗaya da ƙyar Moddibo ya lallaɓasa aka tafi hutun kafin adawo angama gini da kuma tsare tsare sa duk ya buwaye mu da cewa Moddibo na sashi kashe kudinsa”.
Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe tare da cewa.
“Masha Allah shiko wannan wani irin mutum ne?”.
Murmushi M Jameel yayi tare da cewa.
“Ummi haka 'ya'yansa ke fama dashi, kin san ku fulani”.
Murmushi Ummi tayi tare dayi masa daƙuwa.
“Kai A.J kaga kamar binmu akeyi fa ko?”.
Kai Moddibo ya jinjina tare da ɗan yamutsa fuska anitse yace.
“Eh binmu akeyi sai munje gidan Ummi zan tsaya”.
Cikin sauri M Jameel ya juyo gareshi tare da ɗan ware idonsa yace.
“Kama san ana binmu kuma shine ka ƙi tsayawa? Idan kuma wanda zasu cutar da mune fa A.J?”.
Kai Moddibo ya girgiza yana mai cigaba da tuƙinsa tare da buɗe lips inshi a sanyaye yace.
“Ai nasan wanda ke binmu fa Alhaji Bashir ne”.
Da sauri M Jameel yace. “Waye Alh Bashir?”.
Ɗan juyow Moddibo yayi tare da ɗan kallonshi kafin yace.
“Babban yaron Malam Arɗo ne”.
Cikin sauƙe Numfashi M Jameel yace.
“Ok to Meyesa ba zaka tsaya ba?”.
Ba tare da ya juyo ba yace.
“Nasan magana ce mai yawa yazo dashi, koda na tsaya ma, ba zamu gama ba kuma kaga agefen titi muke baya ga hakama na masa signal ya fahimta”.
Kai M Jameel ya gyaɗa tare da faɗin.
“Ok shikenan”.
Daga nan sukaci gaba da tafi.
Suna isa ƙofar gidan Ummi M Jameel ya buɗe ƙofa ya fita dai-dai lokacin da Alh Bashir ya ƙara so fuskarsa ɗauke da murmushi ya miƙa wa Alh Bashir hannu sukayi musabaha cikin sakin fuska Alh Bashir yace.
“M Jameel Ko?”.
Kai M Jameel ya gyaɗa mishi tare da cewa.
“Ya gida ya iyalai ya kuma Baba Arɗo?”.
Cikkn sakin fuska Alhj Bashi yace.
“Duk Suna lafiya”.
Murfin motar M Jameel ya buɗewa Alh Bashir tare da cewa.
“Bismillah kashiga”,
Sannan ya zagaya gefen da moddibo yake wanda har zuwa lokacin bai fito ba yace.
"Bari nashiga ciki sai ka shigo”.
Kai Moddibo ya gyaɗa cikin yanayin sanyin magarsa yace.
“Nima Ina Shigowa yanzu”.
“To sai ka shigo”.
Ya fadi tare da juyawa ya nufi cikin gida yashiga bakinsa ɗauke da sallama.
Ba lefi madedecin gida ne mai kyau daga farkon gidan ze iya ɗaukan motoci biyu se tank na ruwa dake can gefe tsakar gidan shimfiɗe yake da interlock sai babban sashe guda ɗaya cikin gidan zagaye yake da fulawa wi masu kyau wanda keda alaƙa da Moddibo dan duk inda yake da dama sai ya ƙawatasa da fulawowi, sabida suna samishi farin ciki.
Tsarin ginin yayi matuƙar kyau duk da cewa ba babba bane amma komai fess dashi haka zalika madedecin falon nasu da befiye girma ba yayi matuƙar kyau falon na ɗauke da manyan setin kujeru kalar ash da baƙi cai Centre table dake tsakiya da kuma ƙaton TV dake maƙale abango daga gabar da TV akwai ƙaton fanka bayan AC dake maƙale da bango daga yamma da TV zagaye yake da wasu flowes masu kyau da ɗaukar hankali sai tattausan carpet mai ɗan kare kyau dake malale a tsakiyar falon...
Cike da so kulawa ƙauna irin ta uwa Ummi ta kalli Jameel dake shigowa tare da sakar masa da murmushin da bata san ya subce mata ba,
bayan ta amsa sallama.
Cike da farin ciki Asma'u ta miƙe tare da gyara wuyan abaya ɗan baby himar dake zage da fuskarta da ɗauke da murmushi cike da jin daɗi ta rungume M Jameel da faɗin.
“Oyoyo Yaya Jameel na Ina yini”.
Kanta ya shafa cike da son yar uwar tasa yace.
“Lafiya lau my blood ya karatu?”.
Cikin murmushin ta amsa da.
“Alhamdulillah”.
kana ta zauna daga ƙasa kusa da ƙafafunsa,
Ummu kuwa miƙewa tayi tana ɗan leƙan bayansa.
Murmushi M Jameel yayi domin ya fahimci Moddibo take leƙawa ganin basu shigo tare ba.
Cikin yanayin fara'arsa yace.
“Kai Ummina ki bari mugaisa kafin ki tambayi 'yan biyun nawa??”.
Ka ta girgiza tare da cewa.
“A'a gwara in tambaya naji, domin shi yace na muku dambun couscous shiya keso kaga kuwa ai bazan ji daɗi ba in ban ganshi ba”.
Murmushi M Jameel yayi yana mai jin daɗin yadda mahaifiyarsa ke nunawa amininsa ƙauna tamkar ita ta haifeshi, yana murmushi jin dadi yace.
“To yana mota”.
Da sauri ta sake dubansa tare da cewa.
“To me yakeyi amota da bai shigo ba?”.
Ashagwaɓe yace.
“To Ummina mu gaisa mana”.
Dawowa tayi ta zauna bisa kujera 2 str,
shi kuwa M Jameel zamewa ƙasa yayi zauna daɓas bisa carpet kana ya ɗaura kansa acinyarta murya a sanyaye yace.
“Ummina daga shigowa ko gaisawa ba muyiba sannan baki samin albarka ba kika tsareni da tambayar Moddibo”.
Hannunta ta ɗauka bisa tsakiyar kasan tare da shafa kansa tana mai cewa.
“Ubangiji Allah ya Albarkanci rayuwarku! Allah ya dafa muku acikin dukkan lamuranku!!
Ubangiji ya tsareku daga sharrin abinƙi tsakanin mutum da aljan!!!
Allah ya baku 'ya'ya masu biyayya tamkar yadda kuke mana kaida Amininka”.
Cike da tsananin jin dadi da sassayan salama yace.
“Ameen thumma Ameen Yah Ummi”.
Hannunta ta ɗan janye daga kansa tare da sake tambayar sa.
“Ina Moddibo?”.
Ƴar dariya mai sauti yayi tare da miƙewa ya zauna akusa da ita kasancewa kujeran 2sitter ne.
gyara zamansa yayi yana fuskantar ta yace.
“Moddibo zai shigo amma ba yanzu ba”.
Da sauri tace.
“Meyasa?”.
Cikin saurin shima yace.
“Bari dai in miki bayani hankalinki ya kwanta.
Muna tahowa ne Alh Bashir babban yaron Malam Arɗo ya biyo mu to suna mota suna tattaunawa.
Nasan bazai wuce ƙorafi ya kawo akan mahaifinsu ba”.
Tsaresa da ido Ummi tayi kana tace.
“ƙorafi akan Babansu kuma?”.
Kai ya jinjina tare da cewa.
"Eh Ummi saboda Malam Arɗo wani irin mutum ne wanda zamuce mai dukiyar lukudi gashi dai Allah ya bashi dukiya na ban mamaki amma babu wanda ya isa yaci wannan kuɗin kamar abin masifa”.
Gyara zama Ummin tayi tare da cewa.
“Ikon Allah to sabi da me?”.
Numfashin M Jameel ya ɗan fesar tare da cewa.
“Tun bayan rasuwar mahaifinsa abubuwan suka ƙazanta.
Domin baya sauraron shawarar kowa koda kuwa ƙannensa ne domin shine babba acikinsu dan haka babu mai tanƙwarashi.
To fa saidai Allah ya ɗaura masa son Moddibo a zuciyarsa duk abinda Moddibo yace ko kuma ya kawo shawara akai to zaiyi koda kuwa ransa baya so.
Duk da wani lokaci zakiji yana yiwa Moddibon ma faɗa akan cewa zaisa shi kashe kuɗi amma koda ya gama surutun daga baya zakiga yayi abin da ya fadan.”
Gyara zama M Jameel yayu tare daci gaba da cewa.
“To fa wannan dalilin ne yasa muddin 'ya'yansa suna buƙatar wani abu saidai su biyo ta hannunsa Moddibo”.
Ka saƙe Ummi tayi tana kallon Jameel din kana cikin sanyin murya tace.
“To kada fa hakan yasa yayi baƙin jini awajen 'ya'yansa kasan ɗan adam”.
Dariya M Jameel yayi kana yace.
“Ummi me Moddibo zai buƙata awajen Malam Arɗo me zeyi da dukiyarsu? Mutumin da baiwa yayansa Bama me zai bawa Moddibo wanda baida shi".
Kai Ummi ta gyaɗa tare fesar da numfashi a sanyaye tace.
“Hakane kam al'amarin Moddibo da Innayi akwai al'ajabi, domin ko nasan baza su taɓa buƙatar wani abu awajensa ba, duk da kuwa anayi musu kallon basu da wani cikekken jigo acikin rayuwarsu.
Amma kuma yanda suke tafiyar da rayuwarsu cikin tsari da hikima da wadata yana bani makaki”.
Kai M Jameel ya gyaɗa tare da cewa.
“Kinga Koda motar da Malam Arɗo ke hawa tsohuwa ce aƙalla zata kai shekaru ashirin da biyar ko ashirin da takwas amma har zuwa yau ya kasa can zawa, anyi-anyi dashi yaƙi duk yanda akayi dashi ya sauya wata yaƙi kuma kullum ciki bashi ciwon kai takeyi.
har kyautar Mota ɗansa Alh Bashir ya bashi amma yaƙi amsa domin atunaninsa daga baya zai fanshe kuɗin sa.
Ko gidansa da kike gani yanzu ga gini dai yayi mai kyau amma ɗakunan matansa kamar zauren haka suke babu kujeru bare wani abu shi Tv.
Yanzu haka kwanan ake gyaran makarantarsa wanda da taimakon Moddibo akeyinsa kuma adalilinsa ne yake biyan Malamai albashi mai tsoka inba haka ba baki ɗaya makarantar ta koɗe sannan babu albashin kirki saboda Moddibo yanzu aka rushe makarantar ake gyarawa yanzu hutun da aka kara ma gani yake kamar za'a yi masa asara shiryasa yace adawo ko ba'a gama gininba to bayan an dawo yanzu dole aka sake komawa hutu saboda ba'a gama gyaranba yanzu ma cewa yayi dole kada a wuce wata ɗaya da ƙyar Moddibo ya lallaɓasa aka tafi hutun kafin adawo angama gini da kuma tsare tsare sa duk ya buwaye mu da cewa Moddibo na sashi kashe kudinsa”.
Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe tare da cewa.
“Masha Allah shiko wannan wani irin mutum ne?”.
Murmushi M Jameel yayi tare da cewa.
“Ummi haka 'ya'yansa ke fama dashi, kin san ku fulani”.
Murmushi Ummi tayi tare dayi masa daƙuwa.