Sashe 85
Sakayyah Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Kai ta gyaɗa tare da Matsawa kusa dashi still Moddibo na riƙe dashi bakin gadon ta ƙara sa Moddibo kuwa saurin lumshe idanunsa yayi.
Ita ko Khausar cikin kuka ta kalli Ramadan tare da cewa.
“Kayi haƙuri Ramadan da mun sani da baka je makarantar nan ba tun jiya kake cewa baza kaje ba kana ta roƙon Mommy kada kaje”.
Kallonta ta mayar kan Mommy tare da faɗin.
“Dan Allah Mommy duk sanda yaron nan ya sake cewa ba zaije makaranta ba kada abarshi yaje tun jiya yake ta roƙo yau ɗaya abarshi ya huta kamar yasan abinda zai faru dashi”.
Kasa cewa komai Mommy tayi ɗan ita kaɗai tasan yanda zuciyar ta ke mata.
Khausar kuwa ahankali ta tsugunna akan Ramadan ganin yanda goshinsa ke tsats-tsafo da zufa ta ɗago lallausan tafin hannunta tare da mannawa agoshin sa ta yarfe masa zufan.
Ahankali Moddibo ya tsirawa tafin hannunta Idanu cikin wani irin yanayi sannu Ahankali tsikar jikinsa ya fara tashi lumshe idanunsa yayi kana ya tuna lokacin da Amafarki ta sanya Lallausan tafin hannunta tana shafa Sajensa, ɗan juya hannunta ya buɗe Idanunsa da suka sauya launi tare da kallon hannunta yanda take shafa goshin Ramadan ɗin cikin nutsuwa yasa yaji wani abu mai masifar ƙarfi ya tsirga masa tun daga kan yatsan ƙafansa har zuwa ƙwaƙwalwar kansa lokaci ɗaya... ɗin sa ya harba da ƙarfin gaske cikin sauri ya cije lips ɗin sa tare da lumshe idanunsa yana kiran Sunan Allah Aransa.
M Jameel ya juya ya Kalli Moddibo da Idanunsa ke lumshe kana yace.
“Mu tafi ko?”.
Kai ya gyaɗa tare da yunƙurawa ya ɗauki Ramadan dake ta faman kuka Khausar ta kauce gefe tana sakin ajiyar zuciya.
Anutse Moddibo ya juya ya fita kana suma suka fice daga ɗakin zuwa harabar asibitin yana isa jikin motar ya samu har Lamiɗo yashiga gaba kana Mommy tashiga baya cikin sauri Hajiya Bunayya tace.
“Kawo shi nan in riƙe shi”.
Banza Moddibo yayi tamkar baiji me tace ba haka nan zuciyarsa ke raya masa Mommy ce mahaifiyarsu saboda kammani kana ga yanda Khausar ke kiran sunan Mommy akai-akai haka ma Ramadan yasa ya fahimci itace Mahaifiyarsu.
Buɗe bayan motar yayi tare da kallon Mommy da hankalinta ke tashe ahankali ya ɗago Ramadan tare da ɗaura mata shi akan cinyarta.
Cikin sanyayyar muryarsa mai cike da kamala nutsuwa da ladabi da kuma ƙwarjini yace.
“Mommy dan Allah kada ki tada hankalin ki. Insha Allah zai samu lafiya ki cigaba dayi masa addu'a”.
Jinjina kai tayi tare da cewa.
“Nagode Allah ya saka maka da alkhairi Ubangiji ya Albarkanci rayuwar ka nagode”.
Kansa a ƙasa ya amsa da.
“Ameen Allah ya sawwaƙa”.
Sannan ya rufe musu mota.
Driver yaja suka tafi kana Moddibo da M Jameel suka shiga motarsu suka tafi.
Sannan Malam Arɗo da Malam Isa suka shiga mota suka tafi.
Ahankali Moddibo ke Driving yayin daya tsirawa titin Idanu,M Jameel dake gefe ya sauƙe ajiyar zuciya tare da cewa.
“Kai Allah ya gyara wannan al'amarin Ubangiji Allah ya ƙara tsarewa ya kare gaba!”.
Anutse M Jameel ya juya ya kalli Moddibo jin bai amsa addu'ar tasa ba cike da kulawa yace.
“Ya dai? A.J meyafaru ne kayi shiru? Ina ta magana ba reply?”.
Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da furzar da iska mai zafi da kallon M Jameel kamar wanda aka fisgo maganar daga bakinsa yace.
“Wannan Accident ɗin shiryeyyene!”.
Zare ido M Jameel Yayi tare da cewa.
“Kamar ya shiryeyyene?”.
Ƙaramin tsaki Moddibo yaja kana yace.
“Akwai abinda ban gamsu dashi ba amma babu komai insha Allah zamuyi bin cike saboda na ɗauki number Motar Allah dai yabawa yaron nan Lafiya”.
Sauƙe numfashi yayi tare da fesar da iska daga bakinsa kana yace.
“Kaga yanda mahaifiyarsa tashiga tashin hankali amma matar nan da suka zo da ita hmmmm”.
Sai kuma yayi shiru tare da faɗin.
_“Astagfirullah Wa'atubu Ilaik ³_”.
A hankali ya numfasa tare da cewa.
_“Azzanna zambu walau kana haƙƙun,_
Allah kagafar ta min Allah kaya femin munana zato dana yi mata”.
Kallon M Jameel Yayi kana yace.
“J bangamsu da yanayinta ba”.
Jinjina kai M Jameel yayi tare da cewa.
“Sosai ma nima na lura da wani yanayi atare da ita amma dai Astagfirullah Allah mun tuba”.
Har suka shiga makarantar ba wanda ya sake magana Moddibo na Parking ya fita.
Acan gidan Lamiɗo kuwa bayan sun isa Lamiɗo ya riko Ramadan aka kafadarsa Already mai ɗaurin yazo kai tsaye sashen sa ya nufa dashi cikin sauri Mommy ta tsaya daga gefensa cikin raunin murya tace.
“Mai Martaba akaishi wurina kawai aje amasa acan”.
Kallon ta Lamiɗo yayi kana yace.
“Aysha aje amasa awaje na kawai ni yakamata inyi jinyarsa tunda yaro na miji ne”.
Girgiza kai tayi kana cikin sanyin murya tace.
“Zaka bar uzurorin kane ai ƙaramine zan iya yi masa komai yanzu da Haiydar ne zaka iya cewa zai fi ƙarfin indinga ɗaga sa ko kuma yi masa wani abu”.
ta faɗa Idanunta na zubar da hawaye
Jinjina kai Lamiɗo yayi tare da cewa.
“In dai har kina so in Samu ƙarfin gwiwa kidena zubar da hawaye kin san Banason ganin hawayen ki”.
Khausar kuwa tuni ta bar wajen.
Bayan sun shiga falon Mommy Malam Bala ya ɗaura ƙafar cikin tsanananin azaba Ramadan ke kuka saboda zafi da raɗaɗi daya ke ji miƙewa Mommy tayi tashiga Bedroom ɗin tana hawaye cike da tausayinsa Khausar ma miƙewa tayi ta shige Bedroom ɗin ta yana sheshsheƙa ba zata iya juran Kallonsa cikin ciwo ba Lamiɗo kuwa riƙe sa yana rarrashin sa bayan angama ɗaurin Malam Bala ya basu magunguna da za'a shafa ledan da M Jameel ya bashi ya ɗauko tare da ɓalla masa maganin ya bashi sannun ahankali Ramadan ya fara sakin Ajiyar zuciya nan da nan bacci ya ɗauke sa miƙewa Lamiɗo yayi ya kwantar dashi akan 3sitter kana ya nufi Bedroom ɗin Mommy.
Hajiya Bunayya kuwa ganin ba kowa afalo yasa ta sanya hannunta abakin zaninta tare da ciro wayarta kana tayi dearling wani Number tana Jin anyi picking tayi ƙasa da murya tare da cewa.
“Ya haka? Shima wanda kuka buge ɗin karaya ne fa kaɗai!?”.
A kuma dai-dai lokacin Khausar ta fito daga Bedroom ɗin ta jin falon yayi shiru ta ɗago manyan Idanunta da sukayi ja ta kelleta.
Cikin basarwa Hajiya Bunayya tace.
“Wallahi Allah ya taƙaita karaya ce kaɗai toh Nagode”.
sannan ta katse wayar.
Jinjina kai Khausar tayi tare da Kallon ta babu walwala atare da ita tace.
“Hmmm Mai rabon ganin baɗi dai zai gani koda ana kamawa ana sawa aturmi ana kirɓawa, kana zakaran da Allah ya nufa da cara ko ana ga muzuru ga shaho sai yayi”.
Hararan ta Hajiya Bunayya tayi tare da cewa.
“Ni tsiyata dake kin cika habaici da zaurance gaki Bafulatana amma kamar ba haushiya”.
A kuma dai-dai lokacin Mommy da Lamiɗo suka fito daga Bedroom ɗin suna murmushi Mommy na Kallon Hajiya Bunayya tace.
“Yaya keda Khausar dai”.
Murmushin yaƙe Hajiya Bunayya tayi tare da cewa.
“Ai lallai dai kam”.
Kallon Lamiɗo Mommy tayi kana tace.
“Yayi bacci”.
Jinjina kai yayi tare da cewa.
“Eh kafin ya tashi ya kamata adafa masa kaji ahaɗa da maganin da Bala ya bada yana tashi sai abashi yaci”.
Kai Mommy ta gyaɗa tare da karɓa, Khausar ta kalli Mommy tare da faɗin.
“Mommy kawo inje in dafa masa ainaga kamar akwai sauran kaji a fridge kana ta wuce kichen ɗin”,
Jinjina kai Mommy tayi tare da miƙa mata.
Acan Makaranta kuwa Haiydar na ganin Moddibo da M Jameel sun shigo ya miƙe da sauri tare da riƙe hannun Raudat da har zuwa lokacin take kuka kana ya nufi wajensu.
Cikin sanyun muryan yace.
“Malam ya jikin Ramadan?”.
Cike da kulawa Moddibo ya kallesa cike da tausayi ya riƙe hannun Haiydar acikin nasa tare da cewa.
“Bakomai fa ya samu lafiya karaya ne kaɗai Abbanku yaje ya ɗauke sa ankoma dashi gida za ayi masa ɗaurin gida ka kwantar da hankalin ka Haiydar ba komai insha Allah”.
M Jameel kuwa Raudat ya ɗauka tare da kallon Moddibo kana yace.
“Ita wannan kam Malaman su sunce ba tayi karatu ba sai kuka”.
Ahankali Moddibo ya juya ya kalleta baki ɗaya fuskarta yayi ja Idanunta sun kumbura kana jikinta ya ɗauki zafi cikin sanyin murya yace.
“Kiyi haƙuri Hassan ɗinki yana lafiya babu abinda ya sameshi zaki koma ki same shi agida cikin ƙoshin lafiya Insha Allah”.
Kallonsa tayi tare da cewa.
“Da gaske!?”.
Kai ya gyaɗa mata.
“Toh zamu koma gida yanzu”.
Ta faɗa tare da fashewa da kuma hadda sheshsheƙa.
Ajiyar zuciya M Jameel ya sauƙe tare da kallon Moddibo kana yace.
“Ina ganin ya kamata abarsu su koma gida dan yau ɗin nan ko sun zauna bawani karatu zasuyi ba ga Haiydar dake Babba ma baki ɗaya agigice yake bare ita yarinyar sai kuka take duk jikinta yayi zafi”.
Jinjina kai Moddibo yayi idanunsa akan Raudat yace.
“Eh hakan yayi sai su koma gida kawai”.
M Jameel na Kallon Haiydar yace.
“Bari akira gida sai aturo Driver yazo ya ɗauke ku”.
Kai Haiydar ya gyaɗa kana ya nufi Office ɗin Malam Arɗo ya sanar masa nan Malam Arɗo ya kira Lamiɗo babu daɗewa Driver yazo ya ɗauke su.
Ita ko Khausar cikin kuka ta kalli Ramadan tare da cewa.
“Kayi haƙuri Ramadan da mun sani da baka je makarantar nan ba tun jiya kake cewa baza kaje ba kana ta roƙon Mommy kada kaje”.
Kallonta ta mayar kan Mommy tare da faɗin.
“Dan Allah Mommy duk sanda yaron nan ya sake cewa ba zaije makaranta ba kada abarshi yaje tun jiya yake ta roƙo yau ɗaya abarshi ya huta kamar yasan abinda zai faru dashi”.
Kasa cewa komai Mommy tayi ɗan ita kaɗai tasan yanda zuciyar ta ke mata.
Khausar kuwa ahankali ta tsugunna akan Ramadan ganin yanda goshinsa ke tsats-tsafo da zufa ta ɗago lallausan tafin hannunta tare da mannawa agoshin sa ta yarfe masa zufan.
Ahankali Moddibo ya tsirawa tafin hannunta Idanu cikin wani irin yanayi sannu Ahankali tsikar jikinsa ya fara tashi lumshe idanunsa yayi kana ya tuna lokacin da Amafarki ta sanya Lallausan tafin hannunta tana shafa Sajensa, ɗan juya hannunta ya buɗe Idanunsa da suka sauya launi tare da kallon hannunta yanda take shafa goshin Ramadan ɗin cikin nutsuwa yasa yaji wani abu mai masifar ƙarfi ya tsirga masa tun daga kan yatsan ƙafansa har zuwa ƙwaƙwalwar kansa lokaci ɗaya... ɗin sa ya harba da ƙarfin gaske cikin sauri ya cije lips ɗin sa tare da lumshe idanunsa yana kiran Sunan Allah Aransa.
M Jameel ya juya ya Kalli Moddibo da Idanunsa ke lumshe kana yace.
“Mu tafi ko?”.
Kai ya gyaɗa tare da yunƙurawa ya ɗauki Ramadan dake ta faman kuka Khausar ta kauce gefe tana sakin ajiyar zuciya.
Anutse Moddibo ya juya ya fita kana suma suka fice daga ɗakin zuwa harabar asibitin yana isa jikin motar ya samu har Lamiɗo yashiga gaba kana Mommy tashiga baya cikin sauri Hajiya Bunayya tace.
“Kawo shi nan in riƙe shi”.
Banza Moddibo yayi tamkar baiji me tace ba haka nan zuciyarsa ke raya masa Mommy ce mahaifiyarsu saboda kammani kana ga yanda Khausar ke kiran sunan Mommy akai-akai haka ma Ramadan yasa ya fahimci itace Mahaifiyarsu.
Buɗe bayan motar yayi tare da kallon Mommy da hankalinta ke tashe ahankali ya ɗago Ramadan tare da ɗaura mata shi akan cinyarta.
Cikin sanyayyar muryarsa mai cike da kamala nutsuwa da ladabi da kuma ƙwarjini yace.
“Mommy dan Allah kada ki tada hankalin ki. Insha Allah zai samu lafiya ki cigaba dayi masa addu'a”.
Jinjina kai tayi tare da cewa.
“Nagode Allah ya saka maka da alkhairi Ubangiji ya Albarkanci rayuwar ka nagode”.
Kansa a ƙasa ya amsa da.
“Ameen Allah ya sawwaƙa”.
Sannan ya rufe musu mota.
Driver yaja suka tafi kana Moddibo da M Jameel suka shiga motarsu suka tafi.
Sannan Malam Arɗo da Malam Isa suka shiga mota suka tafi.
Ahankali Moddibo ke Driving yayin daya tsirawa titin Idanu,M Jameel dake gefe ya sauƙe ajiyar zuciya tare da cewa.
“Kai Allah ya gyara wannan al'amarin Ubangiji Allah ya ƙara tsarewa ya kare gaba!”.
Anutse M Jameel ya juya ya kalli Moddibo jin bai amsa addu'ar tasa ba cike da kulawa yace.
“Ya dai? A.J meyafaru ne kayi shiru? Ina ta magana ba reply?”.
Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da furzar da iska mai zafi da kallon M Jameel kamar wanda aka fisgo maganar daga bakinsa yace.
“Wannan Accident ɗin shiryeyyene!”.
Zare ido M Jameel Yayi tare da cewa.
“Kamar ya shiryeyyene?”.
Ƙaramin tsaki Moddibo yaja kana yace.
“Akwai abinda ban gamsu dashi ba amma babu komai insha Allah zamuyi bin cike saboda na ɗauki number Motar Allah dai yabawa yaron nan Lafiya”.
Sauƙe numfashi yayi tare da fesar da iska daga bakinsa kana yace.
“Kaga yanda mahaifiyarsa tashiga tashin hankali amma matar nan da suka zo da ita hmmmm”.
Sai kuma yayi shiru tare da faɗin.
_“Astagfirullah Wa'atubu Ilaik ³_”.
A hankali ya numfasa tare da cewa.
_“Azzanna zambu walau kana haƙƙun,_
Allah kagafar ta min Allah kaya femin munana zato dana yi mata”.
Kallon M Jameel Yayi kana yace.
“J bangamsu da yanayinta ba”.
Jinjina kai M Jameel yayi tare da cewa.
“Sosai ma nima na lura da wani yanayi atare da ita amma dai Astagfirullah Allah mun tuba”.
Har suka shiga makarantar ba wanda ya sake magana Moddibo na Parking ya fita.
Acan gidan Lamiɗo kuwa bayan sun isa Lamiɗo ya riko Ramadan aka kafadarsa Already mai ɗaurin yazo kai tsaye sashen sa ya nufa dashi cikin sauri Mommy ta tsaya daga gefensa cikin raunin murya tace.
“Mai Martaba akaishi wurina kawai aje amasa acan”.
Kallon ta Lamiɗo yayi kana yace.
“Aysha aje amasa awaje na kawai ni yakamata inyi jinyarsa tunda yaro na miji ne”.
Girgiza kai tayi kana cikin sanyin murya tace.
“Zaka bar uzurorin kane ai ƙaramine zan iya yi masa komai yanzu da Haiydar ne zaka iya cewa zai fi ƙarfin indinga ɗaga sa ko kuma yi masa wani abu”.
ta faɗa Idanunta na zubar da hawaye
Jinjina kai Lamiɗo yayi tare da cewa.
“In dai har kina so in Samu ƙarfin gwiwa kidena zubar da hawaye kin san Banason ganin hawayen ki”.
Khausar kuwa tuni ta bar wajen.
Bayan sun shiga falon Mommy Malam Bala ya ɗaura ƙafar cikin tsanananin azaba Ramadan ke kuka saboda zafi da raɗaɗi daya ke ji miƙewa Mommy tayi tashiga Bedroom ɗin tana hawaye cike da tausayinsa Khausar ma miƙewa tayi ta shige Bedroom ɗin ta yana sheshsheƙa ba zata iya juran Kallonsa cikin ciwo ba Lamiɗo kuwa riƙe sa yana rarrashin sa bayan angama ɗaurin Malam Bala ya basu magunguna da za'a shafa ledan da M Jameel ya bashi ya ɗauko tare da ɓalla masa maganin ya bashi sannun ahankali Ramadan ya fara sakin Ajiyar zuciya nan da nan bacci ya ɗauke sa miƙewa Lamiɗo yayi ya kwantar dashi akan 3sitter kana ya nufi Bedroom ɗin Mommy.
Hajiya Bunayya kuwa ganin ba kowa afalo yasa ta sanya hannunta abakin zaninta tare da ciro wayarta kana tayi dearling wani Number tana Jin anyi picking tayi ƙasa da murya tare da cewa.
“Ya haka? Shima wanda kuka buge ɗin karaya ne fa kaɗai!?”.
A kuma dai-dai lokacin Khausar ta fito daga Bedroom ɗin ta jin falon yayi shiru ta ɗago manyan Idanunta da sukayi ja ta kelleta.
Cikin basarwa Hajiya Bunayya tace.
“Wallahi Allah ya taƙaita karaya ce kaɗai toh Nagode”.
sannan ta katse wayar.
Jinjina kai Khausar tayi tare da Kallon ta babu walwala atare da ita tace.
“Hmmm Mai rabon ganin baɗi dai zai gani koda ana kamawa ana sawa aturmi ana kirɓawa, kana zakaran da Allah ya nufa da cara ko ana ga muzuru ga shaho sai yayi”.
Hararan ta Hajiya Bunayya tayi tare da cewa.
“Ni tsiyata dake kin cika habaici da zaurance gaki Bafulatana amma kamar ba haushiya”.
A kuma dai-dai lokacin Mommy da Lamiɗo suka fito daga Bedroom ɗin suna murmushi Mommy na Kallon Hajiya Bunayya tace.
“Yaya keda Khausar dai”.
Murmushin yaƙe Hajiya Bunayya tayi tare da cewa.
“Ai lallai dai kam”.
Kallon Lamiɗo Mommy tayi kana tace.
“Yayi bacci”.
Jinjina kai yayi tare da cewa.
“Eh kafin ya tashi ya kamata adafa masa kaji ahaɗa da maganin da Bala ya bada yana tashi sai abashi yaci”.
Kai Mommy ta gyaɗa tare da karɓa, Khausar ta kalli Mommy tare da faɗin.
“Mommy kawo inje in dafa masa ainaga kamar akwai sauran kaji a fridge kana ta wuce kichen ɗin”,
Jinjina kai Mommy tayi tare da miƙa mata.
Acan Makaranta kuwa Haiydar na ganin Moddibo da M Jameel sun shigo ya miƙe da sauri tare da riƙe hannun Raudat da har zuwa lokacin take kuka kana ya nufi wajensu.
Cikin sanyun muryan yace.
“Malam ya jikin Ramadan?”.
Cike da kulawa Moddibo ya kallesa cike da tausayi ya riƙe hannun Haiydar acikin nasa tare da cewa.
“Bakomai fa ya samu lafiya karaya ne kaɗai Abbanku yaje ya ɗauke sa ankoma dashi gida za ayi masa ɗaurin gida ka kwantar da hankalin ka Haiydar ba komai insha Allah”.
M Jameel kuwa Raudat ya ɗauka tare da kallon Moddibo kana yace.
“Ita wannan kam Malaman su sunce ba tayi karatu ba sai kuka”.
Ahankali Moddibo ya juya ya kalleta baki ɗaya fuskarta yayi ja Idanunta sun kumbura kana jikinta ya ɗauki zafi cikin sanyin murya yace.
“Kiyi haƙuri Hassan ɗinki yana lafiya babu abinda ya sameshi zaki koma ki same shi agida cikin ƙoshin lafiya Insha Allah”.
Kallonsa tayi tare da cewa.
“Da gaske!?”.
Kai ya gyaɗa mata.
“Toh zamu koma gida yanzu”.
Ta faɗa tare da fashewa da kuma hadda sheshsheƙa.
Ajiyar zuciya M Jameel ya sauƙe tare da kallon Moddibo kana yace.
“Ina ganin ya kamata abarsu su koma gida dan yau ɗin nan ko sun zauna bawani karatu zasuyi ba ga Haiydar dake Babba ma baki ɗaya agigice yake bare ita yarinyar sai kuka take duk jikinta yayi zafi”.
Jinjina kai Moddibo yayi idanunsa akan Raudat yace.
“Eh hakan yayi sai su koma gida kawai”.
M Jameel na Kallon Haiydar yace.
“Bari akira gida sai aturo Driver yazo ya ɗauke ku”.
Kai Haiydar ya gyaɗa kana ya nufi Office ɗin Malam Arɗo ya sanar masa nan Malam Arɗo ya kira Lamiɗo babu daɗewa Driver yazo ya ɗauke su.