← Book details Sakayyah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 33 OF 114

Sashe 33

Sakayyah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Shi kuwa Moddibo ɗaya daga cikin duwatsun wajen ya samu ya zauna tare da kiran wayar M Jameel.
M Jameel na ɗagawa Yayi Sallama.
Amsawa Moddibo yayi tare da faɗin.
“Kada kaje kata nemana nasan zaka ne meni bana nan sannan ka kira wayata kaji akashe ina wani ƙauye ne da mukaje da Malam Arɗo amma Insha Allah zamu dawo kafin Azahar".
M Jameel yace.
“Toh meyasa baka gaya min ba tun ɗazu”.
Cikin yanayin shaƙuwa yace.
“Nima zuwan ba zata ne, kuma lokacin nasan kana bacci”.
Cikin sauƙe numfashi M Jameel yace.
“Toh badamuwa Allah ya dawo daku lafiya”.

“Ameen”. Yace tare da katse kiran.

Bayan ankira sallan Azahar sun idar kai tsaye wajen motarsu suka nufa Yaya Abba ne ya zo ya miƙa masa kwandon kayan Marmarin da Khausar tace abashi.

Cikin yanayin nutsuwarsa da kuma sanyin murya sa yace.
“A'a Nagode amma ka ajiye awajenka”
Murmushi yaya Abba yayi yace.
“To ai bani ce na baka ba Khausar ce tace abaka”.
Yana gama faɗa ya buɗe bayan motar ya saka masa.
Malam Liman ma ya basu Zabbi Baffa Jauro kuma ya aiko musu da ƙwan Zabbi Hajja Nana kuma ta aiko musu da zuma sannan suka yi musu sallama suka tafi Moddibo kuwa yaba karamci ci halaccin mutanen sukayi.

Suna shiga cikin gari ya wuce da Malam Arɗo gidansa ya ajiye sa sannan ya sauke masa ƙwan Zabbin da kuma Zabbin da goran zuma.

Malam Arɗo yace.
“Ka ɗauki Zabbin da kuma ƙwoyin mana”.
Kai Moddibo ya girgiza yace.
“A'a wannan zumar ma ya isheni”.
Ya ida maganar tare da jan motar ya fice zuwa gidansa.

Acan ɓangaren Mommy kuwa da daren ta samu Lamiɗo ta faɗa masa maganar rasuwar da kuma son zuwanta suyi ta'aziyya, Cikin jimami yace toh Allah ya kaimu gobe zasu zo.

*WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA*

_Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba'a baiwa mai kishiya, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi mai masifar ƙarfi da matse mace, ka masin Daɗi har Maɗigan Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, Zumar goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai tsastsafo da ni'imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai maganin sanyi sadidan, da dai sauransu...Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba...._ _Shin ko kina da labarin Miskilinci da ƙasaitar Rayyan Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_
_Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da sahihan maganin da kuma shu'uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja anma jinta yake tamkar budurwa 'yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma'aurata na tabbata kunsan da cewa basirarta ba'a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma'aurata ta hanyar kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 09097853276 muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah 'yar uwa idan baki shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci...._

🤝🏻🤝🏻🤝🏻🤝🏻🥰😘sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida,

Washe gari Da safe suka ɗauki hanya zuwa Rugar Jauro Yaya sukayi ta'aziyya.
Bayan sun gama gaisawa ne Mommy tace.
“Hajja Nana zamu koma da Khausar dan gobe Insha Allah zasu koma makaranta”.

Kai Hajja Nana ta gyaɗa dan mutuwar ƙaninnata yasa tayi sanyi baki ɗaya.
Tace.
“Badamuwa ku koma da ita amma idan an kwana biyu ta riƙa zuwa saboda su saba da ‘Yan uwanta”.
Kai Mommy ta gyaɗa kana tace.
“Badamuwa Insha Allah zata zo”.

Kasancewar dama Khausar ta haɗa kayanta tun daren jiya yasa ta dauko jakarta sai kuma ta Rungume Hajja Nana tace.
“Hajja Nana zanyi kewarki ki riƙa zuwa bishiyar ƙare zancenka kina kirana dan Allah”.

Murmushi Hajja Nana tayi kana tace.
“Sai kace kin damu dani bayan rashin kunya kike min".
ƙaramin bakinta ta tura tare da ficewa tana cewa nidai zanyi kewarki.
Baki ɗaya Kakannints suka rakata jikin mota bayan sun haɗa mata tsaraba iri-iri Kama daga, Zabbi, Kaji, Ƙwan Zabbi, Nono jarka-jarka da kuma zuma man shanu.
Kawai sai Khausar ta fashe da kuka cikin raunin murya.
Tace.
“Aranan da nazo kamar haka da Baffa Umaru aka tareni yau kuma gashi babu shi!".
Hannunta Baffa Garga ya riƙe cikin rauni da zuba hawaye yace.
“Kiyi haƙuri Khausar haka rayuwar take idan kaini yau gobe ba kai bane, kuma in sha Allah zasuga SAKAYYAH”.

Hawayenta ta share tare da shiga mota tana ɗaga musu hannu Dije ma kan sosai tasha kukan rabuwa da Khausar.
Fatan sauƙa lafiya suka musu sannan suka ja motar suka tafi.

Khausar kuwa motarsu na isa harabar gidan Haiydar, Raudat da Ramadan suka taho da gudu suka rungumeta Ramadan ne yace.
“Addah Khausi nayi missing ɗinki”.
Kansa ta shafa tare da cewa.
“Nima nayi missing naku”.

“Addah Khausar Barka da dawowa daga zuwanki har gidan yayi haske, amma da bakinan duk saiyayi duhu”.
Cewar Haiydar
Ta wani wara manyan Idanunta tace.
“Kada kayi masu gidan suji”
ta faɗa tare da ɗaukar Ramadan suka shiga ciki afalon suka zube suna ta hiran bayan rabuwa.
Cikin sakin fuska Khausar ta kalli Raudat dake zuzzuɓura baki tace.
“A'a My happiness sis ya akayi ne?”.
Baki Raudat ta kuma turawa tare da cewa.
“Ba wani ai naga kinfi son Ramadan”.
Dariya mai sauti tayi tare da jawota ta ruggumeta.
Kana suka ci gaba da hirar yaushe gama. sallah kaɗai ke ɗagasu.

Bayan kwana biyu ya kama yau Asabar zasu koma makaranta kasancewar Asabar ne farkon satinsu Alhamis da juma'a kuma Weekend.
Tun wuri Khausar ta tashi bayan ta idar da sallar asbah tayi Azkharul sabah toilet ta shiga tayi wanka kana ta fito ta zauna gaban dressing mirrow ta shafe jikinta da lotion ɗinta kana ta shafa kajol a manyan Idanunta masu haske sai kuma ta shafa lips dinta Kaɗan tulin sumar kanta dake tsefe ta sanya farin Ribont ta kama ahankali ta buɗe duro ta ɗauki uniform ɗin ta dake goge maroon din wandon ta fara sanya wa sannan tasa ka farin riga sai kuma ta ɗauki farin ɗankwali ta ɗaura kana ta ɗauki maroon din hijab ta Sanya Wanda ya tsaya gwiwarta wani irin kyau tayi na ban mamaki sosai Uniform din ya amshets tamkar dan ita akayi.
A gaban Dressing mirrow ta tsaya ta ɗauki kwalban turare sun kai kala biyar ta feshe ilahirin jikinta dashi sannan ta ɗauki combos Fari ta Sanya tare da ɗaukar school bag ɗinta ta rataya kana ta fito falo.

Murmushi Mommy tayi tace.
“Manana kinyi kyau”.
Ta juya manyan Idanunta tace.
“Nogode Mommy na”.
Haiydar kam murmushi yayi yace.
“Yau za'ayi ruwa da ƙanƙara shugaban ’yan letti ta riga kowa shiryawa”.

Harara ta maka masa batare da tace komai ba ta shirya Raudat sannan sukayi Breakfast suka shiga mota Amina sai Harara take watsa mata ita kuwa khausar bata ma san tana yiba domin aƙasan ranta tunanin haɗuwarta da Moddibo take da kuma irin hukuncin da zai yanke mata.

Suna isa Makarantar lokacin har anfara shiga class cikin sauri sauri Khausar ta riƙe hannun Raudat suka nufi side dinsu Raudat ta ajiyeta a class kana da sauri ta juya, zata fita class ɗin kenan.
Taji Raudat ta saki ƙara tare da kiranta.
Da sauri ta juya tare da kamo Raudat ɗin da taga tana jujjuyawa, tsugunawa tayi tare da cewa.
“Raudat menene ya faru”.
Cikin kuka da yarfa hannu Raudat tace.
“Wayyo idona Adda Khausy ido, borkono".
Da sauri ta jawota tare da fara hura mata idon.
Sai kuma ta amshi goron ruwar da Antin su ke miƙa mata.
Wonke mata fuskar ta ta farayi tare da murza mata idon.
Cikin Sa'a kuwa ɗan abin da ta shiga idon ya fita.
A hankali ta buɗe idann nata, da tuni yayi jazir.
Cikin sanyi tace.
“Ayyah Raudy na sannu ko, yanzu dai ya fita ko?”.
Kai ta gyaɗa mata tare da kama hannun Antin nasu.
Ganin hakane yasa Khausar juyawa da sauri ta fito ta nufi harabar makarantar.

Shiru ba kowa a tsakiyar harabar alamun an gama shiga class kenan.

Cikin sassarfa ta fito daga side din ’yan nursery.
Kana ta nufi sude ɗinsu.

Da sassarfa ta nufi kan step ɗin.
Dai-dai lokacin kuma Moddibo ya fito daga class dinsu ya nufi ƙasa, a hankali yake take steps din yayinda hankalinsa baki ɗaya yana kan....!

Ki biya ki karanta, kiji ainin manufar labarin kiyi dariya kiyi shauƙi kibi haushi kiki tausayi kiyi kuka. Kiyi murmushi

By
*GARKUWAR MARUBUTA*
[19/07, 7:44 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: 📝🍇✨💫⏰🤴🏻👹❤️❤️❤️🍇

*SAKAYYAH*
_Page 9_

NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*FREE PAGE NE ƴar uwa ki biya ki karanta abinki cikin Salamah, littafin SAKAYYAH 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276. Kana in saki a Groups da na buɗe ba SAKAYYAH in da zaki karanta abinki salamun ƙaulum min rabbil rahim. Nama lfy fata lfy. Ba ruwan ki da jiran na sata na Allah ya isa*
Chapter 33 · 0% Book details