Sashe 16
Sakayyah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Murmushi ta ƙaƙalo tare da faɗin.
“A'a Momy babu damuwa munyi magana da Asma'u tace koda awaya zan iya ƙarawa da kaina batare da anwuce Ni ba”.
Dubanta Momy tayi tare da cewa.
“Kin tabbata Khausar har cikin ranki kikeson zuwa Jauro Yaya!?”.
Kai ta gyaɗa tace.
“Eh”.
Aranta kuwa cewa tayi ba gwara masifar wancan tsohuwar ba dan ko yaya bazan tsaya ta dake niba amma wannan mutumin ya riƙa tsareka da firgitattun idanunsa masu saka tsoro da fargaba, baya ga haka in banyi sa'a ba duka na zai sa ayi banyi masa lefi bama idan yasamu sarari sawa yake aci zalina bare kuma nayi masa laifi...
Muryan Momy dake cewa.
“Toh shikenan nima nafi so ki tafi Kinga idan hutun ku ya ƙare sannan anƙarasa muku gyaran makaranta seki dawo”.
Ya dawo da ita daga duniyar data lula.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Shikenan Momy”, Sannan ta miƙe ta shiga Bedroom ɗin ta.
Momy kuwa Hisnul Muslim ta ɗauka ta cigaba da Azkhar yayin da Raudat ta miƙe tabi bayan Khausar.
Ita kuwa khausar na shiga ɗaki ta hau kan stoll ta janyo trolley ɗin ta sannan tashiga haɗa kaya Raudat dake kallonta tace.
”Dani Zaki tafi Addah Khausi?”.
Girgiza mata kai Khausar tayi alamar a'a.
Kuka Raudat ta fashe dashi tana cewa.
“Ni zan biki”.
Zama Khausar tayi ta riƙe hannunta tare da langwaɓar da kai tace.
“Raudat garin bashi da daɗi fa, ga tsohuwar garin ta fiye masifa, kana yi mata kuskure kaɗan zata zane Mutum”.
Jin haka yasa Raudat ta girgiza kai tace.
“Nide ba zanje ba idan haka ne”.
Aɓangaren Momy kuwa bayan tashiga turakar Lamiɗo sunyi shirin kwanciya ta dubesa fuskarta ɗauke da murmushi me sanyi tace.
“Uhum wai ɗazu Khausar ke cemin idan Allah yakaimu gobe tana son zuwa Rugar Jauro Yaya”.
Zamanshi ya gyara tare da faɗaɗa Murmushin dake fuskarsa kana yace.
“Allah ya kaimu hakan nada kyau idan yaso tunda gobe weekend ne zamuje dukan mu kema sai ku gaisa tunda kinyi shekaru baki jeba”.
Kai ta jinjina kafin tace.
“Kai naji dadi Allah ya kaimu”.
Amin yace kana sukaci gaba da hirarsu.
Washe gari Ya kama asabar da wuri Khausar ta tashi ta gyara ɗakinta sannan ta nufi ɗakin Momy ta gyara kana ta share har zuwa falo da kuma duk sashen saida ta gyara ko wani lungu da saƙo.
Bayan ta gama ta dawo ta shiga kichen ta zuba musu Breakfast soyayyan cheaps da tea ita da Raudat ke ciki.
Bayan sun kammala ta miƙe tana ƙoƙarin tattare wajen Momy tashigo Idanunta akan Khausar.
fuska ta ɗan tsuke tare da faɗin.
“Maza kije yanzu Aunty Jamila tayi Miki kitso”.
Aunty Jamila matar ƙani Lamiɗo ne sannan Momy tasan inba tayiwa Khausar dagaske to baza taje ba domin bata ƙaunar kitso.
Ganin fuskar Momy babu walwala yasa Khausar gyaɗa kai tare da shiga Bedroom ta ɗauko dogon hijabinta fari Nevy blue daya sha ninkin guga ta ɗaura akan riga da wandon dake jikinta kana ta fice ta nufi gidan Aunty Jamila tana zumɓura baki da kuma kifiya da kum a hannunta.
Bakinta ɗauke da sallama tashiga gidan, Aunty Jamila dake zaune ta amsa Sallamar tana faɗaɗa fara'ar dake fuskarta tace.
“A'a Khausar kece?, sannu da zuwa”.
Sake fuska Khausar ta ɗanyi tace.
“Eh nice Aunty wai kitso nazo kiyi min zanje Jauro Yaya”.
Murmushi Aunty Jamila tayi tare da cewa
“Masha Allah kice zakije ziyara?”.
Kai Khausar ta gyaɗa tana murmushi.
Cikin sakin fuska Aunty Jamila tace.
“Allah Ya kaiku lafiya".
“Amin ya rabbil izzati”.
Cewar Khausar.
“Kinga kuwa kinyi sa'a duk na gama aiyuka na”.
Da sauri tace.
“Aunty Jamila manya fa zakiyi shida ko takwas”.
Murmushi Aunty Jamila tayi.
Kana ta miƙe ta shiga ɗaƙi tare da kwantar da yaronta kana ta fito,
Akan kujeran roba Khausar ta zauna ita kuma ta tsaya ta fara yi mata kitson suna cikin kitson ne suka jiyo Sallamar Gimbiya Dadu.
Anutse Aunty Jamila ta ɗago kanta fuskarta ɗauke da murmushi tace.
“Sannu da zuwa Mama”.
Asaman laɓɓa Gimbiya Dadu ta Amsawa Aunty Jamila baki ɗaya nutsuwarta da hankalinta suna kan Khausar.
Miƙewa Aunty Jamila tayi tashiga ɗaki dan ɗaukowa Gimbiya Dadu Darduman zama.
Ita kuwa khausar ahankali ta ɗago kanta caraf Idanunta suka sauƙa akan Gimbiya Dadu data tsareta da ido ita kuwa khausar cikin hanzari tayi ƙasa da idanunta tana mai karanto duk wata addu'ar da tazo bakinta kamar minti ɗaya Khausar ta sake ɗago kanta akaro na uku still Idanun Gimbiya Dadu na kanta.
Ita kuwa khausar kasa jurewa tayi ta tsayar da Idanunta akan Gimbiya Dadu cikin dakiya tace.
“Wai dan Allah Gimbiya Dadu Meyesa kike kallona haka?”.
Wani murmushi mai cike da ma'anoni Gimbiya Dadu tayi tare da cewa.
“Uhum yaro man kaza,
ai tunda kika bar cikin Awaki 'yan uwanki kika dawo cikin Kuraye ai dole akalleki! In kalleki in kuma”.
jin abinda Gimbiya Dadu tace yasa ta miƙe cikin rawan jiki da alamar tsoro aƙwayar Idanunta ta sanya hijabinta ta fita batare data jira Aunty Jamila ta fito ta ƙarasa yi mata kitson ba...
Sauri-sauri gudu-gudu take tafiya har ta isa bakin gate dinsu da sassarfa ta shigo coumpund ɗin su har yanzu jikinta be daina ɓari ba tana gyara zaman hijabin kanta Momy ta fito,Kallonta Momy tayi tare da cewa.
“Har angama kitson ne".
Ka ta gyaɗa mata ba tare da tace komai ba.
“Dama yanzu zan aika Haiydar ya kira ki kizo mu tafi”.
Murmushin karfin hali ts ƙirƙira kana tace.
“Eh mun gama”.
Wuce ta Momy tayi taje tashiga gaban mota Ita kuwa khausar kallon Raudat, Ramadan, da kuma Haiydar dake tsaye tayi tare da ɗaga musu hannu suma hannu suka ɗaga mata ahankali ta juya ta nufi wajen motar tana isa tasa hannu ta buɗe tashiga gidan baya Haiydar da Ramadan na cigaba da ɗaga mata hannun.
Babban gate mai gadin ya buɗe musu kana Lamiɗo ya cilla hancin motarsa.
Khausar kuwa jingina bayanta ajikin motar tayi tare da lumshe Idanunta zuciyarta na bugawa da mugun sauri abu biyu ne suka yiwa zuciyarta ƙawanya na farko hukuncin da Moddibo zai ɗauka akanta na biyu kalaman Gimbiya Dadu wanda suke ƙara tabbatar mata da zantuka dake yawo a gari cewa matar nan mayyace...
Anutse Momy ta dubi Moddibo dake sharara gudu akan Lafiyayyan titin nasu tace.
“Abban Haiydar gudun nan baiyi yawa ba”.
Kanshi ya ɗan jujjuya mata,
Ita kuwa cikin sanyi tace.
“Gsky dai ka rage gudun kamar yayi yawa”.
Juyowa yayi ya kalleta da murmushi a fuskarsa yace.
“Lokaci na tafiya kinga yanzu goma tayi gwara mu isa da wuri kada rana tayi mana mu samu mu juyo da wuri”.
Kai ta gyaɗa kafin tace.
“Amma duk da haka arage gudun".
Tattausan murmushin ya sakar mata tare da gyaɗa kai...
Sunyi tafiya mai tsawo kafin suka fara hango garin Atake suka fara tabbatar da sanyin da ake acikin Gembila wasa ne.
Domin tun kafin su shiga garin suka hango tamkar hayaƙi ke tashi saboda masifaffen sanyin da ake tsugawa acikin Jauro yaya suna shiga cikin garin suka fara ratsa bishiyoyi masu korayen ganye suna rangaji tare da fitar da sanyayyan Iska kasancewar hantsi ne duk makiyaya sun tafi se kuma,
'yan dalo da aka ɗaɗɗaure masu kyan launi ga kuma kukan tsuntsaye dana zabbi da ke tashi suna ajiye ƙwai.
Suna shiga tsakiyar Rugar Jauro,
kai tsaye ƙofar gidan dake kusa da babbar fadan Rugar suka nufa anan sukayi parking motar tare da fitowa.
Wasu dattawa dake zaune aƙofan masallacin dake kusa da babbar fadan suka taso baki ɗaya idanun su akan Khausar data fito daga mota tana gyara zaman hijabinta suna faɗin.
“Audiii Barka da zuwa kece?”.
ɗaya daga cikin dattijon ne ya taso wanda ya kasance shine Jauron garin ya riƙe hannun Khausar.
Fuskarsa ɗauke da murmushi yake faɗin.
”Addah, Addah, Addah, kizo ga Khausar”.
sauran ma bin bayansu sukayi zuwa cikin gidan suna masuyiwa Momy da Lamido Barka da zuwa.
Biyu daga cikine suka ce da Momy da kuma Lamiɗo.
“Sannunku da zuwa ya kuka tsaya ku shigo daga ciki”.
Kai Momy ta gyaɗa kana suka yi musu godiya bisa jagoranci suka nufi cikin gidan.
Jauro kuwa yana riƙe da hannun Khausar yana mata wasa da faɗin.
“Iyeee girman falo ji jiki kamar auduga,
bakisan riƙe sandar kiwo ba sannan baki san ta tsar nono ba girman burodi wayon shayi kawai”.
Ita kuwa khausar hannu ta wara da faɗin.
“Ban iya ba kam”.
Murmushi yayi kana yace.
“Zamu koya muki ai”.
maƙale kafaɗa tayi tace.
“Bana so ba kace min girman bread wayon tea ba”.
Murmushi yay i tare da cewa.
“To girman fura da nono”.
Akuma dai-dai lokacin suka shiga ɗakin tsohuwar wanda yake ginin gargajiya shatin kobo.
Suna shiga Jauro yace. “Addah ga 'yar Usman tazo”.
Ya mutse fuska Hajja Nana tayi tare da kallon Khausar tace.
“Shegiyar kaya me wuyar ɗauka se yau kika ga damar zuwa??”.
Murmushi Jauro yayi still hannunsa na cikin na Khausar yace.
“Tazo da mahaifiyarta da kuma Mahaifinta”.
Wani kallo Hajja Nana ta masa tare da cewa.
“Kai Jauro ka gyara kalamanka,
badai mahaifinta ba mahaifin riƙo dai ko? ka manta mahaifinta da kai aka binnesa shekaru goma sha biyar da suka wuce?”.
Kai ya jinjina alamar hakane amma bece komai ba ita kuwa miƙewa tayi ta ɗauko taburma ta shimfida tare da ɗauko darduman kilisa ta shimfiɗa.
A kuma lokacin Momy da Lamiɗo suka shigo cikin sakin fuska tashiga yi musu lale marhaba.
zama Momy da Lamiɗo sukayi akan shimfiɗar data musu kana ita kuma ta zauna awajen zamanta na farko yayin da duka ƙannenta maza suka zauna daga bayanta se ta zamto tamkar sarauniya acikinsu ko wannensu fuskarsa ɗauke da murmushi yake faɗin.
“Addah yau kam ga Khausar tazo”.
Haka yasa ta juyu.
Ta dubi Khausar da alamun farin cikin ganinta afuskarta saidai yanayin zafinta bazai sa ka fahimta ba.
Ta dubi Khausar da tayi kicin-kicin da fuska tace.
“Menene kike wani kumbura fuska? gwara ma ki saki ranki fa”.
Zumɓura baki Khausar tayi saidai ba tace komaiba.
Hajja Nana kuwa sake kallon Khausar tayi akaro na barkatai tace.
“Ki tashi ki kawo ma baƙi abin taɓawa”.
Lumshe idanu tayi kafin tace.
“Nice zan kawo abin taɓa wa?,Nima ai baƙuwa ce akawo mana dai”.
“A'a Momy babu damuwa munyi magana da Asma'u tace koda awaya zan iya ƙarawa da kaina batare da anwuce Ni ba”.
Dubanta Momy tayi tare da cewa.
“Kin tabbata Khausar har cikin ranki kikeson zuwa Jauro Yaya!?”.
Kai ta gyaɗa tace.
“Eh”.
Aranta kuwa cewa tayi ba gwara masifar wancan tsohuwar ba dan ko yaya bazan tsaya ta dake niba amma wannan mutumin ya riƙa tsareka da firgitattun idanunsa masu saka tsoro da fargaba, baya ga haka in banyi sa'a ba duka na zai sa ayi banyi masa lefi bama idan yasamu sarari sawa yake aci zalina bare kuma nayi masa laifi...
Muryan Momy dake cewa.
“Toh shikenan nima nafi so ki tafi Kinga idan hutun ku ya ƙare sannan anƙarasa muku gyaran makaranta seki dawo”.
Ya dawo da ita daga duniyar data lula.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Shikenan Momy”, Sannan ta miƙe ta shiga Bedroom ɗin ta.
Momy kuwa Hisnul Muslim ta ɗauka ta cigaba da Azkhar yayin da Raudat ta miƙe tabi bayan Khausar.
Ita kuwa khausar na shiga ɗaki ta hau kan stoll ta janyo trolley ɗin ta sannan tashiga haɗa kaya Raudat dake kallonta tace.
”Dani Zaki tafi Addah Khausi?”.
Girgiza mata kai Khausar tayi alamar a'a.
Kuka Raudat ta fashe dashi tana cewa.
“Ni zan biki”.
Zama Khausar tayi ta riƙe hannunta tare da langwaɓar da kai tace.
“Raudat garin bashi da daɗi fa, ga tsohuwar garin ta fiye masifa, kana yi mata kuskure kaɗan zata zane Mutum”.
Jin haka yasa Raudat ta girgiza kai tace.
“Nide ba zanje ba idan haka ne”.
Aɓangaren Momy kuwa bayan tashiga turakar Lamiɗo sunyi shirin kwanciya ta dubesa fuskarta ɗauke da murmushi me sanyi tace.
“Uhum wai ɗazu Khausar ke cemin idan Allah yakaimu gobe tana son zuwa Rugar Jauro Yaya”.
Zamanshi ya gyara tare da faɗaɗa Murmushin dake fuskarsa kana yace.
“Allah ya kaimu hakan nada kyau idan yaso tunda gobe weekend ne zamuje dukan mu kema sai ku gaisa tunda kinyi shekaru baki jeba”.
Kai ta jinjina kafin tace.
“Kai naji dadi Allah ya kaimu”.
Amin yace kana sukaci gaba da hirarsu.
Washe gari Ya kama asabar da wuri Khausar ta tashi ta gyara ɗakinta sannan ta nufi ɗakin Momy ta gyara kana ta share har zuwa falo da kuma duk sashen saida ta gyara ko wani lungu da saƙo.
Bayan ta gama ta dawo ta shiga kichen ta zuba musu Breakfast soyayyan cheaps da tea ita da Raudat ke ciki.
Bayan sun kammala ta miƙe tana ƙoƙarin tattare wajen Momy tashigo Idanunta akan Khausar.
fuska ta ɗan tsuke tare da faɗin.
“Maza kije yanzu Aunty Jamila tayi Miki kitso”.
Aunty Jamila matar ƙani Lamiɗo ne sannan Momy tasan inba tayiwa Khausar dagaske to baza taje ba domin bata ƙaunar kitso.
Ganin fuskar Momy babu walwala yasa Khausar gyaɗa kai tare da shiga Bedroom ta ɗauko dogon hijabinta fari Nevy blue daya sha ninkin guga ta ɗaura akan riga da wandon dake jikinta kana ta fice ta nufi gidan Aunty Jamila tana zumɓura baki da kuma kifiya da kum a hannunta.
Bakinta ɗauke da sallama tashiga gidan, Aunty Jamila dake zaune ta amsa Sallamar tana faɗaɗa fara'ar dake fuskarta tace.
“A'a Khausar kece?, sannu da zuwa”.
Sake fuska Khausar ta ɗanyi tace.
“Eh nice Aunty wai kitso nazo kiyi min zanje Jauro Yaya”.
Murmushi Aunty Jamila tayi tare da cewa
“Masha Allah kice zakije ziyara?”.
Kai Khausar ta gyaɗa tana murmushi.
Cikin sakin fuska Aunty Jamila tace.
“Allah Ya kaiku lafiya".
“Amin ya rabbil izzati”.
Cewar Khausar.
“Kinga kuwa kinyi sa'a duk na gama aiyuka na”.
Da sauri tace.
“Aunty Jamila manya fa zakiyi shida ko takwas”.
Murmushi Aunty Jamila tayi.
Kana ta miƙe ta shiga ɗaƙi tare da kwantar da yaronta kana ta fito,
Akan kujeran roba Khausar ta zauna ita kuma ta tsaya ta fara yi mata kitson suna cikin kitson ne suka jiyo Sallamar Gimbiya Dadu.
Anutse Aunty Jamila ta ɗago kanta fuskarta ɗauke da murmushi tace.
“Sannu da zuwa Mama”.
Asaman laɓɓa Gimbiya Dadu ta Amsawa Aunty Jamila baki ɗaya nutsuwarta da hankalinta suna kan Khausar.
Miƙewa Aunty Jamila tayi tashiga ɗaki dan ɗaukowa Gimbiya Dadu Darduman zama.
Ita kuwa khausar ahankali ta ɗago kanta caraf Idanunta suka sauƙa akan Gimbiya Dadu data tsareta da ido ita kuwa khausar cikin hanzari tayi ƙasa da idanunta tana mai karanto duk wata addu'ar da tazo bakinta kamar minti ɗaya Khausar ta sake ɗago kanta akaro na uku still Idanun Gimbiya Dadu na kanta.
Ita kuwa khausar kasa jurewa tayi ta tsayar da Idanunta akan Gimbiya Dadu cikin dakiya tace.
“Wai dan Allah Gimbiya Dadu Meyesa kike kallona haka?”.
Wani murmushi mai cike da ma'anoni Gimbiya Dadu tayi tare da cewa.
“Uhum yaro man kaza,
ai tunda kika bar cikin Awaki 'yan uwanki kika dawo cikin Kuraye ai dole akalleki! In kalleki in kuma”.
jin abinda Gimbiya Dadu tace yasa ta miƙe cikin rawan jiki da alamar tsoro aƙwayar Idanunta ta sanya hijabinta ta fita batare data jira Aunty Jamila ta fito ta ƙarasa yi mata kitson ba...
Sauri-sauri gudu-gudu take tafiya har ta isa bakin gate dinsu da sassarfa ta shigo coumpund ɗin su har yanzu jikinta be daina ɓari ba tana gyara zaman hijabin kanta Momy ta fito,Kallonta Momy tayi tare da cewa.
“Har angama kitson ne".
Ka ta gyaɗa mata ba tare da tace komai ba.
“Dama yanzu zan aika Haiydar ya kira ki kizo mu tafi”.
Murmushin karfin hali ts ƙirƙira kana tace.
“Eh mun gama”.
Wuce ta Momy tayi taje tashiga gaban mota Ita kuwa khausar kallon Raudat, Ramadan, da kuma Haiydar dake tsaye tayi tare da ɗaga musu hannu suma hannu suka ɗaga mata ahankali ta juya ta nufi wajen motar tana isa tasa hannu ta buɗe tashiga gidan baya Haiydar da Ramadan na cigaba da ɗaga mata hannun.
Babban gate mai gadin ya buɗe musu kana Lamiɗo ya cilla hancin motarsa.
Khausar kuwa jingina bayanta ajikin motar tayi tare da lumshe Idanunta zuciyarta na bugawa da mugun sauri abu biyu ne suka yiwa zuciyarta ƙawanya na farko hukuncin da Moddibo zai ɗauka akanta na biyu kalaman Gimbiya Dadu wanda suke ƙara tabbatar mata da zantuka dake yawo a gari cewa matar nan mayyace...
Anutse Momy ta dubi Moddibo dake sharara gudu akan Lafiyayyan titin nasu tace.
“Abban Haiydar gudun nan baiyi yawa ba”.
Kanshi ya ɗan jujjuya mata,
Ita kuwa cikin sanyi tace.
“Gsky dai ka rage gudun kamar yayi yawa”.
Juyowa yayi ya kalleta da murmushi a fuskarsa yace.
“Lokaci na tafiya kinga yanzu goma tayi gwara mu isa da wuri kada rana tayi mana mu samu mu juyo da wuri”.
Kai ta gyaɗa kafin tace.
“Amma duk da haka arage gudun".
Tattausan murmushin ya sakar mata tare da gyaɗa kai...
Sunyi tafiya mai tsawo kafin suka fara hango garin Atake suka fara tabbatar da sanyin da ake acikin Gembila wasa ne.
Domin tun kafin su shiga garin suka hango tamkar hayaƙi ke tashi saboda masifaffen sanyin da ake tsugawa acikin Jauro yaya suna shiga cikin garin suka fara ratsa bishiyoyi masu korayen ganye suna rangaji tare da fitar da sanyayyan Iska kasancewar hantsi ne duk makiyaya sun tafi se kuma,
'yan dalo da aka ɗaɗɗaure masu kyan launi ga kuma kukan tsuntsaye dana zabbi da ke tashi suna ajiye ƙwai.
Suna shiga tsakiyar Rugar Jauro,
kai tsaye ƙofar gidan dake kusa da babbar fadan Rugar suka nufa anan sukayi parking motar tare da fitowa.
Wasu dattawa dake zaune aƙofan masallacin dake kusa da babbar fadan suka taso baki ɗaya idanun su akan Khausar data fito daga mota tana gyara zaman hijabinta suna faɗin.
“Audiii Barka da zuwa kece?”.
ɗaya daga cikin dattijon ne ya taso wanda ya kasance shine Jauron garin ya riƙe hannun Khausar.
Fuskarsa ɗauke da murmushi yake faɗin.
”Addah, Addah, Addah, kizo ga Khausar”.
sauran ma bin bayansu sukayi zuwa cikin gidan suna masuyiwa Momy da Lamido Barka da zuwa.
Biyu daga cikine suka ce da Momy da kuma Lamiɗo.
“Sannunku da zuwa ya kuka tsaya ku shigo daga ciki”.
Kai Momy ta gyaɗa kana suka yi musu godiya bisa jagoranci suka nufi cikin gidan.
Jauro kuwa yana riƙe da hannun Khausar yana mata wasa da faɗin.
“Iyeee girman falo ji jiki kamar auduga,
bakisan riƙe sandar kiwo ba sannan baki san ta tsar nono ba girman burodi wayon shayi kawai”.
Ita kuwa khausar hannu ta wara da faɗin.
“Ban iya ba kam”.
Murmushi yayi kana yace.
“Zamu koya muki ai”.
maƙale kafaɗa tayi tace.
“Bana so ba kace min girman bread wayon tea ba”.
Murmushi yay i tare da cewa.
“To girman fura da nono”.
Akuma dai-dai lokacin suka shiga ɗakin tsohuwar wanda yake ginin gargajiya shatin kobo.
Suna shiga Jauro yace. “Addah ga 'yar Usman tazo”.
Ya mutse fuska Hajja Nana tayi tare da kallon Khausar tace.
“Shegiyar kaya me wuyar ɗauka se yau kika ga damar zuwa??”.
Murmushi Jauro yayi still hannunsa na cikin na Khausar yace.
“Tazo da mahaifiyarta da kuma Mahaifinta”.
Wani kallo Hajja Nana ta masa tare da cewa.
“Kai Jauro ka gyara kalamanka,
badai mahaifinta ba mahaifin riƙo dai ko? ka manta mahaifinta da kai aka binnesa shekaru goma sha biyar da suka wuce?”.
Kai ya jinjina alamar hakane amma bece komai ba ita kuwa miƙewa tayi ta ɗauko taburma ta shimfida tare da ɗauko darduman kilisa ta shimfiɗa.
A kuma lokacin Momy da Lamiɗo suka shigo cikin sakin fuska tashiga yi musu lale marhaba.
zama Momy da Lamiɗo sukayi akan shimfiɗar data musu kana ita kuma ta zauna awajen zamanta na farko yayin da duka ƙannenta maza suka zauna daga bayanta se ta zamto tamkar sarauniya acikinsu ko wannensu fuskarsa ɗauke da murmushi yake faɗin.
“Addah yau kam ga Khausar tazo”.
Haka yasa ta juyu.
Ta dubi Khausar da alamun farin cikin ganinta afuskarta saidai yanayin zafinta bazai sa ka fahimta ba.
Ta dubi Khausar da tayi kicin-kicin da fuska tace.
“Menene kike wani kumbura fuska? gwara ma ki saki ranki fa”.
Zumɓura baki Khausar tayi saidai ba tace komaiba.
Hajja Nana kuwa sake kallon Khausar tayi akaro na barkatai tace.
“Ki tashi ki kawo ma baƙi abin taɓawa”.
Lumshe idanu tayi kafin tace.
“Nice zan kawo abin taɓa wa?,Nima ai baƙuwa ce akawo mana dai”.