Sashe 107
Sakayyah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ahankali Lamiɗo ya sunkuyar da kansa akan Ramadan hawaye masu ɗumin gaske suka shiga zubo masa asaman kincinsa, suna ɗiga kan fuskar Ramadan tal-tal yayinda jinkinsa ya shiga tsuma.
Gimbiya Dadu kuwa bayanta ta jingina da jikin kujeran cikin sanyin murya tace.
“Allah sarki Ramadan ashe dai ciwon kan nan na ɗauka ne? Ciwo lokaci ɗaya!?”.
Akuma dai-dai lokacin Uncle Naseer ya shigo falon ganin yanayin da suke ciki ne yasa ya zauna gefen Gimbiya Dadu tare da cewa.
“A Lafiya meke faruwa?”.
Ahankali Gimbiya Dadu ta ɗago kai tare da Kallonsa tace.
“Wallahi Ramadan ne Allah ya masa rasuwa!”.
Arazane Uncle Naseer ya Kalli Gimbiya Dadu tare da kallon Ramadan dake kwance cikin wani irin yanayi yace.
“Ha'a wani irin magana ne Gimbiya Dadu ya zakice Ramadan ya rasu!? Ko ke Dr ce ya za ayi kice ya rasu taya kika gane hakan?”.
Kallonsa ya mayar kan Lamiɗo daya zubawa Ramadan ido kana yace.
“Yah Lamiɗo mu kaisa asibiti”.
Kallonsa Lamiɗo yayi tare da Girgiza masa kai still Idanunsa na nan ja jawur ruwan hawaye na kwance acikinsu yayinda jikinsa ke cigaba da tsuma zuciyarsa na harbawa da masifan ƙarfi.
Uncle Naseer kuwa hannu yasa a aljihu tare da ciro wayarsa yayi dearling number family Dr su yana ɗagawa yace dan Allah yazo ya duba yaro agida Dr ya amsa da toh.
Bayan minti 16 minute Dr yazo bayan ya duba ya tabbatar musu da Ramadan ya rasu kimanin minti talatin da suka wuce.
Sai asannan Uncle Naseer ya yarda kana ya raka Dr ya tafi yana dawowa.
Sashen Gimbiya Dadu ya hadu da Lamiɗo ya fito da Ramadan Rungume akafaɗarsa bayansa yabi Lamiɗo kuwa kai tsaye Falonsa ya nufa yana shiga ya kwantar da gawar Ramadan Atsakiyar ɗakin kana ya cire masa suturar jikinsa ɗen oh foɗimo.
Cikin rauni da tsinkewar zuciya ya nufi ɗakin Mommy a inda yabar Mommy zaune anan ya dawo ya sameta still Idanunta na zubar da hawaye masu zafi da ƙuna a zuciya.
Khausar dake gefenta ta kalleta tare da cewa.
“Mommy Meye faru me yasamu Ramadan?”.
Ahankali Mommy ta janyota jikinta tare da kwantar da ita akan cinyarta kana ta sanya hannunta akanta tana shafawa cikin sanyin murya mai cike da rauni tace.
“Khausar muyi haƙuri Ramadan kam ya tafi ya barmu.
Ubangiji Allah yajiƙan sa Allah ya masa rahma Allah yasa mai cetone”.
Cikin tsananin tashin hankali Khausar ta fashe da matsanancin kuka me tsuma zuciya yayin da ta shiga girgiza kanta kallon Mommy tayi Muryanta na rawa tace.
“Mommy Ramadan kike cewa ya rasu!? Mommy wannan wani irin magana ne!?
Dan Allah Mommy kice mafarki nake Mommy kice ba gaskiya bane!”.
Girgiza kai Mommy tayi still Hawaye na bin fuskarta amma ta gaza furta komai.
Cikin sauri Khausar ta toshe bakinta jin wani matsanancin kuka ya taho mata.
Ajiyar zuciya Lamiɗo ya sauƙe tare da ƙarasawa cikin falon ya zauna kusa da Mommy, kasancewar akan 3sitter take.
Cikin sanyi murya yace.
“Khausar kiyi haƙuri kinji ko?”.
Kallonsa tayi da jikaƙƙun Idanunta kana tace.
“Abba da gaske wai Ramadan ya rasu!?”.
Nunfashi Abba ya fesar tare da jinjina mata kai yace.
“Da gaske ne Khausar ya muka iya da hukunci Ubangiji, dama shi ya bamu Ramadan kuma shi ya karɓesa, kiyi haƙuri ki daina kukan nan kinji ko!?”.
Girgiza kai tayi tare da sake fashewa da matsanancin kuka mai gunji.
Dafa kanta Lamiɗo yayi cike da tausayawa yace.
“Kiyi haƙuri yanzu ma Naseer ya kira Dr yazo ya dubasa sannan ya tabbatar min da cewa ya rasu!”.
Cikin wani irin yanayi mai cike da ruɗu Khausar ta miƙe da gudu tare da shiga Bedroom ɗinta ta faɗa kan gado tare da sakin marayan kuka.
Lamiɗo kuwa bayan ya sake rarrashin Mommy tare da bata haƙuri da kuma nuna mata muhimmanci tawakkali da haƙuri ya mike ya fita.
Bayan angama shirya Ramadan an masa wanka an suturtasa yanda addinin Musulunci ya tsara aka kaisa gidansa na gaskiya.
Bayan andawo Lamiɗo da ƴan Uwansa da kuma Abokan arziƙi aka zauna zaman Makoki.
Wunin wannan ranan haka Mommy da Khausar suka yini cikin alhini da jimamin rashin Ramadan Hajiya Bunayya kuwa sosai tayi farin ciki sai dai kallo ɗaya zaka mata ka fuskanci mutuwar ta shigeta domin ayanda take nunawa tafi Mommy damuwa wani abin ma Mommy ke tausarta tana bata haƙuri.
Washe gari Khausar ce zaune a ƙasa Mommy na Kan kujera gabansu Kuma kayan Breakfast ne.
Cikin sanyin murya Mommy ta kalli Khausar tare da cewa.
“Khausar ki matso kici abinci”.
Girgiza kai Khausar tayi tare da kallon Mommy da kumburarrun Idanunta kana cikin sanyin murya tace.
“Mommy ba najin yunwa”.
Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe tare da rintse Idanunta kana tace.
“Khausar ki matso kici abinci bana son haka zamuyi fushi da abinda Ubangiji ya jarabcemu da shine Allah daya halicci Ramadan yafimu son sa shi ya bamu Ramadan kuma shi ya ɗauke mana shi!”.
Wasu hawaye masu masifar zafi ne suka zubowa Khausar akuncinta cikin matsanancin kuka tace.
“Mommy shikenan!, Shikenan Ramadan ya tafi baza mu sake Kallonsa ba shikenan mun ransa shi har abada. Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n”.
Kallonta Mommy tayi still Idanunta cike da ruwan hawaye Akuma dai-dai lokacin wayarta ya ɗauki ruri.
Kallon screen ɗin wayar tayi nan taga sunan Hajja Nana na yawo.
Cike da ladabi tayi Picking tare da kaiwa kunnenta tace.
“Hajja ina yini?”.
Daga ɗaya ɓangaren Hajja Nana tace.
“Lafiya lau ina Khausar!?”.
Cikin sanyin murya Mommy ta kalli Khausar da hawaye ke zuba a Idanunta kana tace.
“Gata nan”,
“Toh ki bata wayar”, cewar Hajja Nana ta.
Kai Mommy ta gyaɗa tare da miƙawa Khausar wayar.
Amsa Khausar tayi cikin Muryan kuka tayi sallama.
Cike da kulawa Hajja Nana tace.
“Ke kuma lafiya ya naji muryanki haka kukan me kike!?”.
Cikin sheshsheƙan kuka Khausar tace.
“Hajja Nana Ramadan ɗin mune ya rasu”.
Hajja Nana kuwa cikin sauri tace.
“Innalillahi Wa'inna Ilahi rajiu'n Ayyah Allah sarki Ubangiji Allah ya jiƙansa da rahma Allah yasa maicetone ai bamu da labari bamu sani ba bawa Mommy naki”.
Kai Khausar ta gyaɗa tare da miƙewa Mommy wayar.
Jin Mommy ta amshi wayar yasa Hajja Nana cewa.
“Wai ashe Ramadan ya rasu!?”.
Kai Mommy ta gyaɗa kana cikin sanyin murya tace.
“Eh Wlh”.
Ajiyar zuciya Hajja Nana ta sauke tare da cewa.
“Ikon Allah Meye sameshi haka?”.
Numfashi Mommy ta fesar tare da gyara zaman ta kana tace.
“Wallahi ciwon kai ne mako ɗaya”.
Cikin sanyin murya da tausayawa Hajja Nana tace.
“Allah sarki Allah ya gafarta masa Ubangiji yasa maicetone! Dama yanzu Malam Liman zai shigo Gembulan Insha Allah zan biyo shi muzo”.
Jinjina kai Mommy tayi cikin sanyin murya tace.
“Toh Allah ya kawo ku Lafiya mungode sosai”.
Bayan Mommy ta kashe wayar ta kalli Khausar data zubawa kayan Breakfast Ido Cike da tausayawa ta shiga lallashinta.
Acan gidan Ummi kuwa Moddibo ne zaune afalon ya tsurawa waje ɗaya Idanu yayin da Ummi kanta ke ƙasa hawaye zira-zira baki ɗayan sun zurfafa acikin tunanin da suke Asma'u ta fito daga kitchen cikin mutuwar jiki ta tsugunna kusa da Ummi kana cikin sanyin murya tace.
“Ummi”.
Ahankali Ummi ta ɗago Idanunta dake zubar da hawaye kana cikin sanyin murya tace.
“Na'am”.
Lumshe idanu Asma'u tayi tare da faɗin.
“Ummi yanzun nan mukayi waya da Khausar tace in gaisheki”.
Kai Ummi ta gyaɗa cikin sanyin murya tace.
“Ina Amsawa”.
Asma'u kuwa cikin raunin murya tace.
“Ummi wai Ramadan ya rasu fa”.
Cikin sauri Ummi ta ɗago kanta dake ƙasa ta kalli Asma'u shima Moddibo cikin sauri ya kalli Asma'u zuciyarsa na cigaba da bugawa da masifar ƙarfi.
Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe cikin raunin murya tace.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n yaushe ya rasu!?”.
Gyara zama Asma'u tayi cikin sanyin murya tace.
“Shekaran jiya fa take cemin randa tazo bayan ta koma ciwon kan ya fara mishi, sunyi ta sintirin asibiti a banza, tace shekaran jiya kuma haka aka kwana dashi haka jiya da Asbah ma ya tashi dashi washe gari da safe bayan sallar Asbah ya rasu sai bayan Azahar akayi jana'izar sa!”.
Girgiza kai Ummi tayi tare da fesar da numfashi kana tace.
“Allah sarki rayuwa Ayyah Aysha ta ɗanɗani Mutuwa mai zafi da raɗaɗi mutuwar ɗa akwai ciwo Allah ya masa rahma Allah yasa maicetone”.
Cikin sanyin murya Asma'u tace.
“Ameen Ummi”.
Jinjina kai Ummi tayi tare da cewa.
“Insha Allahu zanyi ƙoƙari muje”.
Moddibo kuwa ahankali ya buɗe Idanunsa dake lumshe ya kalli Ummi tare da cewa.
“Allah yajiƙan sa da rahma, shine yaron da Mota ya buge ko?”.
Kai Asma'u ta gyada tere da cewa.
“Eh shine”.
Cije lip ɗinsa na ƙasa yayi tare da cewa.
“Allah sarki kwanansa na gaba alokacin Allah ya gafarta masa”.
Cikin sanyi murya Ummi tace.
“Ameen”.
Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe kana yace.
“Ummi bari in tashi Inje wajen Abba naji ya ake ciki muji daga Jiya zuwa yau ko sun kira”.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Toh shikenan”.
Cikin sanyin jiki ya miƙe tare da ficewa kai tsaye gidan Abba ya nufa.
Bayan ya isa gidan ya shiga falon Abba nan ya samu Dr Muktar zaune zama gefen Abba yayi bayan sun gaisa Moddibo ya sauƙe numfashi kana cikin sanyin murya yace.
“Abba har yanzu basu kira ba”.
Kai Abba ya gyaɗa masa tare da rintse Idanunsa kana yace.
“Basu kira ba Aliyu bansan me mutanen nan suke nufi da muba”.
Tagumi Moddibo da Abba sukayi duk sunyi jugum-jugum dasu.
Misalin ƙarfe biyu da rabi na rana Hajja Nana da Malam Liman suka iso gidan Lamiɗo bayan sun gama gaishe-gaishe suka zauna har aka Idar da La'asar Lamiɗo ya shigo tare da kallon Hajja Nana kana yace.
“Hajia ki fito malam Liman yana jiranki”.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Toh gani nan fitowa”.
Kallonta ta mayar kan Mommy dake jan Carbi kana tace.
“Yanzu kam ba abinda zance miki, ta'aziyya muka zo miki amma Insha Allah kwanan nan zan dawo kan batun Khausar”.
Jinjina kai Mommy tayi tare da cewa.
“Toh shikenan Nagode Hajja Nana Allah ya saka da alkhairi”.
Gimbiya Dadu kuwa bayanta ta jingina da jikin kujeran cikin sanyin murya tace.
“Allah sarki Ramadan ashe dai ciwon kan nan na ɗauka ne? Ciwo lokaci ɗaya!?”.
Akuma dai-dai lokacin Uncle Naseer ya shigo falon ganin yanayin da suke ciki ne yasa ya zauna gefen Gimbiya Dadu tare da cewa.
“A Lafiya meke faruwa?”.
Ahankali Gimbiya Dadu ta ɗago kai tare da Kallonsa tace.
“Wallahi Ramadan ne Allah ya masa rasuwa!”.
Arazane Uncle Naseer ya Kalli Gimbiya Dadu tare da kallon Ramadan dake kwance cikin wani irin yanayi yace.
“Ha'a wani irin magana ne Gimbiya Dadu ya zakice Ramadan ya rasu!? Ko ke Dr ce ya za ayi kice ya rasu taya kika gane hakan?”.
Kallonsa ya mayar kan Lamiɗo daya zubawa Ramadan ido kana yace.
“Yah Lamiɗo mu kaisa asibiti”.
Kallonsa Lamiɗo yayi tare da Girgiza masa kai still Idanunsa na nan ja jawur ruwan hawaye na kwance acikinsu yayinda jikinsa ke cigaba da tsuma zuciyarsa na harbawa da masifan ƙarfi.
Uncle Naseer kuwa hannu yasa a aljihu tare da ciro wayarsa yayi dearling number family Dr su yana ɗagawa yace dan Allah yazo ya duba yaro agida Dr ya amsa da toh.
Bayan minti 16 minute Dr yazo bayan ya duba ya tabbatar musu da Ramadan ya rasu kimanin minti talatin da suka wuce.
Sai asannan Uncle Naseer ya yarda kana ya raka Dr ya tafi yana dawowa.
Sashen Gimbiya Dadu ya hadu da Lamiɗo ya fito da Ramadan Rungume akafaɗarsa bayansa yabi Lamiɗo kuwa kai tsaye Falonsa ya nufa yana shiga ya kwantar da gawar Ramadan Atsakiyar ɗakin kana ya cire masa suturar jikinsa ɗen oh foɗimo.
Cikin rauni da tsinkewar zuciya ya nufi ɗakin Mommy a inda yabar Mommy zaune anan ya dawo ya sameta still Idanunta na zubar da hawaye masu zafi da ƙuna a zuciya.
Khausar dake gefenta ta kalleta tare da cewa.
“Mommy Meye faru me yasamu Ramadan?”.
Ahankali Mommy ta janyota jikinta tare da kwantar da ita akan cinyarta kana ta sanya hannunta akanta tana shafawa cikin sanyin murya mai cike da rauni tace.
“Khausar muyi haƙuri Ramadan kam ya tafi ya barmu.
Ubangiji Allah yajiƙan sa Allah ya masa rahma Allah yasa mai cetone”.
Cikin tsananin tashin hankali Khausar ta fashe da matsanancin kuka me tsuma zuciya yayin da ta shiga girgiza kanta kallon Mommy tayi Muryanta na rawa tace.
“Mommy Ramadan kike cewa ya rasu!? Mommy wannan wani irin magana ne!?
Dan Allah Mommy kice mafarki nake Mommy kice ba gaskiya bane!”.
Girgiza kai Mommy tayi still Hawaye na bin fuskarta amma ta gaza furta komai.
Cikin sauri Khausar ta toshe bakinta jin wani matsanancin kuka ya taho mata.
Ajiyar zuciya Lamiɗo ya sauƙe tare da ƙarasawa cikin falon ya zauna kusa da Mommy, kasancewar akan 3sitter take.
Cikin sanyi murya yace.
“Khausar kiyi haƙuri kinji ko?”.
Kallonsa tayi da jikaƙƙun Idanunta kana tace.
“Abba da gaske wai Ramadan ya rasu!?”.
Nunfashi Abba ya fesar tare da jinjina mata kai yace.
“Da gaske ne Khausar ya muka iya da hukunci Ubangiji, dama shi ya bamu Ramadan kuma shi ya karɓesa, kiyi haƙuri ki daina kukan nan kinji ko!?”.
Girgiza kai tayi tare da sake fashewa da matsanancin kuka mai gunji.
Dafa kanta Lamiɗo yayi cike da tausayawa yace.
“Kiyi haƙuri yanzu ma Naseer ya kira Dr yazo ya dubasa sannan ya tabbatar min da cewa ya rasu!”.
Cikin wani irin yanayi mai cike da ruɗu Khausar ta miƙe da gudu tare da shiga Bedroom ɗinta ta faɗa kan gado tare da sakin marayan kuka.
Lamiɗo kuwa bayan ya sake rarrashin Mommy tare da bata haƙuri da kuma nuna mata muhimmanci tawakkali da haƙuri ya mike ya fita.
Bayan angama shirya Ramadan an masa wanka an suturtasa yanda addinin Musulunci ya tsara aka kaisa gidansa na gaskiya.
Bayan andawo Lamiɗo da ƴan Uwansa da kuma Abokan arziƙi aka zauna zaman Makoki.
Wunin wannan ranan haka Mommy da Khausar suka yini cikin alhini da jimamin rashin Ramadan Hajiya Bunayya kuwa sosai tayi farin ciki sai dai kallo ɗaya zaka mata ka fuskanci mutuwar ta shigeta domin ayanda take nunawa tafi Mommy damuwa wani abin ma Mommy ke tausarta tana bata haƙuri.
Washe gari Khausar ce zaune a ƙasa Mommy na Kan kujera gabansu Kuma kayan Breakfast ne.
Cikin sanyin murya Mommy ta kalli Khausar tare da cewa.
“Khausar ki matso kici abinci”.
Girgiza kai Khausar tayi tare da kallon Mommy da kumburarrun Idanunta kana cikin sanyin murya tace.
“Mommy ba najin yunwa”.
Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe tare da rintse Idanunta kana tace.
“Khausar ki matso kici abinci bana son haka zamuyi fushi da abinda Ubangiji ya jarabcemu da shine Allah daya halicci Ramadan yafimu son sa shi ya bamu Ramadan kuma shi ya ɗauke mana shi!”.
Wasu hawaye masu masifar zafi ne suka zubowa Khausar akuncinta cikin matsanancin kuka tace.
“Mommy shikenan!, Shikenan Ramadan ya tafi baza mu sake Kallonsa ba shikenan mun ransa shi har abada. Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n”.
Kallonta Mommy tayi still Idanunta cike da ruwan hawaye Akuma dai-dai lokacin wayarta ya ɗauki ruri.
Kallon screen ɗin wayar tayi nan taga sunan Hajja Nana na yawo.
Cike da ladabi tayi Picking tare da kaiwa kunnenta tace.
“Hajja ina yini?”.
Daga ɗaya ɓangaren Hajja Nana tace.
“Lafiya lau ina Khausar!?”.
Cikin sanyin murya Mommy ta kalli Khausar da hawaye ke zuba a Idanunta kana tace.
“Gata nan”,
“Toh ki bata wayar”, cewar Hajja Nana ta.
Kai Mommy ta gyaɗa tare da miƙawa Khausar wayar.
Amsa Khausar tayi cikin Muryan kuka tayi sallama.
Cike da kulawa Hajja Nana tace.
“Ke kuma lafiya ya naji muryanki haka kukan me kike!?”.
Cikin sheshsheƙan kuka Khausar tace.
“Hajja Nana Ramadan ɗin mune ya rasu”.
Hajja Nana kuwa cikin sauri tace.
“Innalillahi Wa'inna Ilahi rajiu'n Ayyah Allah sarki Ubangiji Allah ya jiƙansa da rahma Allah yasa maicetone ai bamu da labari bamu sani ba bawa Mommy naki”.
Kai Khausar ta gyaɗa tare da miƙewa Mommy wayar.
Jin Mommy ta amshi wayar yasa Hajja Nana cewa.
“Wai ashe Ramadan ya rasu!?”.
Kai Mommy ta gyaɗa kana cikin sanyin murya tace.
“Eh Wlh”.
Ajiyar zuciya Hajja Nana ta sauke tare da cewa.
“Ikon Allah Meye sameshi haka?”.
Numfashi Mommy ta fesar tare da gyara zaman ta kana tace.
“Wallahi ciwon kai ne mako ɗaya”.
Cikin sanyin murya da tausayawa Hajja Nana tace.
“Allah sarki Allah ya gafarta masa Ubangiji yasa maicetone! Dama yanzu Malam Liman zai shigo Gembulan Insha Allah zan biyo shi muzo”.
Jinjina kai Mommy tayi cikin sanyin murya tace.
“Toh Allah ya kawo ku Lafiya mungode sosai”.
Bayan Mommy ta kashe wayar ta kalli Khausar data zubawa kayan Breakfast Ido Cike da tausayawa ta shiga lallashinta.
Acan gidan Ummi kuwa Moddibo ne zaune afalon ya tsurawa waje ɗaya Idanu yayin da Ummi kanta ke ƙasa hawaye zira-zira baki ɗayan sun zurfafa acikin tunanin da suke Asma'u ta fito daga kitchen cikin mutuwar jiki ta tsugunna kusa da Ummi kana cikin sanyin murya tace.
“Ummi”.
Ahankali Ummi ta ɗago Idanunta dake zubar da hawaye kana cikin sanyin murya tace.
“Na'am”.
Lumshe idanu Asma'u tayi tare da faɗin.
“Ummi yanzun nan mukayi waya da Khausar tace in gaisheki”.
Kai Ummi ta gyaɗa cikin sanyin murya tace.
“Ina Amsawa”.
Asma'u kuwa cikin raunin murya tace.
“Ummi wai Ramadan ya rasu fa”.
Cikin sauri Ummi ta ɗago kanta dake ƙasa ta kalli Asma'u shima Moddibo cikin sauri ya kalli Asma'u zuciyarsa na cigaba da bugawa da masifar ƙarfi.
Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe cikin raunin murya tace.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n yaushe ya rasu!?”.
Gyara zama Asma'u tayi cikin sanyin murya tace.
“Shekaran jiya fa take cemin randa tazo bayan ta koma ciwon kan ya fara mishi, sunyi ta sintirin asibiti a banza, tace shekaran jiya kuma haka aka kwana dashi haka jiya da Asbah ma ya tashi dashi washe gari da safe bayan sallar Asbah ya rasu sai bayan Azahar akayi jana'izar sa!”.
Girgiza kai Ummi tayi tare da fesar da numfashi kana tace.
“Allah sarki rayuwa Ayyah Aysha ta ɗanɗani Mutuwa mai zafi da raɗaɗi mutuwar ɗa akwai ciwo Allah ya masa rahma Allah yasa maicetone”.
Cikin sanyin murya Asma'u tace.
“Ameen Ummi”.
Jinjina kai Ummi tayi tare da cewa.
“Insha Allahu zanyi ƙoƙari muje”.
Moddibo kuwa ahankali ya buɗe Idanunsa dake lumshe ya kalli Ummi tare da cewa.
“Allah yajiƙan sa da rahma, shine yaron da Mota ya buge ko?”.
Kai Asma'u ta gyada tere da cewa.
“Eh shine”.
Cije lip ɗinsa na ƙasa yayi tare da cewa.
“Allah sarki kwanansa na gaba alokacin Allah ya gafarta masa”.
Cikin sanyi murya Ummi tace.
“Ameen”.
Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe kana yace.
“Ummi bari in tashi Inje wajen Abba naji ya ake ciki muji daga Jiya zuwa yau ko sun kira”.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Toh shikenan”.
Cikin sanyin jiki ya miƙe tare da ficewa kai tsaye gidan Abba ya nufa.
Bayan ya isa gidan ya shiga falon Abba nan ya samu Dr Muktar zaune zama gefen Abba yayi bayan sun gaisa Moddibo ya sauƙe numfashi kana cikin sanyin murya yace.
“Abba har yanzu basu kira ba”.
Kai Abba ya gyaɗa masa tare da rintse Idanunsa kana yace.
“Basu kira ba Aliyu bansan me mutanen nan suke nufi da muba”.
Tagumi Moddibo da Abba sukayi duk sunyi jugum-jugum dasu.
Misalin ƙarfe biyu da rabi na rana Hajja Nana da Malam Liman suka iso gidan Lamiɗo bayan sun gama gaishe-gaishe suka zauna har aka Idar da La'asar Lamiɗo ya shigo tare da kallon Hajja Nana kana yace.
“Hajia ki fito malam Liman yana jiranki”.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Toh gani nan fitowa”.
Kallonta ta mayar kan Mommy dake jan Carbi kana tace.
“Yanzu kam ba abinda zance miki, ta'aziyya muka zo miki amma Insha Allah kwanan nan zan dawo kan batun Khausar”.
Jinjina kai Mommy tayi tare da cewa.
“Toh shikenan Nagode Hajja Nana Allah ya saka da alkhairi”.