Sashe 51
Sakayyah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Mommy ce tashiga ɗakin bakinta ɗauke da sallama kallon Asma'u tayi kana tace.
“A'a Asma'u kece yaushe kika zo”.
Asma'u kuwa zamewa tayi daga kan gadon tare da cewa.
“Ban daɗe da zuwa ba Mommy Ina yini?”.
Mommy ta amsa da.
“Lafiya lau alhamdulillah yasu Umminki?”.
Miƙewa Asma'u tayi tare da zama agefen gadon kana tace.
“Tace agaisheki”.
Masha Allah Mommy ta faɗa tare da maida kallonta kan Dije kana tace.
“Dije kizo Hajja Nana na kiranki wai zaki rakata gidan Aminiyarta”.
Ta ida maganar tare da juyawa ta fice.
Miƙewa Dije tayi tare da kallon Khausar kana tace.
“Khausar mu tafi mana”.
Fuska Khausar taya mutse kana tace.
“A'a kuje kawai Allah ya kiyaye hanya ni bazan jeba, muyita faɗa da ita a gidan mutane muna raba hali agidan mutane duk inda mukaje sai ansan mu”.
Murmushi Dije tayi tare da faɗin.
“Toh shikenan mun tafi”.
Sannan ta fice kai tsaye ɗakin Mommy ta wuce sannan ta samu Hajja Nana atsaye.
Hajja Nana na kallonta tace.
“Wuce ki kira su Aliyu mu tafi”.
Kai Dije ta gyaɗa sannan ta fice.
Mommy kuwa Jakar data haɗa wa Hajja Nana tsaraba ta ɗauka sannan ta fice.
A coumpund ɗin ta samu Yaya Aliyu da Yaya Abba tsaye jikin mota cike da girmamawa da kuma ladabi Ya Aliyu ya kalli Mommy tare da cewa.
“Toh Mommy mun gode Allah ya saka da alkhairi Allah yabar zumunci”.
Murmushi Mommy tayi tare da cewa.
“Amin, Allah ya tsare muku hanya”.
Hajja Nana ta amsa da.
“Ameen”.
Tare da buɗe bayan motar tashiga Dije ta zauna agefenta Yaya Aliyu na gefen mai zaman banza Yah Abba kuwa shike Driving suka fice daga gidan.
Sai da Mommy taga fitar su sannan ta koma cikin gida.
Yaya Abba kuwa kai tsaye gidan su Moddibo ya nufa.
Hajja Nana nayi masa kwatance har suka isa gida suna shiga gidan.
Cikin sauri Yaya Ali ya lumshe Idanunsa kana yace.
“Masha Allah wlh Ina son garin Gembulan nan saboda yana da kyawun tsari dan yafi Adamawa kyawun tsari da komai akwai yanayin sanyi da daɗi”.
Jinjina kai Yaya Abba yayi yace.
“Aikam sosai ma”.
Yaya Ali ya juya tare da kallon Hajja Nana kana yace.
“Hajja Nana wannan kuma gidan wacece ɗinkin ne?”.
Murmushi Hajja Nana tayi alokacin da take sauƙa amotar ta kalli Ali kana tace.
“Ƙawata ce tare mukaje da ita aikin hajji na farko na biyu ma tare muka je sannan ko daga baya muna yawan zuwa Umarah tare da ita”.
Murmushi Yaya Ali yayi tare da cewa.
“Ai dai lalle kam kice gidan Aminiyar kice?”.
Dariya Hajja Nana tayi tare da cewa.
“A'a sosai ma kam”.
Dai-dai lokacin da suka isa ƙaramin gate ɗin da zai sadaka da farfajiyar tsakar gidan Innayi.
Innayi dake zaune ta hango Hajja Nana da baƙi abayanta,
Cike da fara'a ta miƙe da sauri fuskarta ɗauke da ƙayataccen murmushi mai cike da jin daɗi ta matso kusa da Hajja Nana kana tace.
“Aaaa Lalle marhaba Hajjaju Makkatun Masha Allah Hajiya Nana mutanen Makka lale marhaba ku iso”.
Ta faɗa tare da juyawa ta shiga ɗaki tare da ɗaukan lallausan Chanis capet ta shimfiɗa musu.
Sai kuma ta fito cike da farin cikin daya kasa ɓoyuwa afuskarta kallon Yaya Ali tayi tare da cewa.
“Wannan shine Mijin namu na Adamawa da kike bamu labarin?”.
Kai Hajja Nana ta gyaɗa tana murmushi kana tace.
“Eh”.
Innayi ta juya ta kalli Hajja Nana kana tace.
“Ku shiga”.
Sannan ta kalli Yaya Abba da Yaya Ali kana tace.
“Ku ƙara so”.
Ta faɗa tare da ficewa Innayi ta nufi sashen Moddibo tare da cewa.
“Moddibo, Moddibo ga baƙi munyi”
Shi kuwa Moddibo atare suka miƙe da M Jameel suka fito.
Ɗan sake fuska Moddibo yayi kana yace.
“Sannunku da zuwa ku iso”.
ya faɗa tare da matsa musu.
M Jameel na ganin Yaya Abba ya miƙa masa hannu fuskarsa ɗauke da murmushi kana yace.
“Ha'a Abba kaine?”.
Murmushi Yaya Abba yayi kana yace.
“Ni ne dai”.
M Jameel yayi dariya kana yace.
“Sannu ku da zuwa”.
Yaya Abba na bin bayansu yace.
“Laaa Jameel nan gidan kune?”.
M Jameel yayi Murmushi tare da shafa sajensa ya kalli Yaya Abba tare da faɗin.
“Eh gidan mune!”
Murmushi Yaya Abba yayi da faɗin.
“Masha Allah”.
sannan suka shiga falon din wanda tuni Ya Ali da Moddibo suka shiga.
Innayi dake tsaye ta juya tare da cewa.
“Moddibo zoka kawo musu abin taɓa wa”.
Daga ciki Moddibo ya miƙe kana yace.
“Toh Innayi”.
Sannan ya fice tare da bin bayanta.
Juyawa Innayi tayi tare da kallon Moddibo dake biye da ita kana tace.
“Kashiga daga ciki ka gaida ƙawata Hajja Nana dana ke ce maka munje aikin Hajji na farko dana biyu kuma yawanci Umarah ma tare muke zuwa ɗakin mu ɗaya tun da take zuwa gidan nan bata taɓa samunkaba,
Kai ya gyaɗa da faɗin.
“Na'am”.Ya ida maganar tare da shiga ɗakin bakinsa ɗauke da sallama Idanunsa ya sauƙa akan tsohuwar da yaje ya yamata ta'aziyya a Jauro Yaya.
Cike da nutsuwa da kuma ladabi ya zauna daga gefenta kana yasa hannu ya shafa sajensa cikin yanayin rashin walwalarsa yayi ƙasa da kansa tare da cewa.
“Sannun da zuwa”,Ya gaisheta batare daya nuna ya ganeta ba.
Hajja Nana kuwa Kallonsa tayi kana tace.
“A'a kamar nasan wannan fuskarta fa, kwanaki kamar kunje da wani abokin Malam Liman mai suna Malam Arɗo ko?”.
Kai Moddibo ya jinjina still Kansa a ƙasa kana yace.
“Eh”.
Murmushi Hajja Nana tayi kana tace.
“Ayyah sannun ka ashe dai Jikana ne Allah yayiwa rayuwarka albarka Allah yabaka zuri'a ɗayyiban”.
Still Kansa A ƙasa ya shafa kwantaccen sumar kansa mai sheƙi da yalƙi kana yace.
“Ameen Ngd”.
Ya ida maganar a taƙaice tare da miƙewa ya fice.
Tiren da Innayi ta haɗa Gasassun Zabbi da M jameel yasa ta gasa musu, shinkafa da miyar dage-dage da yaji naman kaza sai Akwashi dake ɗauke da ƴaƴan itatuwa ta miƙawa Moddibo amsa yayi kana ya nufi sashen sa dashi.
Bakinsa ɗauke da Sallama yashiga tare da ajiye Tiren akan center table dake tsakiyar falon kana ya maida kallonsa kan M Jameel dake ta hiran Yaushe gamo da Yaya Abba kai ya girgiza tare da cewa.
“J miƙo musu ruwa acikin fridge ka barsu haka gashi har na dawo baka kawo musu komai ba”.
Murmushi M Jameel yayi kana yace.
“Wallahi muna ta hiran yaushe gamo da Abba nasan sa mun taɓa haɗuwa dashi a Adamawa”.
Jinjina kai Moddibo yayi tare da jingina bayansa da jikin kushin kana ya lumshe idanunsa tare da cewa.
“Ayyah ashe kunsan juna”.
Kai Yaya Abba ya gyaɗa alamar Eh.
Ya Ali kuwa hankalin sa ya mayar kan wayarsa yana latsawa.
Acan ɗakin Innayi kuwa zama Innayi tayu tare da kallon Hajja Nana kana tace.
“Yanzu ma kinzo wajen jikar tamu ce?”.
Kai Hajja Nana ta gyaɗa kana tace.
“Eh wallahi".
Murmushi Innayi tayi tare da cewa.
“Shine baki zomin da ita ba”.
Baki Hajja Nana ta taɓe tare da faɗin.
“Barta ba shiri muke da ita ba fitsararriya ce yanzu ma nazo ne akan batun aurenta da yayan ta amma na lura ma kamar batason abin ko yayane ohon mata kinsan ƴaƴan yanzu da tsaurin ido su suke zaɓawa kansu maza yanzu ma na barta tana can tana kumbure kumburen baki”.
Murmushi Dije da ke kurɓan tes tayi aranta tace Dramer Hajja Nana da Khausar bai ƙarewa.
Innayi kuwa murmushi tayi kana tace.
“Ayyah ai da tazo na ganta kice mu shirya akwai shan biki?”.
Dariya Hajja Nana tayi kana tace.
“Ai dai kam Insha Allah akwai shan biki dan biki yana nan yana tafe”.
Innayi kuwa kai ta gyaɗa kana tace.
“Lallai abu yayi kyau amma dai zamu kwana”.
Girgiza kai Hajja Nana tayi kana tace.
“A'a yanzu ma zamu tafi dan mun sallami can kam da zan tafi da jikar tawa ma to sai mahaifiyata take ce min bata da lafiya don haka na barta saboda tana taimakawa mahaifiyar tan da ɗan aikace-aikacen yau da kullum”.
Kai Innayi ta jinjina tare da faɗin.
“Ayyah Allah yabata lafiya.
Yaushe zamu koma Umarah bana zaki je na Ramadan?”.
Hajja Nana kuwa kai ta jinjina kana tace.
“Eh Insha Allahu zanje in Allah ya yarda amman ta Adamawa zan tashi kefa zakije kuwa?”.
Murmushi Innayi tayi tare da cewa.
“Nima zanje in Allah ya yarda amman kin san ni ta nan Jaligo zan tashi”.
Kai Hajja Nana ta gyaɗa tare da faɗin.
“Abu yayi kyau Ubangiji Allah yasanya alkhairi Allah ya bamu sa'a”.
Innayi ta amsa da.
“Ameen”,kana ta cigaba da cewa.
“Nima zamu tafi da jikina da kuma abokinsa tare za muje”.
Dariya Hajja Nana tayi kana tace.
“A'a abu yayi kyau to sai mun haɗu acan ɗin”.
Hiran yaushe gamu suka cigaba dayi yayin da Dije ke gefe tana yagar Gashesh-shen Zabbi da nonon shanu mai ɗumi.
Acan falon Moddibo kuwa bayan sun gama gaisawa Yaya Abba da Yaya Ali suka sha fruit din kana suka ci gashshen Naman dake fitar da ƙamshi tare da ruwan Tea mai zafi.
M Jameel ya kalli Yaya Abba daya koma ya zauna tare da rufe Warmers din Cike da kulawa ya sake Kallonsa kana yace.
“Abba ya bakuci abincin ba”.
Murmushi Yaya Abba yayi kana yace.
“Wallahi aƙoshe muke yanzu ma dan kar kuce munƙi cin komai ne amma Alhamdulillah”.
Murmushi M Jameel yayi kana yace.
“Toh shikenan”.
Miƙewa sukayi Atare jin Innayi na cewa.
“Moddibo kufita Hajja Nana zasu wuce”.
Da to Moddibo ya amsa kana suka fita cike da kulawa M Jameel da Moddibo suka kalli yaya Abba da yaya Ali atare suka haɗa baki wajen faɗin.
“Toh mun gode da ziyara Allah yabar zumunci”.
Yaya Ali ya amsa da.
“Ameen”.
Sannan Yaya Abba yashiga mazaunin Driver Yaya Ali kuma ya zauna gefen mai zaman Banza yayin da Hajja Nana da Dije suka zauna abaya M Jameel ya miƙa kansa ta window tare da ajiye wa Hajja Nana kuɗi akan cinyarta tare da cewa.
“Allah ya tsare”.
Murmushi tayi kana tace.
“Allah ya muku albarka nagode”.
Motar Yaya Abba yaja suka fice saida motar ta fita layinsu kafin Innayi, Moddibo,da kuma M Jameel suka koma cikin gida.
“A'a Asma'u kece yaushe kika zo”.
Asma'u kuwa zamewa tayi daga kan gadon tare da cewa.
“Ban daɗe da zuwa ba Mommy Ina yini?”.
Mommy ta amsa da.
“Lafiya lau alhamdulillah yasu Umminki?”.
Miƙewa Asma'u tayi tare da zama agefen gadon kana tace.
“Tace agaisheki”.
Masha Allah Mommy ta faɗa tare da maida kallonta kan Dije kana tace.
“Dije kizo Hajja Nana na kiranki wai zaki rakata gidan Aminiyarta”.
Ta ida maganar tare da juyawa ta fice.
Miƙewa Dije tayi tare da kallon Khausar kana tace.
“Khausar mu tafi mana”.
Fuska Khausar taya mutse kana tace.
“A'a kuje kawai Allah ya kiyaye hanya ni bazan jeba, muyita faɗa da ita a gidan mutane muna raba hali agidan mutane duk inda mukaje sai ansan mu”.
Murmushi Dije tayi tare da faɗin.
“Toh shikenan mun tafi”.
Sannan ta fice kai tsaye ɗakin Mommy ta wuce sannan ta samu Hajja Nana atsaye.
Hajja Nana na kallonta tace.
“Wuce ki kira su Aliyu mu tafi”.
Kai Dije ta gyaɗa sannan ta fice.
Mommy kuwa Jakar data haɗa wa Hajja Nana tsaraba ta ɗauka sannan ta fice.
A coumpund ɗin ta samu Yaya Aliyu da Yaya Abba tsaye jikin mota cike da girmamawa da kuma ladabi Ya Aliyu ya kalli Mommy tare da cewa.
“Toh Mommy mun gode Allah ya saka da alkhairi Allah yabar zumunci”.
Murmushi Mommy tayi tare da cewa.
“Amin, Allah ya tsare muku hanya”.
Hajja Nana ta amsa da.
“Ameen”.
Tare da buɗe bayan motar tashiga Dije ta zauna agefenta Yaya Aliyu na gefen mai zaman banza Yah Abba kuwa shike Driving suka fice daga gidan.
Sai da Mommy taga fitar su sannan ta koma cikin gida.
Yaya Abba kuwa kai tsaye gidan su Moddibo ya nufa.
Hajja Nana nayi masa kwatance har suka isa gida suna shiga gidan.
Cikin sauri Yaya Ali ya lumshe Idanunsa kana yace.
“Masha Allah wlh Ina son garin Gembulan nan saboda yana da kyawun tsari dan yafi Adamawa kyawun tsari da komai akwai yanayin sanyi da daɗi”.
Jinjina kai Yaya Abba yayi yace.
“Aikam sosai ma”.
Yaya Ali ya juya tare da kallon Hajja Nana kana yace.
“Hajja Nana wannan kuma gidan wacece ɗinkin ne?”.
Murmushi Hajja Nana tayi alokacin da take sauƙa amotar ta kalli Ali kana tace.
“Ƙawata ce tare mukaje da ita aikin hajji na farko na biyu ma tare muka je sannan ko daga baya muna yawan zuwa Umarah tare da ita”.
Murmushi Yaya Ali yayi tare da cewa.
“Ai dai lalle kam kice gidan Aminiyar kice?”.
Dariya Hajja Nana tayi tare da cewa.
“A'a sosai ma kam”.
Dai-dai lokacin da suka isa ƙaramin gate ɗin da zai sadaka da farfajiyar tsakar gidan Innayi.
Innayi dake zaune ta hango Hajja Nana da baƙi abayanta,
Cike da fara'a ta miƙe da sauri fuskarta ɗauke da ƙayataccen murmushi mai cike da jin daɗi ta matso kusa da Hajja Nana kana tace.
“Aaaa Lalle marhaba Hajjaju Makkatun Masha Allah Hajiya Nana mutanen Makka lale marhaba ku iso”.
Ta faɗa tare da juyawa ta shiga ɗaki tare da ɗaukan lallausan Chanis capet ta shimfiɗa musu.
Sai kuma ta fito cike da farin cikin daya kasa ɓoyuwa afuskarta kallon Yaya Ali tayi tare da cewa.
“Wannan shine Mijin namu na Adamawa da kike bamu labarin?”.
Kai Hajja Nana ta gyaɗa tana murmushi kana tace.
“Eh”.
Innayi ta juya ta kalli Hajja Nana kana tace.
“Ku shiga”.
Sannan ta kalli Yaya Abba da Yaya Ali kana tace.
“Ku ƙara so”.
Ta faɗa tare da ficewa Innayi ta nufi sashen Moddibo tare da cewa.
“Moddibo, Moddibo ga baƙi munyi”
Shi kuwa Moddibo atare suka miƙe da M Jameel suka fito.
Ɗan sake fuska Moddibo yayi kana yace.
“Sannunku da zuwa ku iso”.
ya faɗa tare da matsa musu.
M Jameel na ganin Yaya Abba ya miƙa masa hannu fuskarsa ɗauke da murmushi kana yace.
“Ha'a Abba kaine?”.
Murmushi Yaya Abba yayi kana yace.
“Ni ne dai”.
M Jameel yayi dariya kana yace.
“Sannu ku da zuwa”.
Yaya Abba na bin bayansu yace.
“Laaa Jameel nan gidan kune?”.
M Jameel yayi Murmushi tare da shafa sajensa ya kalli Yaya Abba tare da faɗin.
“Eh gidan mune!”
Murmushi Yaya Abba yayi da faɗin.
“Masha Allah”.
sannan suka shiga falon din wanda tuni Ya Ali da Moddibo suka shiga.
Innayi dake tsaye ta juya tare da cewa.
“Moddibo zoka kawo musu abin taɓa wa”.
Daga ciki Moddibo ya miƙe kana yace.
“Toh Innayi”.
Sannan ya fice tare da bin bayanta.
Juyawa Innayi tayi tare da kallon Moddibo dake biye da ita kana tace.
“Kashiga daga ciki ka gaida ƙawata Hajja Nana dana ke ce maka munje aikin Hajji na farko dana biyu kuma yawanci Umarah ma tare muke zuwa ɗakin mu ɗaya tun da take zuwa gidan nan bata taɓa samunkaba,
Kai ya gyaɗa da faɗin.
“Na'am”.Ya ida maganar tare da shiga ɗakin bakinsa ɗauke da sallama Idanunsa ya sauƙa akan tsohuwar da yaje ya yamata ta'aziyya a Jauro Yaya.
Cike da nutsuwa da kuma ladabi ya zauna daga gefenta kana yasa hannu ya shafa sajensa cikin yanayin rashin walwalarsa yayi ƙasa da kansa tare da cewa.
“Sannun da zuwa”,Ya gaisheta batare daya nuna ya ganeta ba.
Hajja Nana kuwa Kallonsa tayi kana tace.
“A'a kamar nasan wannan fuskarta fa, kwanaki kamar kunje da wani abokin Malam Liman mai suna Malam Arɗo ko?”.
Kai Moddibo ya jinjina still Kansa a ƙasa kana yace.
“Eh”.
Murmushi Hajja Nana tayi kana tace.
“Ayyah sannun ka ashe dai Jikana ne Allah yayiwa rayuwarka albarka Allah yabaka zuri'a ɗayyiban”.
Still Kansa A ƙasa ya shafa kwantaccen sumar kansa mai sheƙi da yalƙi kana yace.
“Ameen Ngd”.
Ya ida maganar a taƙaice tare da miƙewa ya fice.
Tiren da Innayi ta haɗa Gasassun Zabbi da M jameel yasa ta gasa musu, shinkafa da miyar dage-dage da yaji naman kaza sai Akwashi dake ɗauke da ƴaƴan itatuwa ta miƙawa Moddibo amsa yayi kana ya nufi sashen sa dashi.
Bakinsa ɗauke da Sallama yashiga tare da ajiye Tiren akan center table dake tsakiyar falon kana ya maida kallonsa kan M Jameel dake ta hiran Yaushe gamo da Yaya Abba kai ya girgiza tare da cewa.
“J miƙo musu ruwa acikin fridge ka barsu haka gashi har na dawo baka kawo musu komai ba”.
Murmushi M Jameel yayi kana yace.
“Wallahi muna ta hiran yaushe gamo da Abba nasan sa mun taɓa haɗuwa dashi a Adamawa”.
Jinjina kai Moddibo yayi tare da jingina bayansa da jikin kushin kana ya lumshe idanunsa tare da cewa.
“Ayyah ashe kunsan juna”.
Kai Yaya Abba ya gyaɗa alamar Eh.
Ya Ali kuwa hankalin sa ya mayar kan wayarsa yana latsawa.
Acan ɗakin Innayi kuwa zama Innayi tayu tare da kallon Hajja Nana kana tace.
“Yanzu ma kinzo wajen jikar tamu ce?”.
Kai Hajja Nana ta gyaɗa kana tace.
“Eh wallahi".
Murmushi Innayi tayi tare da cewa.
“Shine baki zomin da ita ba”.
Baki Hajja Nana ta taɓe tare da faɗin.
“Barta ba shiri muke da ita ba fitsararriya ce yanzu ma nazo ne akan batun aurenta da yayan ta amma na lura ma kamar batason abin ko yayane ohon mata kinsan ƴaƴan yanzu da tsaurin ido su suke zaɓawa kansu maza yanzu ma na barta tana can tana kumbure kumburen baki”.
Murmushi Dije da ke kurɓan tes tayi aranta tace Dramer Hajja Nana da Khausar bai ƙarewa.
Innayi kuwa murmushi tayi kana tace.
“Ayyah ai da tazo na ganta kice mu shirya akwai shan biki?”.
Dariya Hajja Nana tayi kana tace.
“Ai dai kam Insha Allah akwai shan biki dan biki yana nan yana tafe”.
Innayi kuwa kai ta gyaɗa kana tace.
“Lallai abu yayi kyau amma dai zamu kwana”.
Girgiza kai Hajja Nana tayi kana tace.
“A'a yanzu ma zamu tafi dan mun sallami can kam da zan tafi da jikar tawa ma to sai mahaifiyata take ce min bata da lafiya don haka na barta saboda tana taimakawa mahaifiyar tan da ɗan aikace-aikacen yau da kullum”.
Kai Innayi ta jinjina tare da faɗin.
“Ayyah Allah yabata lafiya.
Yaushe zamu koma Umarah bana zaki je na Ramadan?”.
Hajja Nana kuwa kai ta jinjina kana tace.
“Eh Insha Allahu zanje in Allah ya yarda amman ta Adamawa zan tashi kefa zakije kuwa?”.
Murmushi Innayi tayi tare da cewa.
“Nima zanje in Allah ya yarda amman kin san ni ta nan Jaligo zan tashi”.
Kai Hajja Nana ta gyaɗa tare da faɗin.
“Abu yayi kyau Ubangiji Allah yasanya alkhairi Allah ya bamu sa'a”.
Innayi ta amsa da.
“Ameen”,kana ta cigaba da cewa.
“Nima zamu tafi da jikina da kuma abokinsa tare za muje”.
Dariya Hajja Nana tayi kana tace.
“A'a abu yayi kyau to sai mun haɗu acan ɗin”.
Hiran yaushe gamu suka cigaba dayi yayin da Dije ke gefe tana yagar Gashesh-shen Zabbi da nonon shanu mai ɗumi.
Acan falon Moddibo kuwa bayan sun gama gaisawa Yaya Abba da Yaya Ali suka sha fruit din kana suka ci gashshen Naman dake fitar da ƙamshi tare da ruwan Tea mai zafi.
M Jameel ya kalli Yaya Abba daya koma ya zauna tare da rufe Warmers din Cike da kulawa ya sake Kallonsa kana yace.
“Abba ya bakuci abincin ba”.
Murmushi Yaya Abba yayi kana yace.
“Wallahi aƙoshe muke yanzu ma dan kar kuce munƙi cin komai ne amma Alhamdulillah”.
Murmushi M Jameel yayi kana yace.
“Toh shikenan”.
Miƙewa sukayi Atare jin Innayi na cewa.
“Moddibo kufita Hajja Nana zasu wuce”.
Da to Moddibo ya amsa kana suka fita cike da kulawa M Jameel da Moddibo suka kalli yaya Abba da yaya Ali atare suka haɗa baki wajen faɗin.
“Toh mun gode da ziyara Allah yabar zumunci”.
Yaya Ali ya amsa da.
“Ameen”.
Sannan Yaya Abba yashiga mazaunin Driver Yaya Ali kuma ya zauna gefen mai zaman Banza yayin da Hajja Nana da Dije suka zauna abaya M Jameel ya miƙa kansa ta window tare da ajiye wa Hajja Nana kuɗi akan cinyarta tare da cewa.
“Allah ya tsare”.
Murmushi tayi kana tace.
“Allah ya muku albarka nagode”.
Motar Yaya Abba yaja suka fice saida motar ta fita layinsu kafin Innayi, Moddibo,da kuma M Jameel suka koma cikin gida.