Sashe 64
Fuska Uku Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Gidan Mai unguwa Sabi'u ya soma zuwa ya kuma sanar da abinda ya kawosa cewa sak'o yazo badawa ga mahaifan Aliyu, Mai Unguwa ya buk'aci a kirawo Malam Sanda saidai Sabi'u ya nuna yafiso idan da hali a kaisa can gidan Malam Sandan ya fad'i masu sak'om domin kaman hakan zaifi...
Mai Unguwa ya jinjina kai kana ya kirawo d'aya daga cikin 'yan fadansa yace suyiwa bak'om rakiya zuwa gidan Malam Sanda...
Tafiyace mai d'an rata kad'an dashike gidan ba'a cikin gari yake ba kafin suka isa....
Sank'ira yayi sallama k'ofar gidan Malam Sanda, baki na biyu aka amsa daga ciki kafin Malam Sanda ya fito suna gaisawa da Sankira... Nan Sankira yake masa nuni da bak'on da yazo nemansa daga can birnin tarayya
Malam Sanda ya maido da dubansa ga Sabi'u kafin ya mik'a masa hannu sukayi masabaha, cikeda rusunawa Sabi'u ke gaida Malam Sanda kafin Sankira ya masu sallama yace ya barsu lafiya...
Malam Sanda ya dubi Sabi'u kana yace "Toh bawan Allah gashi ban wayeka ba, lafiya dai koh...?"
Sabi'u ya d'an gyara tsayuwarsa kana yace "Toh wato Baba wani Al'amari ke tafe dani, kuma akan D'anka Ahidjo ne, amma idan bazaka damu ba zanso mu shiga daga ciki sai na sanar dakai komai gaban sauran iyalan naka domin Ahidjo ya sanar dani yanada iyali a nan gida..."
Baffah ya jinjina kai kana yace "Haka ne, amma abinda ban gane ba shine wani sak'o ne zai baka dashi bazai iya zuwa ba, wato abin nasa har ya kai ya daina zuwa saidai yayo aike, toh idanma wani abin ya baka ka kawo mana ka maida masa kayansa don dagani har iyalaina bamuda buk'ata...."
Shiru Sabi'u yayi yana duban Malam sanda had'i da karantarsa kana ya d'anyi gyaran murya yace "Baba wato wannan Al'amari da zan sanar daku Al'amari ne mai girma, kayi hak'uri mu shiga daga ciki, ka zauna kaima domin sak'o na magana zan sanar daku ba ta dukiya ko na wani abu makamancin haka ba... Dan Allah Baba..." Ya k'arashe cikin k'ank'an dakai...
Shiru tamkar Malam Sanda bazaice komai ba sai kuma yace "Shikenan mu shiga daga ciki...
Baffah da kansa yayiwa Sabi'u shimfid'a kafin ya kirawo Innah, ganin Baffah da bak'o matashi ya sanya jikin Innah yin sanyi don ba kowa ya fad'o mata ba face tilon d'anta, gaisawa Innah sukayi da Sabi'u kafin Baffah ya buk'aci ta kirawo Deejoh su taho tare...
Nan Innah ke sanar da Baffan Deejohn bataji dad'i ba tun safe zazzab'i ya rufeta, bata gane jikin ba....
Baffah yace "Subhanallah yaya baki sanar dani ba...?".
Naga zazzab'in ya d'an sauk'a ne shiyasa ban sanar dakai ba amma yanzu haka ma bacci take..."
Baffah ya jinjina kai kana yace "Ki zauna toh wannan bawan Allah sak'o yaron nan ya basa ya kawo mana..."
Jin haka yasa k'irjin Innah bugawa da k'arfin gaske domin kuwa tabbas tasan Ahidjo Baffah ke nufi, lokaci guda ta nemi waje ta zauna k'irjinta naci gaba da bugu, don haka kurum ta tsinci kanta da tsoron jin sak'on da za'a isar masun
***
*A garin Damaturu*
Yau yake cika sati biyu cif a asibitin, a hankali ya soma motsa d'an yatsansa, yana mai k'ok'arin bud'e idanunsa da suka masa nauyi tamkar an d'aura masa manyan duwatsu, da kad'an kad'an idanun nasa suka bud'e gaba d'aya... Nurse dake k'ok'arin d'aura drip mamakine ya cikata taga abinda batayi zato ba.... A guje ta fice kiran Dr Sahal hakan yayi dai-dai da shigowarsu Baba Malam da kuma Hafiz, ganin Nurse d'in ta fito daga d'akin a guje ya sanyasu nufan d'akin cikin sauri...
*Toh fah mai karatu wasan zai soma... Just stay tuned guys*
*SameenaAleeyou📚**FUSKA UKU*🏮
*45*
*©Sameena Aleeyou...✍🏽*
Sabi'u yayi gyaran murya kafin yaci gaba da fad'in "Nidai sunana Detective Sabi'u Lawan, kuma ni abokin aikin Ahidjo ne, munsan juna sama da shekara biyar sannan mu aminan juna ne domin mun wuce abokai wannan dalili yasa ya sanar dani labarinku don ko matarsa batasan daku ba...." Fasali ya d'an ja kafin yaci gaba da fad'in "Baba, Iya wato gaskiya kuyi hak'uri da batun da zakuji daga bakina..."
Inna da tuni hawaye ya soma fitowa daga idanunta cikin tsananin tashin hankali ta tari Sabi'u da fad'in "Bawan Allah dan Allah ka sanar damu mai ya sami d'anmu ka rik'e bayananka sai ka sanar damu halin da yake ciki na rok'i aezikinka..." Ta k'arashe cikin tsananin rawar murya... Baffah kam bai ma iya furta komai ba sai k'uri da yayiwa Sabi'u...
Sabi'u ya kuma muskutawa kafin yaci gaba da fad'in "Haka ne, a kwanakin baya yau kimanin wata guda cif an tura wasu 'yansanda daga cikin mu zuwa jihar Borno domin kwantar da tarzoma... Toh Ahidjo yana cikin wad'anda aka tura...."
Kukan da Innah ke dannewa ya fito mata gaba d'aya, lokaci guda take girgiza kai tana k'unshe bakinta zuciyarta bata daina yankewa ba sanda Sabi'u yaci gaba da fad'in "Sak'o ya riske mu cewa 'yan ta'addan sunyi nasaran kashe wasu daga cikin 'yansanda sannan cikin wad'anda tsautsayin ya ritsa dasu harda aminina Aliyu... Allah ya masa rasuwa tun wancan lokacin....!" Ya k'arashe yana matsan k'walla sai ka rantse har cikin zuciyarsa ne...
Jiri ne ya soma d'iban Innah daga zaunen da take, tama kasa yin kukan sai tara-tara da take gani, ta kasa gasgata kalamun wannan mutumi, Aliyunta tilon d'an nata wai shine babu sannan babun na har abada bama babun da za'ace wataran zai dawo ba.... Lokaci guda taji k'irjinta na mata zafi tamkar an d'aura mata gingimen dutse yayinda bakin Baffah bai daina karanto innalillahi wa inna'ilaihi raji'un ba...
Ganin Innah zata zube yasa Baffah saurin rik'ota murya na rawa sosai yake fad'in "Bilkisu ba kuka zakiyi ba, kiyita karanto innalillahi wa inna'ilaihi raji'un....!" Girgiza masa kai kurum Innah take hawaye masu tsananin d'umi suna ci gaba da gangaro mata, shi kansa Baffah da zai samu kuka ya fita masa tabbas da zaiyi sabida tsananin rauni da zuciyarsa tayi...
Girgiza kai Innah keyi tana rik'e da Baffah k'am take fad'in "Malam... Malam kace min ba haka bane, badai Ahidjo na ba, Malam nasan bai mutu ba, Malam ban tab'a ji a jikina ya mace ba... D'ana yana nan, d'ana bai mutu ba.. Dan Allah kuce min yana raye, ku fad'a min... !" Ta k'arashe cikin tsananin kuka mai ban tausayi
"Bilkisu ba'a k'aryan mutuwa, muyi hak'uri haka Allah ya k'addaro mana... Allah sarki Baba Wuro ashe dawowan da bazai mana ba kenan... Ashe rabuwa dashi zamuyi na har abada... Kaico ban bashi daman ya mana sallama ba.. Bilkisu zan dad'e inajin zafin wannan abu cikin zuciyata....!" Ya k'arashe yana fitar da hawaye don jarumtakarsa ta gaza, gudan jini ba wasa ba...
Sabi'u kuwa yanda kasan ya sami TV haka ya maida wad'annan bayin Allah, ya dubi wannan ya dubi wancan, ganin hawaye idanun Baffan Ahidjo da kuma yanda mahaifiyarsa ke fitar da nata kukan ya sanya jikin Sabi'u yin sanyi, sun basa tausayi matuk'a Allah sarki da alama basuda wani d'an sai shi....
Deejoh da k'arasowarta wajen kenan domin cikin baccin nata k'irjinta yayi wani irin yankewa ya fad'i, ba komai yazo bakinta ba sai Yaya Ahidjo, cikin sauri ta fito waje nan kuwa tajiyo kukan Innah daga sashen Baffah, k'afafunta na rawa ta k'arasa ga uban juwa dake d'ibanta, a dai-dai lokacin da Deejoh ke k'arasowa wajen ta jiyo muryar Sabi'u na fad'iwasu Baffah "Kuyi hak'uri ku masa addu'a Ahidjo mutumin arziki ne kuma yayi zaman amana da kowa, ubangiji ya gafarta masa.."
Idanuwan Deejoh shafe mata sukayi, wani irin bugu taji k'irjinta na mata tamkar ana sauk'e mata guduma.... Kalmar Allah yayi masa rahama ne kurum ke yawo a dodon kummuwarta da kwanyarta... Wani irin k'ara ta saki had'i da zubewa a wajen gaba d'aya hankulansu yayi wajenta....
Sabon tashin hankali daga Innah har Baffah suka nufeta cikin sauri domin ceto nata rayuwar....
***
Dr Sahal ya buk'aci su basu waje don ya gana da patient d'in nasa ya fahimci wani hali yake ciki.... Gaba d'aya Baba Malam da Hafiz suka fice suka bar Dr Sahal da wannan majiyanci...
K'uri Dr Sahal ya masa yana karantarsa yanda yayiwa Dr Sahal k'uri babu um balle um-um, da fari saida ya karkad'a hannunsa saman idanunsa ya tabbatar ganinsa bai gushe ba kafin daga bisani ya matso dab dashi kana yace "Sannu bawan Allah.. Zaka iya fad'a min sunan ka....?"
Shiru majinyacin bai amsa sa ba sai kauda kai gefe da yayi, Dr ya kuma komawa b'angaren da ya juya kansa kana ya maimaita masa tambayar da ya masa... K'uri majinyacin ya masa ba tareda ya furta komai ba... Dr Sahal ya soma tunanin k'ila ya rasa jinsa ne... Maimaita masa tambayar yayi a karo na uku sai sannan majinyacin ya d'an girgiza masa kai alamun a'a cikin murya da bai fita sosai irinta majinyanci mai tsananin jin jiki yace "Ina ne nan, meye nakeyi a nan...?"
Saida Dr Sahal ya masto da kunnensa dab da bakin majinyacin kafin yaji maganganun da yakeyi.... Murmushi Dr yayi don an haye wani sirad'in, rank'wafowa ya kumayi yana duban patient d'in kana yace "I'm Dr Sahal and nan da kake gani asibiti kake, you went through a serious accident... Zaka iya fad'a min menene sunanka ko kuma menene ya sameka...?" Ya k'arashe yanai masa k'uri
Patient d'in ya d'ibi dak'ik'ai yana duban Dr Sahal kafin ya d'an kuma girgiza kai a karo na biyu kana yace "I don't know, ban sani ba, I don't remember anything...." Daga haka kauda kansa gefe yayi ba tareda ya kuma amsa sa ba....
Mik'ewa Dr Sahal yayi had'ida d'an fuzar da iska kafin ya janyo file d'insa dake bisa table d'in gefen gadon yayi wasu rubutu kana ya fito ya taddasu Hafiz da Baba Malam....
Dr Sahal bai b'oye masu komai gameda patient d'in nasu ba don dama ya sanar dasu irin haka ka iya faruwa, shi baima zaci zai tsaya a haka ba, yayi zaton zai iya rasa ganinsa ko jinsa koma hankalinsa gaba d'aya amma Allah cikin ikonsa sai tunaninsa ya shafe kawai, tabbas abin a godewa Allah ne...
Mai Unguwa ya jinjina kai kana ya kirawo d'aya daga cikin 'yan fadansa yace suyiwa bak'om rakiya zuwa gidan Malam Sanda...
Tafiyace mai d'an rata kad'an dashike gidan ba'a cikin gari yake ba kafin suka isa....
Sank'ira yayi sallama k'ofar gidan Malam Sanda, baki na biyu aka amsa daga ciki kafin Malam Sanda ya fito suna gaisawa da Sankira... Nan Sankira yake masa nuni da bak'on da yazo nemansa daga can birnin tarayya
Malam Sanda ya maido da dubansa ga Sabi'u kafin ya mik'a masa hannu sukayi masabaha, cikeda rusunawa Sabi'u ke gaida Malam Sanda kafin Sankira ya masu sallama yace ya barsu lafiya...
Malam Sanda ya dubi Sabi'u kana yace "Toh bawan Allah gashi ban wayeka ba, lafiya dai koh...?"
Sabi'u ya d'an gyara tsayuwarsa kana yace "Toh wato Baba wani Al'amari ke tafe dani, kuma akan D'anka Ahidjo ne, amma idan bazaka damu ba zanso mu shiga daga ciki sai na sanar dakai komai gaban sauran iyalan naka domin Ahidjo ya sanar dani yanada iyali a nan gida..."
Baffah ya jinjina kai kana yace "Haka ne, amma abinda ban gane ba shine wani sak'o ne zai baka dashi bazai iya zuwa ba, wato abin nasa har ya kai ya daina zuwa saidai yayo aike, toh idanma wani abin ya baka ka kawo mana ka maida masa kayansa don dagani har iyalaina bamuda buk'ata...."
Shiru Sabi'u yayi yana duban Malam sanda had'i da karantarsa kana ya d'anyi gyaran murya yace "Baba wato wannan Al'amari da zan sanar daku Al'amari ne mai girma, kayi hak'uri mu shiga daga ciki, ka zauna kaima domin sak'o na magana zan sanar daku ba ta dukiya ko na wani abu makamancin haka ba... Dan Allah Baba..." Ya k'arashe cikin k'ank'an dakai...
Shiru tamkar Malam Sanda bazaice komai ba sai kuma yace "Shikenan mu shiga daga ciki...
Baffah da kansa yayiwa Sabi'u shimfid'a kafin ya kirawo Innah, ganin Baffah da bak'o matashi ya sanya jikin Innah yin sanyi don ba kowa ya fad'o mata ba face tilon d'anta, gaisawa Innah sukayi da Sabi'u kafin Baffah ya buk'aci ta kirawo Deejoh su taho tare...
Nan Innah ke sanar da Baffan Deejohn bataji dad'i ba tun safe zazzab'i ya rufeta, bata gane jikin ba....
Baffah yace "Subhanallah yaya baki sanar dani ba...?".
Naga zazzab'in ya d'an sauk'a ne shiyasa ban sanar dakai ba amma yanzu haka ma bacci take..."
Baffah ya jinjina kai kana yace "Ki zauna toh wannan bawan Allah sak'o yaron nan ya basa ya kawo mana..."
Jin haka yasa k'irjin Innah bugawa da k'arfin gaske domin kuwa tabbas tasan Ahidjo Baffah ke nufi, lokaci guda ta nemi waje ta zauna k'irjinta naci gaba da bugu, don haka kurum ta tsinci kanta da tsoron jin sak'on da za'a isar masun
***
*A garin Damaturu*
Yau yake cika sati biyu cif a asibitin, a hankali ya soma motsa d'an yatsansa, yana mai k'ok'arin bud'e idanunsa da suka masa nauyi tamkar an d'aura masa manyan duwatsu, da kad'an kad'an idanun nasa suka bud'e gaba d'aya... Nurse dake k'ok'arin d'aura drip mamakine ya cikata taga abinda batayi zato ba.... A guje ta fice kiran Dr Sahal hakan yayi dai-dai da shigowarsu Baba Malam da kuma Hafiz, ganin Nurse d'in ta fito daga d'akin a guje ya sanyasu nufan d'akin cikin sauri...
*Toh fah mai karatu wasan zai soma... Just stay tuned guys*
*SameenaAleeyou📚**FUSKA UKU*🏮
*45*
*©Sameena Aleeyou...✍🏽*
Sabi'u yayi gyaran murya kafin yaci gaba da fad'in "Nidai sunana Detective Sabi'u Lawan, kuma ni abokin aikin Ahidjo ne, munsan juna sama da shekara biyar sannan mu aminan juna ne domin mun wuce abokai wannan dalili yasa ya sanar dani labarinku don ko matarsa batasan daku ba...." Fasali ya d'an ja kafin yaci gaba da fad'in "Baba, Iya wato gaskiya kuyi hak'uri da batun da zakuji daga bakina..."
Inna da tuni hawaye ya soma fitowa daga idanunta cikin tsananin tashin hankali ta tari Sabi'u da fad'in "Bawan Allah dan Allah ka sanar damu mai ya sami d'anmu ka rik'e bayananka sai ka sanar damu halin da yake ciki na rok'i aezikinka..." Ta k'arashe cikin tsananin rawar murya... Baffah kam bai ma iya furta komai ba sai k'uri da yayiwa Sabi'u...
Sabi'u ya kuma muskutawa kafin yaci gaba da fad'in "Haka ne, a kwanakin baya yau kimanin wata guda cif an tura wasu 'yansanda daga cikin mu zuwa jihar Borno domin kwantar da tarzoma... Toh Ahidjo yana cikin wad'anda aka tura...."
Kukan da Innah ke dannewa ya fito mata gaba d'aya, lokaci guda take girgiza kai tana k'unshe bakinta zuciyarta bata daina yankewa ba sanda Sabi'u yaci gaba da fad'in "Sak'o ya riske mu cewa 'yan ta'addan sunyi nasaran kashe wasu daga cikin 'yansanda sannan cikin wad'anda tsautsayin ya ritsa dasu harda aminina Aliyu... Allah ya masa rasuwa tun wancan lokacin....!" Ya k'arashe yana matsan k'walla sai ka rantse har cikin zuciyarsa ne...
Jiri ne ya soma d'iban Innah daga zaunen da take, tama kasa yin kukan sai tara-tara da take gani, ta kasa gasgata kalamun wannan mutumi, Aliyunta tilon d'an nata wai shine babu sannan babun na har abada bama babun da za'ace wataran zai dawo ba.... Lokaci guda taji k'irjinta na mata zafi tamkar an d'aura mata gingimen dutse yayinda bakin Baffah bai daina karanto innalillahi wa inna'ilaihi raji'un ba...
Ganin Innah zata zube yasa Baffah saurin rik'ota murya na rawa sosai yake fad'in "Bilkisu ba kuka zakiyi ba, kiyita karanto innalillahi wa inna'ilaihi raji'un....!" Girgiza masa kai kurum Innah take hawaye masu tsananin d'umi suna ci gaba da gangaro mata, shi kansa Baffah da zai samu kuka ya fita masa tabbas da zaiyi sabida tsananin rauni da zuciyarsa tayi...
Girgiza kai Innah keyi tana rik'e da Baffah k'am take fad'in "Malam... Malam kace min ba haka bane, badai Ahidjo na ba, Malam nasan bai mutu ba, Malam ban tab'a ji a jikina ya mace ba... D'ana yana nan, d'ana bai mutu ba.. Dan Allah kuce min yana raye, ku fad'a min... !" Ta k'arashe cikin tsananin kuka mai ban tausayi
"Bilkisu ba'a k'aryan mutuwa, muyi hak'uri haka Allah ya k'addaro mana... Allah sarki Baba Wuro ashe dawowan da bazai mana ba kenan... Ashe rabuwa dashi zamuyi na har abada... Kaico ban bashi daman ya mana sallama ba.. Bilkisu zan dad'e inajin zafin wannan abu cikin zuciyata....!" Ya k'arashe yana fitar da hawaye don jarumtakarsa ta gaza, gudan jini ba wasa ba...
Sabi'u kuwa yanda kasan ya sami TV haka ya maida wad'annan bayin Allah, ya dubi wannan ya dubi wancan, ganin hawaye idanun Baffan Ahidjo da kuma yanda mahaifiyarsa ke fitar da nata kukan ya sanya jikin Sabi'u yin sanyi, sun basa tausayi matuk'a Allah sarki da alama basuda wani d'an sai shi....
Deejoh da k'arasowarta wajen kenan domin cikin baccin nata k'irjinta yayi wani irin yankewa ya fad'i, ba komai yazo bakinta ba sai Yaya Ahidjo, cikin sauri ta fito waje nan kuwa tajiyo kukan Innah daga sashen Baffah, k'afafunta na rawa ta k'arasa ga uban juwa dake d'ibanta, a dai-dai lokacin da Deejoh ke k'arasowa wajen ta jiyo muryar Sabi'u na fad'iwasu Baffah "Kuyi hak'uri ku masa addu'a Ahidjo mutumin arziki ne kuma yayi zaman amana da kowa, ubangiji ya gafarta masa.."
Idanuwan Deejoh shafe mata sukayi, wani irin bugu taji k'irjinta na mata tamkar ana sauk'e mata guduma.... Kalmar Allah yayi masa rahama ne kurum ke yawo a dodon kummuwarta da kwanyarta... Wani irin k'ara ta saki had'i da zubewa a wajen gaba d'aya hankulansu yayi wajenta....
Sabon tashin hankali daga Innah har Baffah suka nufeta cikin sauri domin ceto nata rayuwar....
***
Dr Sahal ya buk'aci su basu waje don ya gana da patient d'in nasa ya fahimci wani hali yake ciki.... Gaba d'aya Baba Malam da Hafiz suka fice suka bar Dr Sahal da wannan majiyanci...
K'uri Dr Sahal ya masa yana karantarsa yanda yayiwa Dr Sahal k'uri babu um balle um-um, da fari saida ya karkad'a hannunsa saman idanunsa ya tabbatar ganinsa bai gushe ba kafin daga bisani ya matso dab dashi kana yace "Sannu bawan Allah.. Zaka iya fad'a min sunan ka....?"
Shiru majinyacin bai amsa sa ba sai kauda kai gefe da yayi, Dr ya kuma komawa b'angaren da ya juya kansa kana ya maimaita masa tambayar da ya masa... K'uri majinyacin ya masa ba tareda ya furta komai ba... Dr Sahal ya soma tunanin k'ila ya rasa jinsa ne... Maimaita masa tambayar yayi a karo na uku sai sannan majinyacin ya d'an girgiza masa kai alamun a'a cikin murya da bai fita sosai irinta majinyanci mai tsananin jin jiki yace "Ina ne nan, meye nakeyi a nan...?"
Saida Dr Sahal ya masto da kunnensa dab da bakin majinyacin kafin yaji maganganun da yakeyi.... Murmushi Dr yayi don an haye wani sirad'in, rank'wafowa ya kumayi yana duban patient d'in kana yace "I'm Dr Sahal and nan da kake gani asibiti kake, you went through a serious accident... Zaka iya fad'a min menene sunanka ko kuma menene ya sameka...?" Ya k'arashe yanai masa k'uri
Patient d'in ya d'ibi dak'ik'ai yana duban Dr Sahal kafin ya d'an kuma girgiza kai a karo na biyu kana yace "I don't know, ban sani ba, I don't remember anything...." Daga haka kauda kansa gefe yayi ba tareda ya kuma amsa sa ba....
Mik'ewa Dr Sahal yayi had'ida d'an fuzar da iska kafin ya janyo file d'insa dake bisa table d'in gefen gadon yayi wasu rubutu kana ya fito ya taddasu Hafiz da Baba Malam....
Dr Sahal bai b'oye masu komai gameda patient d'in nasu ba don dama ya sanar dasu irin haka ka iya faruwa, shi baima zaci zai tsaya a haka ba, yayi zaton zai iya rasa ganinsa ko jinsa koma hankalinsa gaba d'aya amma Allah cikin ikonsa sai tunaninsa ya shafe kawai, tabbas abin a godewa Allah ne...