Sashe 26
Fargar Jaji Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shamsiya ta yi shuru kafin ta ce" Kina da tabbacin in mganar ta kai wajen su Baffa komai zai yi daidai? Ni fa sai na ke ganin sako su a ciki zai iya ɓata komai, ki sake ɓata ran Habib har ya yanke miki hukunci cikin fushi."
Ummu ta yi zuru tana kallon Shamsiya kamar wata doluwa cikin bugawar zuciya ta ce" Wani hukunci zai yanke a kaina?
"Hukunci rabuwa da ke mana, kin ga ya cuce ki ya cutar da iyayenki ya sa kin zama ƙaramar bazawara."
Gaban Ummu ya amsa! Tana son Habib ba za ta iya juran rasa shi ba.
"Ki tsira da auran ki Ummu-Salma, kuma ni ban ga laifin Habib ba, haka na faruwa ko wata da muke É—aki É—aya a makaranta mijinta ya ce sai sun shekara biyar da aure za ta haihu kuma ta amince. So normal ne kawai fahimta ce tsakanin ma'aurata, ke kan ki Ummu nawa kike? Kina da sauran damarma ki masu tarin yawa ma anan gaba ni ban ga laifin Habib ba, ra'ayin shi ne kuma girmama ra'ayin juna a zamantakewa kamar dole ne."
Ummu ta jinjina kai cikin sanyin jiki kafin ta ce'" Ina son aurena sannan ina son cikina Bestie."
"To sai dai ki zaɓi ɗaya ko auran ki, ko cikin."
Ummu ta kasa zaɓan wanda ya fi sauƙi a ciki, duk tana son ta tsira da su da auran da cikin jikinta.
Shamsiya kuma ta yi ta nuna mata ba matsala in ta zubar yanzu gaba za ta iya samun wani a lokacin da suka shirya suna da dama, tun da lamarinn nan ya fara faruwa ba ta ji ta samu salama ba sai da ta yi mgana da Shamsiya sannan ta samu jin wani abu ya faɗa daga ƙirjinta.
Shamsiya ba ta tafi ba sai da Ummu ta ba ta tabbacin za ta amince da umarnin Habib. Ita fa Shamsiya ƴar boko ce, sannan renon yan boko su a ganin su hakan ba matsala ba ne bayan tafiyar Shamsiya Ummu ta yi ta tufka tana warwara, shawaran Shamsiya ta fi zama mata sosai a cikin zuciyarta duk da tana son cikin ta amma kuma tafi son Habib a kan cikin, kamar yadda Shamsiya ta faɗa ne in tana son Habib to ta bi umarnin sa sai su zauna lafiya. Za ta amince da a zubar da cikin amma sai ya ba ta tabbacin zuwa yaushe yake son ta haihu ? Allah na gani tana son haihuwa har mafarkin tana shayar da jariri take yi. In har ba zai wuce shekara biyu ba to za ta iya haƙuri a zubar da wannan amma in dai ya gota ba za ta iya haƙuri ba.
***
A RANAR.
Habib Ya fito daga wajen aiki kenan misalin 4:40pm, ya tsaya tare da wani abokin sa suna magana. Ya ji saƙo ya faɗo wayarsa amma saboda suna mgana bai duba a lokacin ba sai da suka yi sallama kowa ya nufi in da ya yi parking ɗin motar shi ya shiga.
Shi dai yana shiga cikin motar na shi jakar hannun sa ya sauke a gefen kujeran mai zaman banza. Sannan ya fiddo wayarsa dake cikin aljihun wandon shi saƙo ne daga M.S kamar yadda ya yi zato tun farko.
"Habib lokaci yana ƙure mana fa, ina jin tsoro, tsoron kar maganar nan ta je kunnen iyayenta daga nan waliyanka su ji labari alalan mu ya yi ruwa, tsarin mu ya lalace ba yadda muka shirya ba. Don Allah ka yi wani abu da gaggawa ba mu da lokaci"
Mirmishin sarari ya yi kafin ya tura mata da amsa.
"Kar ki damu ba abin da suka isa su yi. Ba kuma wanda ya isa ya lalata mana shirin mu."
"In cikin bai zube ba fa?
"Ba wanda ya isa ya sa ni na karɓi abin da na ce bana so. Da gaske bana son ta sannan ba na son haɗa zuru'a da ita, in kuma ta cigaba da taurin kai to zan saka rayuwarta da na iyayenta a uku."
Yana turawa ba jimawa sai ga wani saƙon ya sake shigowa.
"Ka yi komai, in dai ka san ba zai hana shirin mu tafiya ba."
"Zan yi."
Da haka ya ma yar da wayar na shi cikin aljihun wondon shi ya kunna motar ya yi riverse ya bar haraban bankin, yana tafe yana wani tunani matukar Ummu ta cigaba da taurin kai to komai zai ƙare a tsakanin su, ta je can ta riƙe cikin sai ta zame masa uwa da uba. Abin da ya sa ya aureta tuni ya gama samun shi babu kuma sauran wani abu da ya rage a tsakanin su
**
Da wuri Habib ya dawo kamar ya san Ummu ta tsala kwalliya tana jiran dawowan shi, da yake ta ji sauƙi tana samun ƙarfin jiki ya sa har girki ta yi masa ta gyara gidan yana tashin ƙamshi.
Lokacin da ya dawo tana falo tana zaman jiran shi, bai yi mata mgana ba sai ita ce ta ce masa ya tsaya ya saurare ta.
"Na faÉ—a miki ba wani sauran mgana a tsakanina da ke malama."
Ya faɗa a fusace yana ƙoƙarin shigewa ɗakin da yanzu ya ke rayuwa a ciki.
"Ko da a ce maganar na amincewa da ɓukatar ka ne?
Ta faÉ—a a sanyaye, ai yana jin haka da sauri ya juyo yana kallon ta.
"Me kika ce?
Ya tambaya yana É—an rage É—aure fuskar da ya yi.
"Cewa na yi ko da maganar tawa na cewa na amince zan bi Umarnin ka ne?
Â
Kamar walƙiya sai ga shi a gabanta yana mai sakin jakar hannunsa kafin ta yi wani yunƙuri ya rumgume ta ƙamƙam cikin matsanancin farinciki.
"Haba ko ke fa Baby, sai yanzu na ji na samu natsuwa."
Murna yake yi a zucci da sarari nan da nan ya fara sumbatar ta a ko'ina na fuskar ta, yana mai nuna mata farincikin sa bisa amincewa da ta yi da bukatar shi, zuciyar Ummu ya cika da farinciki ganin yadda Habib ya ke yi mata rawan jiki, ta faɗa masa ta amince da buƙatar sa amma zuwa wani lokaci ya shirya ya zama uba ita kuma ta zama uwa.
"Nan da shekara É—aya Baby. Lokacin duka mun shirya zamo wa iyaye amma by now mu cigaba da cin lokacin mu."
Ya faÉ—a yana yi mata mirmishi, wannan mirmishin da shi ya yi amfani ya sace zuciyarta.
 Sai ga shi ranar tare suka yi Dinner yana ba ta abinci a baki tana bashi, ganin ta ɗan yi sanyi sanyi ya sa ya ke sake jadadda mata kar ta damu zai kai ta asibiti a bata maganin da cikin zai zuɓe ba tare da an samu wata matsala ba yana faɗa mata cikin ƙarami ne ba za ta fuskanci wata matsala ba.
Duk da Ummu ta amince da buƙatar Habib sai ta ji ta kasa samun natsuwa, a cikin zuciyarta ta kasa samun natsuwa cikin ta kawai take shafawa tana jin wani iri, sai take ganin kamar abin da za ta aikata ba alheri ba ne.
"Ummu-Salma ki sake tunani."
In ta amince aka zubar da cikin tana da garantin cewa Ubangiji zai sake ba ta wata damar! Ko kuma ranar gobe ƙiyama cikin da ta zubar ya tambaye ta a gaban Ubangiji da cewa wani laifi ya aikata mata da ta yi masa haka? Ba ta da amsa a wannan lokacin sai ta ji ta sare son cikin ta ya sake shigan ta, tuni ta ji ta sauya shawara gwara ta ce ma Habib ya yi haƙuri tun da cikin ya shiga ya bari in ta haihu sai su tsayar da haihuwar har zuwa lokacin da ya ke so.
Da wannan tunanin ta tsayar da shawara tana ɗakin ta ne Habib ya je ɗakin sa ya dawo ba jimawa sai ga shi ya shigo da gajeren wando jikinsa ba ko riga tana so ta yi masa mganar amma bai ba ta dama ba haka ya fara naniƙarta da sam ta ji ba ta bukatar hakan amma ta kasa yi masa gaddama. Bai bar ta ba sai da ya samu yar natsuwa sannan ya ɗan dakata a gefenta yana mayar da numfashi.
"Gobe Baby za mu je asibiti, ko kuma kawai na siyo miki mganin ki sha zai fi sauƙi ko?
Ya faɗa yana leƙen fuskarta, sai ta yi shuru ta kasa mgana haka kurum ta ji zuciyarta ta karye.
"Kin yi shuru."
Sai da haÉ—iye miyau sannan ta ce" Habib na sauya shawara."
Yadda ya miƙe zaune a firgice ne sai da Ummu ta ji tsoro itama ta tashi zaune tana mai rufe jikinta da bargon dake gefen ta.
"Raina mini wayau za ki yi?
Ya faÉ—a a fusace yana kallon ta.
"Aa wallahi."
"To me hakan ke nufi, mun gama mgana kuma yanzu kina faÉ—a mini wata maganar banza."
Ya katse ta a fusace yadda ya ta so mata in ta yi wasa zai iya kai mata duka.
"Ina so ne, ka bari sai na haihu."
Ta faɗa hawaye na kece mata kanta na ƙasa domin kauce ma wani mugun kallo da Habib ke jifanta da shi.
"Kin haihu a ina?
A gida na? Ba ki isa ba.'
Ya faÉ—a a fusace kafin ya diro daga kan gado.
"Sau nawa zan faÉ—a miki bana son na haihu da ke ne Ummu-Salma, ?
"Ai ka ce zan haihu nan da shekara ɗaya shi ne na ce tunda ina da cikin yanzu ka bari in na haihu daga baya sai na bari sai lokacin da ka shirya sai in sake haihu."
Kafa ya sa ya daki gefen gado cikin ƙaraji ya ce" Ke wata irin daƙiƙiya ce,? Da wani yare zan faɗa miki ki yarda da mgana ta?
Ya faɗa kamar ya kai mata duka, Ummu ta takure waje ɗaya tana mai kuka ƙasa-ƙasa.
"Na faɗa miki ba na son ki, bana son ki me ya sa ƙin ki gane hakan ne?
Ummu ta ɗago tana kallon shi da idanuwanta masu zubar ƙwallah.
"Ko ƙwaƙwalwarki kike so na buɗe na saka miki mganar ne sannan za ki fahimce ni?
Ya gama faÉ—a yana dafe kansa.
"To ka san haka me ya sa ka aure ni, ka nuna mini so kuma?
Ummu ta yi zuru tana kallon Shamsiya kamar wata doluwa cikin bugawar zuciya ta ce" Wani hukunci zai yanke a kaina?
"Hukunci rabuwa da ke mana, kin ga ya cuce ki ya cutar da iyayenki ya sa kin zama ƙaramar bazawara."
Gaban Ummu ya amsa! Tana son Habib ba za ta iya juran rasa shi ba.
"Ki tsira da auran ki Ummu-Salma, kuma ni ban ga laifin Habib ba, haka na faruwa ko wata da muke É—aki É—aya a makaranta mijinta ya ce sai sun shekara biyar da aure za ta haihu kuma ta amince. So normal ne kawai fahimta ce tsakanin ma'aurata, ke kan ki Ummu nawa kike? Kina da sauran damarma ki masu tarin yawa ma anan gaba ni ban ga laifin Habib ba, ra'ayin shi ne kuma girmama ra'ayin juna a zamantakewa kamar dole ne."
Ummu ta jinjina kai cikin sanyin jiki kafin ta ce'" Ina son aurena sannan ina son cikina Bestie."
"To sai dai ki zaɓi ɗaya ko auran ki, ko cikin."
Ummu ta kasa zaɓan wanda ya fi sauƙi a ciki, duk tana son ta tsira da su da auran da cikin jikinta.
Shamsiya kuma ta yi ta nuna mata ba matsala in ta zubar yanzu gaba za ta iya samun wani a lokacin da suka shirya suna da dama, tun da lamarinn nan ya fara faruwa ba ta ji ta samu salama ba sai da ta yi mgana da Shamsiya sannan ta samu jin wani abu ya faɗa daga ƙirjinta.
Shamsiya ba ta tafi ba sai da Ummu ta ba ta tabbacin za ta amince da umarnin Habib. Ita fa Shamsiya ƴar boko ce, sannan renon yan boko su a ganin su hakan ba matsala ba ne bayan tafiyar Shamsiya Ummu ta yi ta tufka tana warwara, shawaran Shamsiya ta fi zama mata sosai a cikin zuciyarta duk da tana son cikin ta amma kuma tafi son Habib a kan cikin, kamar yadda Shamsiya ta faɗa ne in tana son Habib to ta bi umarnin sa sai su zauna lafiya. Za ta amince da a zubar da cikin amma sai ya ba ta tabbacin zuwa yaushe yake son ta haihu ? Allah na gani tana son haihuwa har mafarkin tana shayar da jariri take yi. In har ba zai wuce shekara biyu ba to za ta iya haƙuri a zubar da wannan amma in dai ya gota ba za ta iya haƙuri ba.
***
A RANAR.
Habib Ya fito daga wajen aiki kenan misalin 4:40pm, ya tsaya tare da wani abokin sa suna magana. Ya ji saƙo ya faɗo wayarsa amma saboda suna mgana bai duba a lokacin ba sai da suka yi sallama kowa ya nufi in da ya yi parking ɗin motar shi ya shiga.
Shi dai yana shiga cikin motar na shi jakar hannun sa ya sauke a gefen kujeran mai zaman banza. Sannan ya fiddo wayarsa dake cikin aljihun wandon shi saƙo ne daga M.S kamar yadda ya yi zato tun farko.
"Habib lokaci yana ƙure mana fa, ina jin tsoro, tsoron kar maganar nan ta je kunnen iyayenta daga nan waliyanka su ji labari alalan mu ya yi ruwa, tsarin mu ya lalace ba yadda muka shirya ba. Don Allah ka yi wani abu da gaggawa ba mu da lokaci"
Mirmishin sarari ya yi kafin ya tura mata da amsa.
"Kar ki damu ba abin da suka isa su yi. Ba kuma wanda ya isa ya lalata mana shirin mu."
"In cikin bai zube ba fa?
"Ba wanda ya isa ya sa ni na karɓi abin da na ce bana so. Da gaske bana son ta sannan ba na son haɗa zuru'a da ita, in kuma ta cigaba da taurin kai to zan saka rayuwarta da na iyayenta a uku."
Yana turawa ba jimawa sai ga wani saƙon ya sake shigowa.
"Ka yi komai, in dai ka san ba zai hana shirin mu tafiya ba."
"Zan yi."
Da haka ya ma yar da wayar na shi cikin aljihun wondon shi ya kunna motar ya yi riverse ya bar haraban bankin, yana tafe yana wani tunani matukar Ummu ta cigaba da taurin kai to komai zai ƙare a tsakanin su, ta je can ta riƙe cikin sai ta zame masa uwa da uba. Abin da ya sa ya aureta tuni ya gama samun shi babu kuma sauran wani abu da ya rage a tsakanin su
**
Da wuri Habib ya dawo kamar ya san Ummu ta tsala kwalliya tana jiran dawowan shi, da yake ta ji sauƙi tana samun ƙarfin jiki ya sa har girki ta yi masa ta gyara gidan yana tashin ƙamshi.
Lokacin da ya dawo tana falo tana zaman jiran shi, bai yi mata mgana ba sai ita ce ta ce masa ya tsaya ya saurare ta.
"Na faÉ—a miki ba wani sauran mgana a tsakanina da ke malama."
Ya faɗa a fusace yana ƙoƙarin shigewa ɗakin da yanzu ya ke rayuwa a ciki.
"Ko da a ce maganar na amincewa da ɓukatar ka ne?
Ta faÉ—a a sanyaye, ai yana jin haka da sauri ya juyo yana kallon ta.
"Me kika ce?
Ya tambaya yana É—an rage É—aure fuskar da ya yi.
"Cewa na yi ko da maganar tawa na cewa na amince zan bi Umarnin ka ne?
Â
Kamar walƙiya sai ga shi a gabanta yana mai sakin jakar hannunsa kafin ta yi wani yunƙuri ya rumgume ta ƙamƙam cikin matsanancin farinciki.
"Haba ko ke fa Baby, sai yanzu na ji na samu natsuwa."
Murna yake yi a zucci da sarari nan da nan ya fara sumbatar ta a ko'ina na fuskar ta, yana mai nuna mata farincikin sa bisa amincewa da ta yi da bukatar shi, zuciyar Ummu ya cika da farinciki ganin yadda Habib ya ke yi mata rawan jiki, ta faɗa masa ta amince da buƙatar sa amma zuwa wani lokaci ya shirya ya zama uba ita kuma ta zama uwa.
"Nan da shekara É—aya Baby. Lokacin duka mun shirya zamo wa iyaye amma by now mu cigaba da cin lokacin mu."
Ya faÉ—a yana yi mata mirmishi, wannan mirmishin da shi ya yi amfani ya sace zuciyarta.
 Sai ga shi ranar tare suka yi Dinner yana ba ta abinci a baki tana bashi, ganin ta ɗan yi sanyi sanyi ya sa ya ke sake jadadda mata kar ta damu zai kai ta asibiti a bata maganin da cikin zai zuɓe ba tare da an samu wata matsala ba yana faɗa mata cikin ƙarami ne ba za ta fuskanci wata matsala ba.
Duk da Ummu ta amince da buƙatar Habib sai ta ji ta kasa samun natsuwa, a cikin zuciyarta ta kasa samun natsuwa cikin ta kawai take shafawa tana jin wani iri, sai take ganin kamar abin da za ta aikata ba alheri ba ne.
"Ummu-Salma ki sake tunani."
In ta amince aka zubar da cikin tana da garantin cewa Ubangiji zai sake ba ta wata damar! Ko kuma ranar gobe ƙiyama cikin da ta zubar ya tambaye ta a gaban Ubangiji da cewa wani laifi ya aikata mata da ta yi masa haka? Ba ta da amsa a wannan lokacin sai ta ji ta sare son cikin ta ya sake shigan ta, tuni ta ji ta sauya shawara gwara ta ce ma Habib ya yi haƙuri tun da cikin ya shiga ya bari in ta haihu sai su tsayar da haihuwar har zuwa lokacin da ya ke so.
Da wannan tunanin ta tsayar da shawara tana ɗakin ta ne Habib ya je ɗakin sa ya dawo ba jimawa sai ga shi ya shigo da gajeren wando jikinsa ba ko riga tana so ta yi masa mganar amma bai ba ta dama ba haka ya fara naniƙarta da sam ta ji ba ta bukatar hakan amma ta kasa yi masa gaddama. Bai bar ta ba sai da ya samu yar natsuwa sannan ya ɗan dakata a gefenta yana mayar da numfashi.
"Gobe Baby za mu je asibiti, ko kuma kawai na siyo miki mganin ki sha zai fi sauƙi ko?
Ya faɗa yana leƙen fuskarta, sai ta yi shuru ta kasa mgana haka kurum ta ji zuciyarta ta karye.
"Kin yi shuru."
Sai da haÉ—iye miyau sannan ta ce" Habib na sauya shawara."
Yadda ya miƙe zaune a firgice ne sai da Ummu ta ji tsoro itama ta tashi zaune tana mai rufe jikinta da bargon dake gefen ta.
"Raina mini wayau za ki yi?
Ya faÉ—a a fusace yana kallon ta.
"Aa wallahi."
"To me hakan ke nufi, mun gama mgana kuma yanzu kina faÉ—a mini wata maganar banza."
Ya katse ta a fusace yadda ya ta so mata in ta yi wasa zai iya kai mata duka.
"Ina so ne, ka bari sai na haihu."
Ta faɗa hawaye na kece mata kanta na ƙasa domin kauce ma wani mugun kallo da Habib ke jifanta da shi.
"Kin haihu a ina?
A gida na? Ba ki isa ba.'
Ya faÉ—a a fusace kafin ya diro daga kan gado.
"Sau nawa zan faÉ—a miki bana son na haihu da ke ne Ummu-Salma, ?
"Ai ka ce zan haihu nan da shekara ɗaya shi ne na ce tunda ina da cikin yanzu ka bari in na haihu daga baya sai na bari sai lokacin da ka shirya sai in sake haihu."
Kafa ya sa ya daki gefen gado cikin ƙaraji ya ce" Ke wata irin daƙiƙiya ce,? Da wani yare zan faɗa miki ki yarda da mgana ta?
Ya faɗa kamar ya kai mata duka, Ummu ta takure waje ɗaya tana mai kuka ƙasa-ƙasa.
"Na faɗa miki ba na son ki, bana son ki me ya sa ƙin ki gane hakan ne?
Ummu ta ɗago tana kallon shi da idanuwanta masu zubar ƙwallah.
"Ko ƙwaƙwalwarki kike so na buɗe na saka miki mganar ne sannan za ki fahimce ni?
Ya gama faÉ—a yana dafe kansa.
"To ka san haka me ya sa ka aure ni, ka nuna mini so kuma?